JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   5 / 37

12K to 15K   out of 109.4K words

Bad."


Nikam Ayusher nace mefa?


Jalal ya fito cikin takaici ya karasa office d'insu sai da abinda yakara d'aure mai kai Manager ya kara gani a tsaye a kofar, yace lafiya? Manager yace " ance in kaika da kaina, d'an haka wuce muje." Jalal ya kalleshi yace ina?
Hannunsa manager d'in ya kama suka fara tafiya, Jalal ya kwace hannunsa yace itace dai? A hankali Manager ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ya d'aga kansa alamar eh, Jalal yace zanje da kaina, nan ya fara tafiya yagama shirya yawan rashin mutuncin dazai kwara mata.
Da karfi ya bud'e kofar ko sallama baiyi ba, sai dai me? Habib ya gani zaune a kujerar sa Seemah na tsaye tana waya jikinsa ne yai sanyi a hankali yace "am sorry."
Habib ya kalli Seemah dake ta shagwab'a a waya, Jalal kam takaicin yanda take shagwab'a yakeyi amma da alama ko saurayinta ne, sai dai jin tace " Dad sai anjima." Yasa ya d'ago, Dad?
Maganar Habib ce ta katseshi dayace " Seemah wannan ne?"
Seemah ta kalli Jalal tace eh yaya please.
Habib ya kalleshi yace " d'an Allah so nake ka taimakamin, kanwata ce kesan zuwa yin shopping to nikuma inada aikin yi shine tace tanaso kad'an kaita."

Jalal da mamaki ya kalli Seemah ya mata kallan jiya baki daddara ba ko? Baki ta murgud'amai tace " ni yaya dama shi ka bani a matsayin driver na." Wani kallo da Jalal ya watsa mata ba ita ba har Habib sai dayasha jinin jikinsa, ganin yanda ya kafeta da ido yasa ta had'iyi wani yawo tace" Wasa nakeyi maida wukar."
Habib ya d'an kakaro dariya yace " karka damu akwaita da tsokana, she is just joking."
Sai a lokacin Jalal yad'auke idanunsa, sannan yace " yau ne kad'ai zan kaita ko?"
Habib ya d'aga kai yace yau ne kad'ai, in ka kaita ka karasa da ita gida, Jalal yace to sannan ya kalleta yace " muje ko Madam?"

Seemah ta anshi key sannan ta fito.

Sunje shiga mota Seemah harta bud'e baya Jalal ya sa hannu ya fizgota ya sata a gaba sannan ya rufe shima ya shiga, kallansa tai tace " meye hakan kuma?"

Jalal yace tambaya kike? Batace komak ba kawai ta juya kanta tana kallan window, Jalal ya tada mota sun d'an fara tafiya tace " wato bazaka bani hakuri ba ko?"
Jalal ya kalleta yace " laifin menai dazan baki hakuri? Bakya tunanin ke zaki bani?"
Juyowa tai tace " kamanta me kamin ne?"

Jalal ya saki murmushi yace " au duk wannan abun da kikemin so kike in baki hakuri?"
Ta d'an turo baki tace " eh mana, kuma inaso kabani yanzu."

Jalal yace " lalai kin da aiki a gabanki."

Tace sai in taka burk'i yanzu, ko in bud'e kofar motar, uhmmm ko insa ihu in ma sharri.

Ga mamakinta dariya taga Jalal yasa abinda bata tab'a gani ba, dariya sosai yai, sannan ya kalleta yace ko zaki gwada?

Ganin yanda take kallansa yace " kallan fa?"
Ta kifta ido tace " dama kana dariya?" Da sauri ya had'e rai yace " baki gani daidai bane, ba dariya nai ba."


Seemah tai murmushi tace "yau naga side d'inka kala kala, d'azu ka makamin kallo kamar zaka dakeni yanzu kuma dariya?"

