JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   22 / 37

63K to 66K   out of 109.4K words

saurin shigewa gidansu Isma'il.





? *THE SEEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 4? 7?




Fatima na shiga gidan ta ga mutane a zazaune anata murna, idanu suka had'a da Isma'il, jitai ance " Baiwar Allah lafiya kika shigo ba sallama?"

D'auke idanta tai daga kansa tai saurin cewa Salamu Alikum, dariya suka sa mata Hajiya tace " daga ina kike?"

Fatima tad'an saci kalan Isma'il sannan ta nuna da d'an yatsarta tace daga nan gidan, Goggo(uwar gidan Kawu) tace shigo ki zauna nasan kukan yaro kikaji shiyasa kika shigo ko? Kallan yaran tai a hannun ta murmushi ta saki sannan ta karasa tare da gaishesu, suka amsa goggo ta mik'a mata d'an, Kuramai ido Fatima tai tana san yara itakam, a hankali ta d'ago tad'an kalli Isma'il ga mamakinta shima idanunsa na kanta da sauri tai kasa da ido tace " Allah ya raya." Sukace Amin.

Goggo tace " Isma'il ko zaka dubo mai kazar ko ya fito, naga tun d'azu mahaifinka bai dawo ba, ga shi ya kamata ama mai jego farfesu."

Isma'il yace " bari naje."

Ji sukai Fatima tace " bari ni naje nasan gurin."

Hajiya takalleta fuskarta da fara'a tace " keda kikazo barka, ya za'ai musaki aiki sannan ga magriba ta kawo kai."

Isma'il ya mik'e tare da cewa bari naje.

Yana fita, Fatima tace " bari naje gida zan dawo gobe." Nan suka mata sallama ta fito da sauri.

Can taganshi har yayi nisa, da sauri ta shiga binsa har da had'awa da gudu, tai sa'a ta kusa isa gunsa, a hankali tace " Malam." Ga mamakinta gani tai ya juyo d'an batai tunanin zai jita ba.

Tsaya tai tana hakki, Isma'il ya matso kusa da ita yace " yana ganki anan?"

Cikin hakki tace " biyoka nai."

Kallanta yai da mamaki yace " abu kikesan fad'amin?" Kai ta gyad'a sannan tace " Malam alfarma da taimako nakesan kamin."

Isma'il ya kalleta yace " namefa?"

Tai shiru tare dayin kasa dakai, ya kara kallanta yace " ke nake jira."
Tana wasa da 'yan yatsun hannunta tace " Karatu nakesan ka koyamin."

Dariya Isma'il yasa yace " in kinasan karatu sai kice a saki a makaranta."

Tai kasa dakai tace " ni na islamiya nakeso, kullum Hajiya sai tace in tashi inyi sallah nikuma a garinmu sai mutum yayi aure yakeyin sallah to in ina kula da yanda takeyi sai inga tana motsa baki amma bansan me take cewa ba, shine nakeso ka koyamin na islamiya insan yanda ake sallah."


Kallanta yai cikin tausayawa, gata dai 'yar kauye mara ilimi sai dai komai nata na birgeshi, da wani ne haka zai karashi rayuwarsa ba tare dayace a koyamai ba."


Yaja dogon numfashi yace " yanzu kije gida gobe kisame ni da yamma a kofar gida, sai insan yanda zamuyi karatun."

Murmushi ta saki tace " nagode Malam. "

Tanakainan ta juya ta fara tafiya, kallo ya bita dashi ya shagala yana kallanta yaji an dafa kafad'arsa, ya juyo a zabure Amadu ne ya kalli inda Isma'il yake kallo yace " kasanta ne?"

Isma'il yai saurin wayancewa yace " wa?"
" wacce kake kallo mana."
" ni kaga ina kallan wata? Kawo nake lek'awa munjishi shiru tun d'azu daya fita siyo kaza." Isma'il yai maganar yana waige-waige.


Amadu yace " Niba wannan ba gurinka fa zanje yanzu."

" haba? To gani Allah yasa lafiya."

