JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   31 / 37

90K to 93K   out of 109.4K words

hawayen daya zubo mai sannan ya kakaro murmushi tare da juyawa zai fita, Seemah zata sake magana kawai ta hango kamar Jalal, da sauri ta saki Ammar sannan cikin kakusar murya tace " *DEEN WAIT*

Tsayawa Jalal yai cak ba tare daya juyo ba, Seemah ta kalli Ammar tace " Yaya in mai magana?"

Gaban Jalal ne ya fad'i jin kalaman Seemah, amai magana? Au in zata mai magana sai ta nemi izini? Idanunsa ya runste.

Ammar ya d'agama Seemah kai sannan ya juya ya bar falon, ba shakka yaji dad'in yanda Seemah tabashi matsayi.


Zaid ma ya juya yai waje, Jalal baisan Seemah ta karaso ba jin kanshin turarenta yasa ya fahimta, a hankali ya bud'e idanunsa ya zubasu akanta.

Seemah ta kuramai ido gyambon data d'auka ya warke ne ya motsa, hawaye ne ya zubo mata, shima hawayen ne ya zubo, bakinta ya fara rawa ta kasa mai magana.

Jalal ya goge hawayensa sannan ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace " how have you been?"

Kallansa kawai take ta kasa magana, Jalal ya d'aga kai ya d'an ja hanci yace " I see, ya za'ai ma in tambayeki haka bayan nagani you are fine."
Ya had'iye wani abu yace " kinga abinda akai?"

Kai ta d'aga mai tana hawaye, Jalal ya share nashi hawayen tareda cewa " meyasa ruwan nan yaki daina zubowa daga idona, inaji wani abu ya fad'amin ne."

Kallan tausayi tamai tace " Deen me ya kaika shiga harkar mutumin can? Kasanshi kuwa? Kasan wani irin mutum ne?"


Jalal ya kalleta ya d'anyi dariya tare da cewa " Koma wani irin mutum ne ai baifi karfin Allah ba, sannan ni ba tsoronshi nake ba kin manta nine?"

Tasa hannu ta dakeshi da karfi a kirji tace " Deen meyasa kake abu domin ni? Meyasa bazaka manta dani ba? Why? Why are you making me miserable. "
Ta sa wani irin kuja tare da tsugunawa akasa.
Jalal ya kalleta zaiyi magana Ammar ya karaso gun ya d'agata sannan ya kalli Jalal, Seemah ta kara sa kuka tace " Ya Ammar?"

Ammar ya mata alama datai shiru yace " wuce d'aki." Ya fad'a tare da goge hawayensa.
Seemah ta juya tai d'aki tana tafe tana waiwayen Jalal.






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 6? 6?




Ammar ya dawo da hankalinsa kan Jalal hannu ya mikamai suka gaisa, Ammar ya kalleshi yace " Jalal mutumin da kai magana dashi wannan mara mutuncin shine kakeso kacemana mahaifin Seemah ko me?"


Jalal ya kalli Ammar yace " ni kaina dana fara ganinshi ban amince ma idanuna ba."

Ammar yace " inaaa... da sake taya za'ayi Seemah wacce ba ruwanta me mutunci ace ta fito daga tsatson wannan mutumin? I just can't believe it."

Jalal yad'an dafashi yace " Ammar kamar ka manta fyad'e yana mahaifiyarta? Duk mutumin da zai ma wacce saura kwana biyu ya aura fyad'e ai kasan sai a hankali sai dai koni banyi zatan rashin imani da mutuncin sa yakai haka ba."

Ammar yai shiru, Jalal yai murmushi yacigaba da cewa " kamanta Allah ne ke fitar da rayyaye acikin mattace kuma mattace acikin rayayye? Please Ammar ka daure zuciyarka idan zuciyarka ta karaya tun yanzu ya kakeso Seemah tayi?"

