JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   35 / 37

102K to 105K   out of 109.4K words

ya juya harzai fita sai kuma ya fasa ya koma ya tsaya tare da cewa " Kanwata ko in juya ne?"
Kallansa tai da sauri tare da juyawa ta goge hawayenta ta mike tace " yaya yaushe kazo?"

Ammar yadan hade rai kadan yace " nafi awa biyu fa anan."
Cikin tsananin mamaki ta kalleshi tace " da gaske? "
Dariya yai yace " lalai taya za'ai ki yarda?"

Harararsa tai tace " Yaya wato dai kai na kula inba tsokanata kaiba sam bakajin dadi ko? "

Shiga ciki yai kusa da ita ya tsugunna kasa ya dauko agoggon data yar tana saurin mikewa, kallan agoggon yai sannan ya mike tare da mika mata, kallansa tai batare da ta amsa ba, kallanta ya sakeyi yace " amsa mana nasan abune mai mahimmanci a gunki."

Kallansa tai tareda shan jinin jikinta tace " Yaya ba......"
Murmushi ya mata yace " ansa mana."
Hannu tasa cikin sanyin jiki ta amsa, yace " me? Kinaso ki mai sallama ne kafin biki?"

Kallansa tai cikin tsananin mamaki, da sauri ta juyamai baya tace " bafa haka bane yaya, kawai ganin agoggon nai."

Ya dawo gabanta tare da daga kai yace " nasani Seemah nasan komai hakan ne yasa banaso kidinga boyemin komai, nine na tambaye ki bawai ke kika tambayeni ba."

Idannunta ne suka ciciko ta girgiza kai tare da cewa " how can I......?"

" I am okay!" Ya fad'a yana kallanta, tai kasa dakai, yace " banaso ki dinga tunanin bakimai sallama ba..."
Ganin tayi kasa dakai ya juya tare da cewa " in bakyaso shikenan."
Yana fada ya juya kamar zai wuce, jiyai ta riko hannunsa ta baya, ya tsaya batare da ya juya ba, duk da kishin dake damunsa amma bayaso yaganta cikin wannan halin saboda shi.
A hankali Seemah tace " Yaya zan iya?"
Bai juyo ba ya daga mata kai tare da daurewa yace " banine na ce ba?"
Ta goge hawayen ta da d'aya hannun tace " yaya zan mai sallama tare da ajiye duk wani ragowar abu dake zuciyata, bazan sake tunaninsa ba bare insa ka kaji ba dadi ba."

Ammar ya daure ya juyo ya kalleta tare da mata Murmushi yace " karki damu Kanwata farincikina bai wuce naganki kina farinciki karki damu dani farincikina na tattare dake."

Yai ajiyar zuciya tare da cewa " in har kinaso ki ganni ina farinciki to ke zan jira kiyi farinciki kafin ni."

Seemah ta share kwallarta jikinta yai mugun sanyin, tausayin Ammar ya kara shigar mata zuciya, zare hannunsa yai yace " kishirya in ajiyeki, in yaso sai ya dawo dake."

Yana kainan ya fita, kallon tsananin tausayi ta bishi dashi, zama tai a gun tare da runtse ido tace " Seemah meke damunki? Taya zakice zakije bayan kinsan koyace kije dolene yaji haushi?"

Ta dade a zaune kafin Ammar ya kirata yace tafito yana jiranta.


Jalal kam zauje yake a dan karamin gidan daya kama, saboda ya sai gida babba yanzu a kaduna inda Umma da kuma matarsa Zainab suke zaune acan, Zahida kam itama jiki ya fara sauki sosai Zaid kam kusan duk karshen sati sai yaje, tun Zaheeda na wase wa harta fara saki gashi ba laifi yanzu tana iya takawa kadan kadan inta rike sanda.