Amadu yasa dariya yace " Habiba ta sauka d'azu da rana na k'ira wayarka bansamu ba shiyasa na yanke hukuncin zuwa gunka."

Fara'ar Isma'il ce ta k'aru yace " kai haba? Amma naji dad'i, nima yanzun nan Samira ta sauka, oh ikon Allah kaga sun haihu a rana d'aya."

Amadu ma fara'ar fuskarsa ya fad'ad'a yace " ikon Allah meta samu?"
"Namiji."
"Nima Namiji. "
A tare suka sa dariya tare da rike hannu Amadu yace " lalai wad'annan Aminai zasu zama da alama."

Nan Amadu ya raka Isma'il gun mai kaza anan suka tadda kawo, sun siya suka taho tare kawo na tayasu murna yace " Lalai naji dad'i Allah ya kare mana su." Amin suka fad'a a tare.


Har gida Amadu ya rakasu, nan matan kawu suma sukai ta tayashi murna, ya d'auki d'an cikin farinciki yace " Isma'il tunda mun haihu a tare sai muyi canje, ni zan rad'ama d'anka suna kaima sai ka rad'ama nawa."


Duk suka kwashe da dariya kowa ya shiga cewa lalai hakan yayi.

Amadu ne ya rad'ama Ammar suna na gaskiya sunan mahaifin Amadu wato Kabir sai yasamau sunan daza'adinga cemai Ammar.

Shima Isma'il da kansa yaje gidan ya rad'ama yaron Jalaludeen saboda sunan dayasu rad'ama Ammar kenan.

Murna agun mutane ba'a magana saboda kowa yasan amintar dake tsakanin Amadu da Isma'il.


Washegari da yamma yana zaune a dakalin kofar gidan Fatima ta fito, cikin tafiyarya mai nutsuwa, tana ganinshi tai kasa dakai tana murmushi, Isma'il ya shiga kallanta harta karaso gurin, ta gaidashi a hankali, shima ya amsa tare da cewa " na d'auka kin fasa koyar karatun ganin kin dad'e baki fito ba." Yai maganar cikin zolaya, abinka da rashin wayau sai tace " bayan yanzu kazo tun d'azu nake lekowa bana ganinka."

Dariya yai yace " ashe da gaske takesan koyan karatun."

Kasa tai dakai tana wasa da 'yan yatsun hannunta, Isma'il yace na yanke shawara, duk ranar asabar da lahadi shine bani da makaranta da safe, wajen karfe 11 sai ki d'inga zuwa islamiya ina koya miki zuwa karfe 1, kinga karfe 2 ne ake fara karatu."



Kai ta d'aga tace to "Malam na gode, amma wannan yaron d'anka ne?"
Isma'il ya kalleta da mamakin tambayarta, yace " meyasa kikesan sani."

D'agowa tai a hankali ta kalleshi batace komai ba ta maida kanta kasa tare da cewa " sai ranar asabar d'in."

Ya amsa da "Allah ya kaimu."

Ta juya tai ciki, kallanta yai tare da murmushi.

Itakam tana shiga ta d'au tsintsiya ta hau shara ba gaira ba dalili bayan gun a gyare yake tas, shara take Hajiyar Abdul na zaune taji karar tsintsiya ta mik'e tare da fitowa, Fatima tagani tanata zabga shara zatai magana taji muryar Abdul yace " Faty Shara kikeyi ne?"

Kallansa tai ta kaida kanra kan shara, itakam zuciyarta batasan ace d'an Isma'il ne d'an ita tanada mugun kishi shiyasa bazata iya auren mai mata ba, zuciyarta tace anya kuwa kamar malam zai rasa mata?"

Jitai Abdul ya dafata yace " meke damunki haka?"

Ta d'ago tace " d'an Allah ina rokonka kadaina tab'ani in zakamin magana."

Ga mamakinta jitai yace " Sorry na daina."

D'agowa tai tana mai kallan mamaki tace " ina abokan naka?"

Yai dariya yace " suna gidansu."