Ammar yad'an ture hannunsa daga kafad'ar sa ya kifta ido yace " waya fad'ama zuciyata takaraya? Sannan ce maka nai mun zama abokai da har zaka wani dafani?"
Yanda yai maganar ne yasa Jalal yasa dariya yace " Ammar bansa kanada wannan cute site d'in ba, duk sanda muke had'uwa cikin d'aurewar fuska muke."
Ammar ya d'an harareshi yace " yanzun ma acikin b'acin ran nake ai."

Jalal ya kalleshi yace " tuba nake Ammar nasan akan me kake cikin b'acin rai sai dai nasani tuni Seemah ta cireni a ranta kaima kasani dazatamin magana fa sai data nemi izininka."

Ammar yai shiru kawai yana kallan Jalal aransa yace Jalal kenan.
A fili ya wayancewa da cewa " kaje falo nasan Dad nasan ganinka."
Jalal ya d'aga kai alamar to sannan ya kalli kofar d'akin da Seemah take ya wuce.

Ammar bayan yaga Jalal ya wucene shikuma ya wuce d'akin Seemah, knocking yai dama tana tsaye jikin kofar tanasan jin me suke cewa sai dai ta kasa jiyosu, bud'ewa tai Ammar ya shigo.
Kallanta yai ta kalleshi tanasan tambayarsa meya cema Jalal sai dai inaa bazata iya ba, ta daure tace " Yaya amma ai ba mutumin nan bane mahaifina bako?"
Ammar ya kalleta kai ta girgiza tace " haba dai yaya it can't be, mahaifi fa akace, da mahaifinane ina ganshi ai ina tunanin jikina zai bani munada alaka dashi amma ni farkon ganina da tsanarsa na wuce ta ya zakuzo kucemin mahaifinane?"

Ammar yad'an harareta yace " na d'auka Seemah ta tace ba ruwanta koma waye mahaifinta itadai Dad ne nahaifinta."

Da sauri tace " eh haka ne amma...amma...amma.."
Ammar yasa dariya yace " amma me? Yau kece kike in ina?ko rasa abin cewa kikai?"

Ta juya yai tare da rangwab'ar dakai, Ammar yai murmushi yace " karki damu kinji kinmanta nabarmiki Dad nina koma d'an gidan Abba?"

Juyowa ai tana dariya tace " kai yaya."
Yace "ahhbhh aikina ya biya tunda kinyi dariya."
Kallansa kawai tai batace komai ba, ya matso kusa da ita tare da turo fuskarshi kusa da ita yace " kallam fa?"

Tasa hannu tad'an ture fuskarshi kad'an sannan tace " kai Yaya."
Tai maganar kamar zatai kuka, yai murmushi sannan ya fita, har yaje kusa da kofa ya tsaya, jitai yace " Jalal nagunsu Dad."
Da sauri tace cema akai inasan insan inda yake?"

Yanakai nan yai waje yana murmushi, Seemah kam yana fita ta furzar da wata iska tace " Deen me kakeyi acan?"

Jalal kam bayan ya shiga azazzaune ya taddasu suna maganar Abdul, Dad yace " nasan Abdul fa, bansan ya akai ya canza haka ba, duk ba bayaji amma iskancinsa baikai haryai fyad'e ko shan giya ba, nadaisan yana shan taba, ina mamakin yaushe ya koma haka."
Abban Jalal yace " Abokan fa? D'an alokacin bazan manta ba shima kamar bayasan shawarar fyad'en da kuma kama Jalal kawai dai sun sugashi ne sannan yana kwad'ayin hakan dama a kasan ransa."

Abban Zaid ya kalli Jalal yace " matsonan Jalal."
Nan Jalal yazauna kusa da Junaid tare da gaidasu, Dad yai ajiyar zuciya yace " Jalal kasan mutumin nan mai karfi ne tunda Senate ne da mutane ke sanshi meya kaika yimai haka? Sai ka sanar damu."

Jalal zaiyi magana wayar Sagir ta buga Abban Zaid yace " d'aga mana."
Jalal ya d'aga tare da cewa " Sagir ya akai?"
Sagir cikin tashin hankali yace " Jalal duk an tsayar da saida Jaridun nan sannan duk 'yan jaridan nan sun watse daga gidansa."