Takardu ya gama dubawa sannan ya mike danjin yunwa ta fara kamashi, kallan calendar dakinsa yai ya zagaye wata number da jan biro, karasawa yai jikin calender yace " saura 7 days?"
Ajiyar zuciya yai sannan ya kalli wayarsa dayaji tayi kara alamar text, dagata yai yaga sako ne ga mamakinsa daga police station ne, wai Abdul na nemansa, yataimaka ya ziyarceshi."



Wata iska ya furzar yace a fili " Allah yasa ya daidaita tunaninsa akan 'yarsa."

Window ya zuge ya kurama titi ido, yaushe rabansa da Seemah?
Kai ya girgiza tare da cewa " Ahhhh...."






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*





@&.

Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Arewa hausa novels
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)

WHATSAPP NO:
+2347039625239
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


_Ina kara godiya da jinjina gareku 'yan group d'ina na *Queen Bee* da kuma *Ayusher Fan Club* na gode kwarai da kaunar ku.......Allah yabarmu tare Ameen_


No. 7? 5?



Jalal na tsaye jikin window yaji kiran Ammar daga wa yai yana tsokanarsa Ango da kanka?
Ammar ya kalli Seemah dake zaune a gefensa tayi shiru yace " ka fito ina wajen gidanka."
Jalal yace " ok ganinan dama ina so muce wani guri dakai."
Ammar yana kashe wayar ya kalli Seemah datai shiru, yace " zaki kai minti nawa?"
Kallansa tai idanunta suka dan canza kala tace " ni kati kawai zan bashi sai sallama da godiya daxan mai sannan in bashi hakur....."

Ammar jiyai zuciyarshi takasa jure wa ya kalleta hakan yasa tadan juya fuska tace " kajirani anan yana fitowa zan fita minti 10 ma ya isa."

Ammar baice komai ba ya juya ya kalli hanyar kofar da Jalal zai b'ulo, itama shiru tai tana tunanin anya ta kyautama Ya Ammar?
Kallan inda Ammar yake kallo tai daga nesa ta hango Jalal ya fito, Jallabiya ce a jikinsa fara sai dai tamai kyau, ido ta kuramai gani tai kamar yanzu yafi da kyau jitai zuciyarta ta shiga bugawa ta kasa dauke idonta daga kanshi, Ammar daya juyo dan yi mata magana yaga yanda take kallan jalal jiyai wani kishi ya taso mai, haushin kanshi ya fara ji menene dalilinsa na barinta taga Jalal? Anya yasan me yakeyi kuwa?

Har Jalal ya kusa isowa motar, Ammar ya kalleta tare da daurewa yace " Ki sauka kije kinga cema Dad nai xamu anso dinkinki, kallan Ammar tayi tace " yaya mu tafi kawai."

Da mamaki ya kalleta yace " kin fasa sallamar daban hakurin?"
Kallansa tai idanunta sun ciciko tace " Yaya banaji zan iya......"
Ammar zai yi magana kawai Jalal shikuma zuciya daya ya bud'e kofar inda Seemah take da tunanin zama a gun dan suje inda yace, glass d'in motar irin wace na ciki yana ganin na waje ne amma na waje baya ganin na ciki, ga mamakinsa Seemah ya gani zaune da sauri ya maida kofar ya rufe jikinshi a sanyaye, zuciyarshi ce ta fara bugawa da sauri.

Juyawa yai kawai maimakon ya koma gida kawai ya kama tafiya, Ammar ne yabishi da kallon tausayi sannan yace " Seemah bazakije ba?"

Jiki a sanyaye ta bud'e kofar, dan tunda suka hada ido da Jalal taji gaba daya jikinsa ya kama rawa ta fita tare da kallan Jalal daya tsallaka titi kamar ta kula kawai tafiya yake hakan yasa ko Ammar bata sakema magana ba balle ta rufe kofar tai gunsa da sauri.


Sam hankalinta nakan Jalal, So take ta tsayar dashi gashi batasan ya zatai ba, Ammar na jingine a mota yana kallanta, tazo tsallaka titi wani mai babur ya taho a guje, karar da Ammar yai na kiran sunanta yasa Jalal juyowa, da gudu ya taho gunta, itakam sam hankalinta nakan Jalal ganin ya nufota da gudu yasa ta tsaya cak, ta manta sam a titi take.