Jalal ya had'e rai ya cigaba da tuk'insa, Seemah ma shiru tai sai dai murmushi bai bar fuskarta ba......







? *NWA*
@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MOHD*




No. 1? 2?


Habib kam sam jiyai gidan ya isheshi hakan yasa yace zasu wuce, sun musu sallama sannan suka fito, harsun zauna a mota yaga yanda idan Seemah ya kad'a yai jaa kawai ya bud'e motar ya koma ciki, suna zaune sunyi tagume sallamar Habib ne ya katsesu, da sauri suka mik'e suka fito.

Habib yace " har na shiga mota naga kamar ya kamata inji menene dalilinku na k'in sakema Seemah?ko d'an bata tab'a zuwa ba sai yau?"
Kawo yai saurin cewa shine dalili yaza'ayi ace sai yau zata tab'a zuwa gaidamu?
Kallansa Habib yai bayajin zuciyarsa ta gamsu da maganar saidai tunda sunce hakan yace " ayya amma kawo kasan ba laifinta bane Dad ne yake hanata zuwa."

Hajiya tace to jeka ku tafi ko ka manta kanada aiki ne?
Nan Habib ya juyo ya shiga mota, dad'insa d'aya yana shiga yaganta tana waya da Ammar sai dariya take, hakan yasashi dariya, sun fara tafiya shima yanata janta da hira, bayan sun shiga Abuja ne ta kalleshi tace "yaya muje Company sai anjima sai in koma gida."
Yace "shikenan dama yau driver d'inki zaizo sai yazo ya d'aukeki"

Murmushi tasaki a ranta tace Jal we will meet again.

Suna isa Company d'in Sagir yazo ya sanar ma habib akwai meeting dazasuyi yanzu, nan ya kalli Seemah yace kije office d'ina tace to nan ya juya a hankali tace Sagir? Juyowa yai yazo kusa da ita, tace " ina Abokink?"
Cike da mamaki ya kalleta? Yace wa kenan?
kallansa tai batare datace komai ba hakan yasa yace Jalal? Ta had'e rai tace " yana ina? D'an yau sai na zabgamai rashin mutunci.

Kai ya jinjina yace hmm yana office a k'irashi ne?, tad'an juya kai tace inane office d'in ku ba meeting zaku shiga ba? Nuna min kawai.

Yace a third floor yake kina shiga daga hagu zakiga Department d'insu, tace ok ta juya tai gaba, Sagir yace " Yau kuma wani fad'an za'ayi?"

Elevator ta hau ganin ba kowa yasa tad'an fito da madubi daga jakarta tad'an duba fuskarta murmushi tai sannan tad'an sa janbaki kad'an tace " yau sai ka kasa ganeni."
Tana isa tai inda akace tare da murd'a kofar tai sallama, office ne babba sai dai kowa da desk d'inshi sai gurin da aka kewaye ma manager, sunajin sallamar suka juyo gaba d'aya suka zuba mata ido, kallansu ta shiga yi sai dai bataga Jalal ba, karasawa tai ciki tace " Jalal nake nema?" Wani ya matso kusa da ita yace ga desk d'inshi nan ya fita inaji ko kasa yaje submitting d'in proposal.

Desk d'in ta kalla sannan tace bari na jirashi, karasawa tai ta zauna a inda yake zama tare da bud'e takardun dake gun, kowa sai kallanta yakeyi, manager d'inne ya fito ganin Seemah yasa ya karasa da sauri yace " Ranki ya dad'e me kikeso? Ai da baki zo ba kin turo kawai."

Had'e rai tai tace " inasan ganin Jalal ne d'an yau banajin zan iya kyaleshi."
Yawo ya had'iya aransa yace Jalal me kayi?
A fili yace " ayi hakuri Madam......."
Katseshi tai tace " asa a k'irashi yanzun nan."
Nan ya fita da sauri yai waje, Seemah ta kalli ragowar tace " kucigaba da aikinku." Wata mace ce tad'an matso kusa da ita tace " laifin me ya mik'i? Naji dad'i da kikace zaki hukuntashi dama haushi yake bani, farkon zuwa na ina bala'in san mutumin nan har abinci nake zama a gida in had'omai sai dai duk wannan wahalar danake bazai ci abincin ba kuma baya kulani, rannan ma ba ka ra yacemin bayasona."