Jalal yace " What?"
Sagir yai ajiyar zuciya yace " Jalal yazamuyi? Nasan yanzu kanka abin zai dawo."

Jalal yad'an mike daga gunsu Abba zai d'an fita, Dad ne ya rikosa yace " yi wayar anan."
Kallansa Jalal yai sannan ya daure yace " Sagir karka damu ai dama nasan hakan zata faru, in ba'ai hakan ba kenan ba mutum bane mai matsayi."

Sagir yace " to sai kazo."
Nan suka kashe wayar, Jalal ya kalli Dad yad'anyi murmushi yace " Dad is not a big deal."
Junaid ha kalleshi yace taya zakace haka bayan da alama Abdul is out to get you."

Jalal ya kalli Abbansa sannan ya kalli Dad yace " Dad zan koma Birnin gwari yanzu nasan nan zai nufa dan cimin zarafi."

Dad kallan Jalal kawai yake, Abban Zaid ne ya daure yace " Jalal ka cire hannunka daga abun mutumin nan, mu zamu karasa abinda ka fara."
Jalal ya girgiza kai yace " me kenan akai Abba? Na fara abu sannan inbarku ku karasa? Idan Abun yazo da downfall d'ina sai in jawoku mu fad'i gaba d'aya kenan?"

Ammar ne ya katseshi da cewa " Ni zan rakashi muje Birnin gwarin tare, Abba dukanki please karkusa hannu a wannan harkar."

Jalal ya kalli Ammar yai murmushi, Ammar yai saurin juya kai tare da cewa " malam daina min murmushi bancema munzama abokai ba tukun."
Dariya dukansu sukasa a falon, Abban Jalal yace " nufinka kenan kunzama abokai, dama can abokan ne ku."
Ammar yai saurin juyawa ya fita, Jalal yai kasa dakai yana murmushi, Junaid ya matso kusa dashi yace " Ammar tsoro yake karka tafi kai kad'ai wani abun ya sameka."
Jalal ya jinjina kai yace " nagane nima, bayaso ya fad'i abinda ke ransa ne."

Nan suka sakeyin murmushi.


Ammar d'akin Seemah ya koma, a bud'e kofar take, Seemah tana zaune Zahra na tsaye tana 'yar mita yanzu shikenan baza ai partyn ba? Nafa fad'ama kawaye na, wai meke faruwa agidan ne?"

Seemah ta girgiza mata kai tace " kedai fad'i gaskiya bawai partyn kikeso ba so kike kiga an kawo miki lefen ki."

Zahra ta turo baki tace " eh d'in nibama lefe ba na kosa ma ai auran."
Seemah tace " dama ai na sani basai kin fad'a ba da alama kekam kin gaji da gida."
Zahra ta murguda mata baki tace " kefa? Baki kosa a d'aura muku aure da Ya Ammar ba?"

Seemah tai shiru zatai magana Ammar yai saurin katseta da shigowa yace " Ahh Zahra na kula kina neman takurama Seemah ta."

Seemah ta kalleshi, Zahra tace " haka kace yaya? Shikenan nima zan rama ai." Tana fad'a tai waje.

Ammar ya kalli Seemah yace " baki mamaki ba daga fitata harna dawo?"
Tai murmushi tace " nasani Yaya damuwa kai da halin da nake ciki."

Yatsarsa ya nunata dashi yace "hmm wannan kanwartawa ta gama sanina."
Ta juyar da kai tace " wa zai sanka bayan ni? Tare fa muka taso yaya?"

Yai ajiyar zuciya yace " Haka ne kinci gari, amma naji dad'i naga kin ware."
Tace " ba dole ba duk yanda kai kokari gurin sani dariya?"
Ammar har kasan ransa yaji dad'in kalaman nan yace " ina neman izini."
Tace " name fa?"
Yai shiru can yace " Zan d'anyi tafiya ne, amma yau zan dawo."

Ta kalleshi tace " Yaya inzakai tafiya sai ka nemi izini ai kawai sanar dani zakai."
Yace " haka ne amma ni nafisan in nemi izinin."