Saura kiris mai babur yai gaba da ita Jalal ya fuzgota, yai baka tim, Tsoro ne ya kamata, ta dago cikin firgice, tare da fara jijiga Jalal, hawaye sai malala suke tana kuja tana kiran Deen! Deen.

Ammar ma daya taho da gudu yai turus ganin Jalal a kasa, ganin yanda Seemah take kuka yasa hankalinsa ya dawo, matsowa yai tare da cewa " Jalal!"
Ido Jalal ya bud'e tare da kallan Ammar yace " Ammar dan taimaka ka tayani na mik'e."

Seemah ce ta kalleshi cikin mamaki au dama yana jinta? Mik'ewa tai tare da fara goge hawayenta, tace " Ya Ammar kacemai mu tafi asibiti a dubashi."
Mamaki ne ya kama Jalal, bai kalleta ba shima ya kalli Ammar daya mikamai hannu ya kama sannan yace " Ammar kacema matarka basai naje asibiti ba."

Ammar ya karasa dagashi tare da kallan Seema sannan ya kalli jalal yace " ni ba sakon wanda zan isar, Amma Jalal ka tabbata zaka iya tafiya?"
Jalal ya dan cizi leb'ensa kadan yace " karka damu z......"
Seemah ce ta katseshi da kallan Ammar tace " Yaya a'a mu kaishi asibiti please kaga saboda nine."

Jalal bai kalleta ba yace " nace bazani ba, gida zan koma."

Seemah kam daurewa tai ta matso daf da Jalal sun kusa isa mota, tace "kalleni."

Jalal yaki kallanta, ta kalli Ammar sannan ta kara cema Jalal " Deen please. ..."
Jin yanda tai maganar yasa Jalal ya kalleta a sanyaye tace " Deen muje asibiti please. "

Ammar kam da tundaga faduwar Jalal yasa duk jikinsa yai sanyi, ya kalli Jalal yace " Jalal muje asibiti a dubaka inba sokake hankalinmu yaki kwanciya ba."

Jalal bai magana ba har suka karasa motar, Seemah da sauri ta bud'emai gaba, ya kalli Ammar yace " A baya zan zauna."

Jiki a sanyaye Seemah ta maida kofar ta rufe tare da bud'ema Jalal baya, Ammar ne yataimaka mai ya shiga, gyambon dayake fatan ya warke shine ya mik'e shikadai yasan meyakeji ganin Seemah a kusa dashi kuma wai ankusa bikinta, jiyai kamar ya dauketa su gudu, hakan yasa bayasan kallanta bare yimata magana saboda shikadai yasan meke ranshi.


Sun fara tafiya Seemah dai a zaune kawaj take sai dai akai akai tana goge hawayenta, Ammar yai shiru a mota kawai tuki yake, sai taimakon Seemah da Jalal yai shi kuma ya buge, ga Seemah tun dataga Jalal ya buge take kukan nan , wani irin so Jalal kema Seemah?

Tambayar dayake nanatawa a zuciyar sa kenan har suka isa asibitin, bayan yaga likita nan akasa a mai X ray.

Seemah tai shiru a wajen dakin daya shiga tana tuno yanda Jalal ya buge, Ammar kam yana gurin likita, Jalal na fitowa ya dan tsaya a jikin kofa yana kallan Seemah batare data sani ba, jin kamar ana kallanta yasa ta juya, da sauri Jalal ya dauke idansa tare da cewa " Ammar fa?"

Seemah ta mik'e tsaye tace " ba dai wani abun ko? Ba dai wani abun ko?"

Kallanta Jalal yai zuciyarshi ta kara karyewa, a hankali yace " kar ki damu ba wani abun."
Ta matso kusa dashi tace " Deen meyasa d'azu zaka taimakamin? Kana tunanin zanfi farin ciki ne in ni banji ciwo ba kaikuma ka ji?"