Tai kasa dakai tare dad'an tab'e baki a ranta tace " da walaki, d'an dama inshi kad'ai ne zakaga yanada saukin kai kuma bashi da rashin mutunci, anma da zarar sun had'u da abokansa shi kenan kuma sai rashin mutunci ta ko ina."



Kallanta ya tsaya yanayi tana shara, sai murmushi yakeyi, Hajiya dake tsaye tana kallansu tai murmushi itama, da alama Fatima ce zata sa d'anta ya shiryu d'an wannan shine addu'arta yaran maraya ne bashida uba, sai dai yabiyema kawayen banza sun canza mai halaye.








*THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 4? 8?




Anyi suna lafita kowa na murna, Abba kam shima a lokacin Mamie nada tsohon ciki hakan yasa batazo ba, sai dai tunda akai suna jikin Samira yak'i dad'i kullum cikin cuta.


Fatima kam duk karshen sati suna zama da Isma'il a makaranta ya koya mata karatu, a sanu a sanu wata shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu batare da Isma'il ya farga ba, sai dai bai tab'a tunanin zai iya furta mata yana santa ba saboda sau dayawa yanaji tana zancen batasan kishiya.


Rayuwa kenan yanzu an wayi gari shekararsu Jalal 5, kusan kullum Jalal na gidansu Ammar inkuwa baizo ba to zakaga Ammar a nasu gidan.

Jalal ya taso yaro mai zuciya, shikuma Ammar hakuri gareshi, a duk lokacin da yara sukaso rainama Ammar hankali, Jalal ne ke zuwa ya musu shegen duka, hakan yasa suka daina tsokanar Ammar.


A b'angaren Fatima kam tana shiga gidansu Isma'il sosai sai dai a randa tasan yanada aure harda 'ya'ya ranar tasha kuka harda zazzab'inta, yanzu Fatima ta kile sosai d'an inba fad'ama akai ba bazaka tab'a cewa 'yar kauye bace.



Samari kuwa dake santa a k'aueyen nan yawa garesu, sai dai ita zuciyarta nakan Isma'il, ta kasa tsayawa da wani sam.



Kamar yanda ta saba yau asabar ta gama duk ayukanta, tace " Hajiya zan fita."

Hajiya tace " Fatima jiya da daddare sai nawa Abdul ya shigo?"


Fatima ta kalli Hajiya tace " Hajiya wlh bansani ba nidai harnai bacci banji motsin bud'e kofa ba, amma ai dama yace Campain yakeyi."

Hajiya tai shiru tace " wani campain me da daddaren Allah? Keda kin yarda? So yake yaja min zagi dama mutane nacemasa d'an mace tunda mahaifinsa ya rasu da daddewa."


Fatima ta matso kusa da Hajiya tace " Hajiya Allah ya gani kinayin daidai kokarinki ga matsalar kafar da kike fama da ita sannan ni fa hajiya? Kinsan iyayena sun rasu tun ina karama agun kanwar mahaifina na taso."


Hajiya tai murmushi tace " jeki ko ba gun karatu zaki ba?"

Mik'ewa tai tana murmushi ta mata sallama ta fita, Hajiyar Abdul ta bita da kallon k'auna.


Tazo fita taji an cafko hannunta, ko bata juyaba tasan waye hakan yasa ta dage ta fizge hannunta da karfi, Abdul haushi ya kamashi, yana takaicin yanda take nunamai kamar tana kyamarsa, sa hannu yau ya fizgota ya matseta jikin bango, ta d'ago tare da had'e rai, Abdul ya kalleta ya saki wani mugun murmushi yace "Fatima na yanke hukuncin muyi aure kawai."
Batasan sanda ta bugamai wata harara ba, batai auni ba taji ya kifa mata mari yace " ni kike harara? Ko kin manta ni waye?"

Kasa tai da kai tare da rik'e gun, ya saketa yace " ankusa nad'ani Chairman a garin nan, in har mai aikin gidanmu bata bani girma ba wa zai bani?"

Ta kalleshi a ranta tace " tir da wannan mik'amin da ake shirin ba ka." Ya saketa tare da shiga ciki, cikin takaici itama ta wuce waje.