Seemah ta saki dariya tace " ke meya kaiki san wanda baya sanki? Ai kece mak kuskuren ba wani ba."
Haushi ya kama matar ta juya ta zauna a ranta tace " Allah yasa kema kiyayyace ba so kike masa ba."

&&&&&&&&&


Jalal ne ya shigo da sauri yana neman me nansa, kallan kowa ya shiga yi yaga suna nunamai desk d'insa karasawa yai desk d'in d'an baya gano kowaye tunda ta juya kujerar baya tana game, jin sallamar Jalal yasa ta kashe game d'in tana jiran k'arasowarsa.
Jala mamaki yake wani rik'eken ne wannan? yana zuwa gun yace " excuse me"

Seemah ta juyo da kujerar ta cik'e da mamaki ya kalleta yace " You?" Gira yad'agamai sannan ta mik'e tare da had'e rai tace " Follow me."
Tana kainan tai waje, hartaje kofa taga bashi da niyyar tahowa haushi ya kamata ta juyo tazo inda yake cikin magana mai rad'a tace " so kake in jaka da kaina?"
Yace muje.

Sun fito ta kalleshi tace " kar mutane suganmu ka sameni a gun jiya rooftop, tana kainan ta wuce.

Iska ya furzar yace " Ahh wannan tagama rainani, me? In sameki a ina?" Sai a lokacin ma yabi bayanta da kallo, atamfa? Shi da sam bai kula bama, daga kanta yafara kallanta har kan takalmin datasa mai tsini sosai, tayi kyau sosai, wani b'angare na zuciyarsa ya fad'a da sauri ya girgiza kai sannan ya wuce shima.

Ta rigashi isa hakan yasa ta karasan can bango tana kallan kasan titi yanda motoci suke wucewa, Jalal ne ya bud'e kofar tare da kallan inda take tsaye murmushi yai sannan ya karasa gun, gefenta kad'an yaje ya tsaya, batare da ta kalleshi ba tace " a haka mutum sai yaga kamar kowa na duniya yana cikin kwanciyar hankali."

Kallanta yai sannan ya kalli kasa yace " a binda mutum yake gani daga nesa dama haka yake ai sai kiga kamar kowa yana walwala, amma me ya kawo ki office d'inmu?"


Juyowa tai ta kalleshi sannan tace " ya kagan ni?"

Kallanta yai kad'an sannan yad'auke kai yace " bangane yaran ba?"
Leb'enta tad'an ciza sannan tace " kalleni da kyau ka gani baka ga komai ba?"
" Banga komai ba, akwai abinda yakamata in gani ne?" Ya fad'a yana kallanta.
Haushi ya kamata ta juya cikin fishi zata wuce tsinin takalminta ne ya shige d'an rami tai wala wala zata fad'i da sauri yasa hannu ya tarbota kallan juna suka fara, Seemah kam zuciyarya sai duka take, kallanta yai sannan yace " da saninki ko? So kike in tare ki."
Harararshi tai tace " nina saka?" Baya yai da ita kamar zai saketa, kara tad'an saki yace " au ashe kina tsoro."
Cikin shagwab'a tace " da yarda ni zakai?"
Kai ya rangwab'ar yace " sai in yadda ke indai baki fad'amin me zan gani ba."

Hannu tasa ta rufe idanta a hankali tace bakaga kayan danasa ba?

D'agota yai ta tsaya daidai sannan ya juya ya kalli titi yace " au sai yanzu na kula ai."

Haushi ya kamata tace " hakama zakace?"