Tai murmushi sannan tace " an baka Allah ya kiyaye hanya."
Yace Amin, sai naji kamar......."
Harararsa tai tace " zaka fara ko yaya?"


Ammar yace " sorry na daina, sannan ya d'aga mata hannu yai waje."
Tabi bayansa da kalli tare da cewa " Deen ko ya tafi shima? Ahhh yazanyi?"

Kai ta girgiza tace " me ya dameni ma da koma ina yake? Meye tsakanina dashi dazan damu?"






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*





@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com



_'Yan Uwa rabin jiki godiya! Jinjina! Ga 'yan uwana._
_Na sadaukar da wannan shafin ne zuwa gareku My Sweet babbar Yaya Aunty Faty, Yaya Faen and my dearest kanwa Meema ('yar fara) love you sooo much_=?
?=??




No. 6? 7?


Ammar ya koma falon inda Jalal yake, nan suka mik'e tare da yima su Dad sallama, Zaid ne ya shigo falon ko sallama baiyi ba ya kalli Jalal sannan ya kalli Ammar yace " shine zaku zame ku barni?"
Ammar ya kalleshi yace " Zaid mu zame kamar ya?"
Zaid ya burtso baki yace " ko ma miye I am in, dan kuwa dani za'ayi tafiyarnan."

Abbansa ya kalleshi yace " kai kuma me zakaje kayi? So kake kaje kawai ka hargitsa komai kome?"

Zaid ya shagwab'e fuska yace " ni wai meyasa akemin haka ne? Ni ba namiji bane? Koma menene nidai dani za'aje."


Jalal ya kalleshi yace " baka tsoro?"

Hararar Jalal yai yace " tsoro? Farauta zaku ko me? "
Junaid yai murmushin mugunta yace " Abba ina ganin ya kamata abar Zaid yaje, waya sani ko shima akwai tasa mahimmiyar gudun mawar dazai ba da?"

Abbansa yace " waye zai bada mahimmiyar gudub mawa? Wannan?"yafad'a yana nuna zaid da hannu.
Zaid cikin shagwab'a ya matsa gun Dad yace " Dad kaga Abba ko? San na kula bai yadda dani ba kallan soko kawai yake min."

Dad yace " to ya isa haka, yanzu dai kaje ka shirya kai ma ka je."

Zaid yace YES!!!!



Sun fito su uku, Seemah na tsaye a jikin kofar falo tana d'an lekowa kad'an,, ganin Ammar, Zaid da Jalal sun nufi mota a tare yasa tai saurin bud'e kofar ta fito, kallansu tai cikin mamaki.
Daurewa tai tace " Ya Ammar!"
Ammar ya juyo ya kalleta, murmushi ya mata sannan ya kallesu yace ina zuwa.

Zaid ya tab'e baki tare da girgiza kai yace " kuma wlh kar a shanyamu a tafi soy........"kallan Jalal dayai ne yasa ya kasa karasa abinda yake shirin fad'a.
Jalal dayakejin wani abu na kishi na tasomai ya daure tare da yin yake yace " karasa Zaid karka damu dani."
Yana fada ya kalli inda Seemah take, idanunta na kansa, ga Ammar na tafe kusa da ita, Jalal ya kurama Seemah ido, itama kallansa kawai takeyi har Ammar yazo kusa da ita bata kula ba.
Da mamaki Ammar ya kalli inda take kallo, ganin tana kallan Jalal yai shiru batare da ya katsesu ba, sai dai kasan zuciyarsa wani irin kuna ne ke ratsashi, haka zai zauna yana kallan Seemah daga gefe tana kaunar wani ba shi ba?
Jalal ne yai saurin dauke kansa daga kallan Seemah tare da saurin karasawa jikin mota ya bude ya shiga.

Seemah ta bishi da kallo harya shiga mota sannan ta juyo ta kalli Ammar da mamaki tace " yaya!"
Ammar ya kalleta sai dai duk yanda yakeso ya danne zuciyarsa karta gane ransa ya baci ya kasa.