Abdul na shiga ya gaida hajiya tare da cewa " Umma nikam aure nakeso."

Kallansa tai cikin mamaki da kuma murna tace " wa kakeso Abdul? Naji dad'i?"

Ya d'an sosa k'eya yace " ni Fatima zaki auramin."

Murmushin fuskarta ne ya fad'ad'a tace " Da gaske Abdul?"
Yai murmushi yace " sosai ma, amma d'an Allah Umma tunda yarinyar nan a gunki take kuma anan gidan zata zauna asa auren nan da sati 2."

Dariya ta saki tace " Abdul matsuwar ta menene haka?"
Yace " ni kawai so nake ayi nan kusa."

Shiru tai lalai dole ta yarda ai nan kusa, d'an tasan inka ga namiji ya matsu da aure sosai to gwara amai kafin abin kunya ya ratsu ciki.

Tace to naji jeka.

Nan ya mik'e tare da Murmushin mugunta, d'an shikam kullum da sha'awar ta yake kwana.



Fatima kam tana fitowa a waje kan dakali taga Jafar da Ammar, ta matsa tare da cewa " Me kukeyi a nan?"

Jafar ya kalleta yace " a zaune kawai muke."

Fatima tai murmushi tace " ku bakwa wasa irin na yara?"

Jafar ya kalli Ammar yace " yaran ne 'yan rainin hankali, munfisan muyi wasanmu mu biyu."

Tace " Ammar ina Babanka?"

Yace ya fita, tai murmushi tad'auko naira goma a jakarta tace " ungo kusai alawa."
Jafar ya kalleta yace " mun gode amma bazamu ansa ba."

Ta kalleshi sannan tace "Ammar kaifa?" Kallan Jalal yai yace "a'a mun gode. "

Ta d'an yi kasa dakai alamar rashin jin dad'i sukam sauka su kai suka shiga gidan da gudu.

A hankali take tafiya, samarin garin kowa na sha'awar yanda take da hankali ga kyau, harta isa makaranta, ta tadda Isma'il a zaune, ta gaidashi ya kalleta cikin kulawa yace " yau kin d'an dad'e Allah yasa lafiya."

Ido ta kuramai kamar batasan me yake cewa ba, ganin yanda take kallansa yasa yai murmushi yace "da alama kunyar fulani tabar jikinki."

Da sauri ta d'auke ido tace " Malam duk kunyata?"
"Hmm a da ba? Yanzu naga harkin fara kurama mutane ido."
Ta had'e rai tace " kaine mutane?"

Yai murmushi ya wayance da cewa " matso muyi sauri matata batajin dad'i."

Had'e rai sosai Fatima tai dama yasani, shikuma harga zuciyarsa yasan yanasanta sosai, sai dai yasani bazata iya auransa ba, ga 'ya'yan masu kud'i na santa samari, ina zai so abinda yake neman fin karfinsa?shiyasa yakesan itama ta daina sanshi.

Mik'ewa tai cikin tsananin kunar rai ba tace mai komai ba tai hanyar waje.

Isma'il ya kalleta yace " nayi zuwan banza kenan?"
Tsayawa tai cak batare da ta juyoba idanunta na zubar da kwalla, mai yasa zuciyarta bata iya b'oye so ba?

Haka ta juya sukai karatun ba dad'i.




Tana dawowa gida Hajiya tasanar da ita zancen aurensu da Abdul, cikin mamaki ta kalleta tace " ni kuka Hajiya? Mai zai yi dani 'yar kauye?"

Hajiya tace " Fatima kitaimakeni bad'an shi ba d'an ni ayi auren nan,wannan shine buri na d'aya da ya rage min a duniya, d'azu na k'ra kanwar Babanki bakiga murnar datai ba."

Fatima ta d'ago a ranta tace tayi murna mana tunda taji zan auri mai kudi.

Murmushin yake Fatima tai mata sannan ta mik'e ta shiga d'an d'akinta, tana isa ta fad'a gado kuka sosai ta shiga yi, meyasa ba wanda zai tambayeta ko akwai wanda takeso? Tasani da mahaifanta nada rai dasai sun tambayeta ko tanaso, ta dad'e tana kuka kafin ganin ba mai lalashi ta mik'e.