Kallanta Jalal kawai yake cikin wani yanayi, ta share hawayenta tace " me yasa baka barni ba? Kasan yanda nakeji kuwa ganinka cikin wannan yanayi a maimakona?"


Jalal ya d'auke idansa tare da daurewa yace " ko waye ma naganshi cikin wannan yanayi zan taimaka mai, ya wuceta zai wuce, sai dai tsayawa yai cak ganin Ammar ya juya baya, da alama ya gansu tarene yasa ya juya baya, Jalal na kallansa ya gangara yai wata hanyar.

Tausayin kansu ne ya kamashi, me yasa zuciyarsu zataso mutum daya? Why?

Muryar Seemah yaji kamar tasan me yake cewa tace " Deen ka taba tunanin ya nakeji a cikin raina? How can u walk away from me bayan kana ganin waye ya kawoni dan inma sallama? Meyasa zuciyarka bata tunanin halin danake ciki?"



A hankali Jalal ya juyo idanunsa sunyi jaa sosai kamar masu shirin kawo ruwa cikin raunanniyar murya yace " Meemah I am okay! Kije gun Ammar I think shine yake bukatarki."

Kallansa tai jiki a sanyaye tace " bam gane ba."

Ya kalleta da raunannan idanunsa yace " ta ya ma zakisa Ammar ya kawoki nan? Me yasa bakya duba halin dazai shiga? "


Jiki a sanyaye ta kalleshi, Jalal ya juya kamar zai tafi da sauri tace " I am Scared."
Cak ya tsaya batare da ya juyaba, ta cigaba " zuciyata na tsoron kar inyi aure ba tare da na ganka ba."

Jalal ya juyo ya kasa kuma danne abinda ke ransa, cikin wata irin murya yace " what about me?"
Cikin tsananin mamaki ta kalleshi, yace " kinsan halin da nake ciki me zai sa kizo gurina ki nemi tada min hankali dayawa? Meemah kin dauka ni basan ganinki nake ba?"

Yai ajiyar zuciya tare da girgiza kai yace " noo."
Kawai banaso ran mutane dayawa ya b'acine ta sana diyyar mu."

Ya danyi hucci kadan sannan ya juya ya fara tafiya, kuka Seenah ta cigaba dayi, tun tana kallansa har ya bace mata.


Jalal kam gate kawai ya wuce ya tari babur yahau.

Sai text yama Ammar akan yaje ya dauki Seemah shi ya wuce gida, karya damu buguwar batai karfi ba.

Ammar na ganin sakon ya taho gun da sauri, a tsugunne yaga Seemah tana kuka wiwi, tsayawa yai daga nesa kawai yana kallanta zuciyarsa sai kuna take, ba abinda ya tsana irin hawayen Seemah.

Sai data gama sannan yaje ya mikar da ita suka wuce gida.

Jalal kam da yamma yaje gun Abdul, rokansa Abdul yai akan yana san ganin Seemah.


Jalal ya fadamai zai sa Ammar ya kawota duk da yasan ba lalai tazo ba.
Jalal duk ya canza da ya dade bai ga Seemah ba amma yanzu tunda ya ganta yaji hankalinsa yaki kwanciya jiyake kamar yafi santa yanzu ma.

Haka Seemah tun bayan sun rabu da Jalal ta zama maman shiru, tsakaninta da kowa a gidan bai wuce gaisuwa sai eh da a'a.

Ammar kam shima ya shiga wani yanayi balle tunda yaga Seemah ta canza gaba daya, Jalal ya sanar dashi Abdul na nemanta amma daya sanar da Dad yace " ya bari sai andaura aure sai suje tare."




Duk abinda akasama rana tofa lalai zaizo da sauri, yau gashi ta kama ranar alhamis ranar kamu kenan, hidima kam sai yinta akeyi, kowa ka kalla yana cikin farin ciki yake.