Kallanta yai yace " naam"
Baki ta motsa dan ta fahimci ya dade agun, kasa tai da kanta da sauri tace " yaya I......."

Kai ya girgiza mata yace " Zamu wuce kar dare ya mana."

Ta kalleshi da mamaki tace " yaya wai da deen zaku tafi?"
Yamaimaita sunan Deen? Hmm haka ne da deen zamu tafi.

Ta kalleshi da mamaki yanda ya bata amsar, tace " yaya amma...."
Ammar ya kalleta tare da yi mata murmushi yace " karki damu Seemah kin manta kin bani izini?"
Ta d'an hade rai tace " amma ai bansan ba kai kadai bane."

Ammar yace " me? Bakyasan ki ganmu tare?"
Kai ta girgiza da sauri tace " a'a bafa haka nake nufi ba."

Yai sake yin murmushi yace " inje? Kar suyi ta jirana."

Ta daga kai tare da cewa " Amma me zakuje yi?"
Ammar yai shiru kawai yana kallanta.
Tai murmushi tare da cewa " shikenan Allah yakaiku lafiya."

Ya amsa da Ameen sannan ya juya.

Mota ya bud'e gaban mota gefen Jalal ya zaune.

Zaid ne a zaune ya hakimce.
Ammar a kalleshi yace " malam Zaid dan koma baya ko?"
Zaid ya kalleshi yace " kamar ya?"
Ammar ya furzar da wata iska yace " ahhh da ina tunanin baka number wata hadaddiyar yarinya dana gani amma da alama zan fasa."
Da sauri Zaid ya kalleshi yace " da gaske?"
Jalal ya guntse dariyarshi yace " gaskiya kam da alama zakai rashin yarinya.

Ai kan Jalal yagama magana Zaid ya haura baya da sauri.
Ammar yazauna tare da yin dariya Jalal ma dariya yasa basu san sanda suka tafa ba.
Sai da suka tafa kuma kowa ya kalli window irin waskewar nan.
Zaid ya matso da kansa yace " dariyar fa ta meye?"

Jalal ne ya tada mota yaja batare da ya bashi amsa ba.


Haka suka tafi Zaid na tasasu dariya har ya gaji yai shiru, motar tayi shiru kamar ba kowa, can cikin wata murya Jalal yace " nayi mamaki danaji zaka biyoni."
Ammar ya kalli window yace " sai ka daina mamakin tinda dai gamu a hanya."

Jalal ya jinjina kai ba??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ice komai ba.
Muryar Ammar yaji yace " Meyasa ka zama dan jarida?"
Jalal ya dan kalli Ammar kadan yace " Long wish dinane."
Ammar ya kalleshi ba tare da ya gamsu ba.

Jalal yai murmushi yace " why?bakai tunanin haka ba? Ko ka dauka saboda Seemah na zama?"

Ammar ya kalleshi da mamaki yace " me? Ba hakan bane?"

Jalal ya kalli Zaid dake bacci ta mirrow sannan yace " nidai nacema ba haka bane."


Ammar ya furzar da wata iska baice komai ba.

Shiru sukai har suka isa ba wanda ya sake magana.

Suna isa suka fito dukansu suka nufi lungun, Zaid kam ya kasa jurewa yace " wannan lungun fa...."
Ammar ne ya harareshi hakan yasa ya hadiya maganarsa.

Sai dai me? Suna isa suka tada sai watsi ake musu da kaya daga ciki ake cilo kaya zuwa waje, abubuwa sai farfashewa suke.

Idanun Jalal ne suka kada sukai jaaa, wani mugun bakin ciki ne da takaici suka ziyarceshi, a zuciye ya shiga cikin gidan daidai nan wanda ke watsi da kayan ya daga tabirma zai cillo.
Jalal ya kalleshi, bai taba ganin shiba, ga Zainab a tsugunne a kusa dashi tana kuka tana kuma bashi hakuri, Mutumin sai ihu yake yana cewa a kira mai Jalal.

A zuciye Jalal ya karasa ya rike tabirmar, mutumin ya kalleshi

31 / 37