Isma'il kam ya dawo yana shiga d'aki, ya tadda Samira a zaune, ya shiga shima ya zauna, tamai sannu da zuwa tare da cewa" dagaske kaima kanacikin jerin masu san Fatima?"

Da mamaki ya kalleta yace " me kike fad'a haka?"

Ta juyarda kai tace " d'azu na fita gunsu Hajiya naji wani saurayi yazo kawo musu kara wai kana santa duk asabar da lahadi sai kun had'u a makaranta kunyi zance."

Ya mik'e tsaye yace " kuma sai kika yarda da zancen nakejan yarinya zuwa makaranta inayi?"

Juya kai ta sakeyi hakan yasa ya gane wato ta yardan kenan, a zuciye ya fito waje, Hajiya ya gani dasu Goggo suma suna maida zancen, kallansu yai cikin takaicin abinda kowake fad'a zaiyi magana sai ga Jafar ya shigo, ya kalli Isma'il yace " Dad wai ana magana dakai."

Yace " Jafar inji wa?"

Yace " Abba nane."

Tare suka juya sukai waje, bayan sun gaisa da Amadu ne yace " Amadu ya akai?"

Amadu yai shiru can yace " haryanzu kana koyama Fatima karatu ne?"

Kai ya gyad'a alamar eh, Amadu ya dafa kafad'arsa yace "kayi hakuri ka rabu da yarinyar nan, nasan ka sosai Isma'il nasan kuma kana santa, wani karatu kake koyamata har shekara 5?"

Yai ajiyar zuciya sannan ya cigaba " kaga d'azu a shago naji ana gulmarka, sannan naji ma yarinyar yaron gidan zata aura, Isma'il ka hakura kasan Abdul wanda za'aba Chairman ba mutunci garesu ba su da abokansa."

Isma'il zuciyarshi ta tab'u dajin wai anmata miji, ya d'aure yace " nagode Amadu, insha Allah kuma mungama karatun."



Tun daga wannan rana bata sake sa Isma'il a idanunta ba, zuciyarta takasa hakura da rashinshi, wani sa'in har gidan take zuwa sai dai kowa taga ya daina sakar mata fuska, ga abin takaici shirye-shiryen bikinsu kawai sukeyi ba wanda ya damu da halin da take ciki.






Isma'il kam shima komai nasa ya canza bai fiya magana ma sosai ba, duk 'yan gidan hatta Samira sun fahimci yanasan Fatima sosai, sai dai yaza'ayi?


Abdul kam abokansa sai dariya sukemai wai zai auri 'yar kauye, yace " nimafa bawai d'an inzauna da ita d'ind'ind'in nakesan auranta ba, d'an kawai in kauda kwad'ayi nane, dariya suka kwashe dashi sukace " in wannan ne ba kawai sai ka....."
Shidai kam zuciyarshi batasan wannan kawai....d'in.


Yau saura kwana 2 biki, d'anginsu Fatima sun cika gida, itakam kallan kowa take a baibai, sai dai ba yanda zatai, duk ta rame ta canza.


Dad nakawo nan yai shiru tare da kallan Seemah dake zubar da kwalla kamar an bud'e famfo, Ammar ma hawaye ke zubar mai, ya kalli Habib shima haka.

Yai shiru can yace " Ana saura kwana 2 auranta ne Ammar yazo ina zaune kusa da Samira da ba lafiya ya sanar dani wai matar nan ta gidan nan, tace d'an Allah tanasan ganina a shagon Abban Jafar. "


Samira dake kwance ba lafiya na kalla, na share maganar tare da kallan matata, Samira ta juyamin baya tana zubar da kwalla, tausayinta dana kaina ya kamani hakan yasa na watsar da maganar Fatima nasan ganina.


A b'angaren Fatima kam tun karfe 2 tazo gefen shagon take tsaye, har la'asar, Amadu tausayinta ya kamashi yace " Fatima anya zaizo kuwa?"

22 / 37