" a ina kika ari kaya? D'an a yadda kika nuna baki da wani kayan hausawa sannan jiya kika siyo naki nasan a k'ala baza........"

Zuciya ta kawo mata wuya jakarta ta d'aga ta kwad'a mai a kafa, tace " kace ka gani ko yamin kyau shine bazaka iya ba? Gwara ka cimin mutunci?"

Juyowa yai yace zan iya tafiya?
Haushi yakara kamata tace kabar kasar ma,

Juyowa yai zai tafi sai dayaje kusada kofar fita ya juyo yace " kayan kasarmu sunfi miki kyau."
Yana kainan ya fita, kallan kofar tai sannan tai murmushi tace " kafad'i hakan tun d'azu shine bazaka iya ba?" Baki ta murgud'a sannan ta juya ta cigaba da kallan titi tana kallo tana murmushi. .....













? *NWA*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?





Na *AYUSHER MOHD*


NO8?




Likita yazo ya dubata, wahalace kawai da yunwa suka had'un mata nan ya bata magani ya tafi, Habib ya kalli wayarsa dake ka ra yai shiru ya rasa mai zaice d'an tun rana Dad ke k'iransa akan yaji Seemah shiru, yanason lale abashi 'yarsa suyi magana.
Kallanta yai sannan ya kalli wayar, jiyai ance " Dad ne ko?" Habib ya kalli Seemah yace " eh" hannu ta mik'amai ya bata wayar daga kwance ta d'aga wayar tare da cewa " Dad d'ina."
Dad yace " Princess ina kika shiga? Bayan tun rama nake nemanki, sannan ya naji muryarki haka?"
Da sauri tace " Dad bacci fa nakeyi yaya ya tasheni."
" Ayya kiyi hak'uri ban sani ba, tunda naji muryarki yanzu mayi waya da safe."
Dad ya fad'a cike da namaki ganin seemah ba baccin wuri takeyi ba.
Seemah tace "to Dad nyt, love u." Tana kai nan ta kashe wayar tare da sakin ajiyar zuciya.
Habib ya kalleta yace " Bari a kawo miki abinci." Kafin ya mik'e Farida ta shigo d'auke ta tire ta ajiye kusa da Seemah tace " Seemah tashi kid'an ci wani abun."
Habib ya taimaka mata ta zauna, Farida ta zuba mata nan tafara ci, tad'anci dayawa kafin tace ta koshi, Farida ta zuba mata juice ta sha sannan tajingina.

Habib ya kalleta yace " Seemah meta faru wai?ance da wani kuka tafi, waye shi?"
Tai ajiyar zuciya tace
" Yaya irin wannan tambaya?"
Habib ya had'e rai sosai yace " ki fad'amin wanene in ba haka ba indai nai bincike da kaina, banajin zan barshi haka."
Shiru tai can tace " nima ban sanshi ba yaya, kawai dai da Aisha takusan kad'ashi ne na fita bashi hakuri sai yake cemin kamar jiya ya ganni a Company d'in dayake aiki, nikuma ganin a Company d'inka yake aiki yasa nace ya karasa dani shine yai wani gurin dani."
Habin ya mik'e cikin b'acin rai yace " ki kwanta ki huta gobe karfe 10 zansa a d'aukoki ki duba kaf ma'aikatan Company d'in ki nuna min shi."
Gaban Seemah ya fad'i a hankali tace to yaya.
Nan ya juya ya fita ta bishi da kallo, itakam menene nata na kare Jal? Meyasa batasan asan shine?

Mik'ewa tai ta shiga toilet tai alwalata dawo ta tada Sallah, bayan ta idar ne ta mik'e ta hau gado, Aisha ce ta kalleta tace Sannu Seemah, sannan d'azu Special Bros ya k'iraki, da sauri ta d'au waya ganin missed call 40 ta duba duk yayinta 3 sun nemeta da kuma dad sai dai na yaya habib yafi yawa tunda shi kad'ai yasan meke faruwa, layin Ammar ta d'anna, ringing 2 yad'aga ta saki murmushi tare da cewa" Oppa ya? Da alama yau kayi missing d'in kanwarka dayawa."