Jalal kam yau da zazzabi ma yatashi a jikinsa, a kwance yake tun dare gashi ba kowa a gidan shikuma baisan kiran ko Sagir ne, Seemah ma kawai yake takeyi dan batasan Dad da Ammar su gane.
Sai dai Ammar tun da suka bargun Jalal yasan halin datake ciki.

Anyi kamu na gani na fada a gidan Abba, Amarya Zahra da Seemah ansha kyau, haka aka gama taru lafiya sai kuma washe gari daurin aure.

Ammar na kwance a d'aki yana kallan number Jalal ya dade kafin ya daure da kirashi, sai dai duk yanda ya kira Jalal bai daga ba ya kalli agoggon bango na dakin karfe takwas na dare, yasan tabbas baiyi bacci yanzu ba.

Ya dade yana kiran Jalal sai dai duk da haka bai daga ba, kallan Zaid yai dake faman waya da Zaheeda yai dan bugemai kafada yace " tashi muje gun Jalal."

Zaid ya cema Zahi yana zuwa sannan ya kalli Ammar yace " ban gane ba."
Ammar yace Jalal yaki daukan waya inaji ba lafiya ba.

Nan yai waje tare da cewa " Zaid ka biyoni muje."

Sunje gida sukaita kwankwasawa, Jalal dakyar ya mik'e dan tun dafe ba abinda yaci ga zazzabi mai zafi dake damunsa......

Yana bude kofar ya fadi kasa.......







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com



No. 7? 6?




Ammar na tura kofar yaga Jalal a kwance a kasa cikin kid'ima shida Zaid sukai mota dashi, asibiti suka wuce dashi hankalin Ammar yayi dubu gun tashi gani yake kamar shine sanadiyar wannan ciwon, suna zuwa asibiti akai emergency dashi, Ammar ya tsaya a wajen dakin jiyake kamar yai ihu, Zaid ya kalleshi yace " kazo likita nasan ganinka."

Ammar jiki a sanyaye ya karasa ciki, likitan yace " kaine Guardian dinsa?"
" eh, wani abun ne?"

Likitan yace " me kukeyi har jikinsa yakai haka? Ga bigewar dayai abayansa baizo anyi treating dinsa ba sannan ga rashin cin abinci dan da alama rabonsa da abinci tun jiya da rana, ga damuwa mai karfi dake ransa, so kuke ku kasheshi ko me?."

Yai ajiyar zuciya sannan ya kalli Ammar wanda gaba daya abinduniya ya dameshi likitan ya daure ya dafashi, yace " ba komai zamu dubashi dakyai."

Ammar ya kurama Jalal ido, nan likitan yasa akaja gadon Jalal akai wani dakin dashi, Ammar ya kalli Zaid yace " ka fito da wayarka?"
Mikamai Ammar yai yana cewa ya kamata asanar da su Zahee ko?
Ammar bai amsa mai ba ya danna number Dad.
" Ammar kana ina ne kawu na nemanka?"
Ammar cikin sanyin murya yace " Dad ina asibiti."

A zabure Dad ya mike yace " kana asibiti kamar ya? Me a sameka? Ciwo kaji?"

Ammar ya girgiza kai kamar yana ganinshi yace " Dad kazo please, Jalal na kwace ba lafiya sosai."

Mamaki ne karara ya bayyana a fuskar Dad yace " inalilihi wa ina ilaihi raji'un, Ammar meya sami Jalal din?"

Ammar dake kallan Jalal yace " Dad nidai kazo please. "
Dad yai ajiyar zuciya yace bari na zo.
Jiyai Ammar yace " kazo kai kadai please Dad."
Dad ya amsa tare da fitowa.


Sunyi shiru, a inda Jalal ke kwance, Dad ya kalli Zaid yace " tsaya anan Ammar ina da magana dakai."

Sun fita waje can gun da ba mutane sosai, Dad ya kalli Ammar yace " meya sameshi haka? Duk ya canza?"

Hawaye ne suka dan

35 / 37