Murmushi yai yace " Seemah kinsan dai bana jure rashinki ko? Sanda na tafi South Korea wani Conference sau nawa muke waya dake?"
Dariya tai tace " Kai yaya wayar fa damukeyi yawanci ni nafi nemanka."
"Seemah ni dai banasan haka daga yau na k'ayade mana waya sau 8 a rana, ni zan k'ira sau biyar ke ki k'ira sau 3 duk wanda yai missing k'ira ko d'auka zai biya kud'i."
Dariya sosai tayi tace " shikenan yaya deal?" Yace deal.
Sun dad'e suna waya Aisha dake kwance tanata mamaki wannan dabad'an yayanta bane lalai sai ta ce su masoyane.


0
0
0
0
0
0
0
0
0
0
0
0

Seemah ta kwanta bacci tad'ade kafin tai baccin sam ta rasa meke damunta, sai dai 1 thing is cleared sai tai ta hango Jalal sanda yana tsaye a waje ita kuma tana mota, bargo taja ta rufe kanta gaba d'aya sai dai duk da haka ta sake ganinshi yaye bargon tai sannan ta d'an sa ihu kad'an tace " Frustration! !!!!! Yau kuma meke damuna? Can tace nama gane, tsabar tsanar dana mai ne."
Tadad'e bata bacci ba sai can ya sace ta.

b&b&b&b&b&b&b&b&b&



9 ta tashi tai wanka tasa kayanta, yau doguwa ce rigar sai dai ta kanti ce mai bin jiki ta d'auko har zata fito sai kuma ta koma ta cire ta kara duba akwatinta, riga da wando ta d'auko na pakistan da yaya junaid ya siyo mata dayaje india tasa tare da yafa mayafin, tayi kyau sosai.
Ta sauko kasa ta taradda Aunty Farida kad'ai nan tai breakfast ko tambayar Aisha batai ba, kafin ta gama har driver yazo, Nan sukai sallama da Farida ta fita.

Suna isa company d'in ta sauko a hankali, Habib tagani a tsaye mamaki ya kamata a hankali ta karasa, sai dai abinda yabata mamaki tun daga cikin bakin kofar company d'in mutane suka jeru, ajiyar zuciya gai takarasa gun habib, yace " muje ki duba ga kananan ma'aikata anan manyan kuma na inda muke meeting." kallan yaya tai a hankali tace to.

Sun fara dubawa tana tafe yana binta a baya, sai kallan mutane takeyi, kowa tagani tace bashi bane, sai da suka zo kusan karshe, idanunsu ya had'u da Jalal, kallan juna sukai ta kuramai ido mamakinta babu alamar tsoro a idanunsa, jitai Habib yace " Shine?" Da sauri ta girgiza kai alamar a'a, mamakine ya kama Jalal da sagir, me take nufi? Jitai Jalal yace ki kara dubawa dai.
Yawo ta had'iya sannan ta kalleshi ta wuce na gaba dashi, har taje karshe tace ba kowa, nan sukai hanyar inda manya suke, ba shakka sunji haushin wannan rainin hankalin, wai an tarasu saboda wata 'yar yarinya, Seemah ta duba nan ma tace ba kowa, Habib yai shiru can ya kalli Sagir yace kaita office ni zamuyi meeting.
Suna fitowa suka had'u da Jalal, ya matso kusa dasu kad'an yace " Follow me. "
Tad'an harareshi tace dalili? Yace " karki b'atan rai ki biyoni ko?"
Nan ta kalli sagir tace ina zuwa.
Elevator ya bud'e ya shiga itama ta shiga, sun yi shiru har suka isa last foor suna zuwa ya karasa sama itama ta bishi, saman ba

5 / 37