JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   21 / 37

60K to 63K   out of 109.4K words

ta koma.


Mamie tai ajiyar zuciya ta kalli Habib tace "Habibu?"

Habib ya kalleta yace " Mamie d'an Allah karku k'ara kokarin b'oye mana wani abu, d'an gaba d'aya na kasa fahimtar inda kuka dosa."


Mamie tai shiru can tace " Ni kaina banasan wannan b'oye-boyen, sai dai ina tsoron yanda zaku d'au al'amarin."

Ammar kam shi kansa ya kasa magana, kawai jinsu yake, Habib yace " Mamie babu wani yanda zamu d'auki al'amarin gaskiya kawai muke san ji."


Mamie ta runtse ido sannan tai gyaran murya.......





b&b&b&b&b&b&b&b&b&b&b&b&



Jalal kam har ya isa office ya zauna sai dai sam hankalinsa ya kasa nutauwa akan aikinsa mik'ewa yai da hanzari ya fito daga office d'in, asibitin da aka kwantar da Hajiya, inda suka had'u da Ammar ya tsaya jiya nan Jalal ya tsaya yana tunanin a ina zaiga Dad, cikin ikon Allah sai ga Dad da Abba sun fito daga wani d'aki da likita a kusa da su.

Da hanzari Jalal ya karasa gun, likita na tafiya Jalal yace " Dad ina kwana?"

Juyowa Dad da Abba sukai suka kalli Jalal, da mamaki Dad yace " Jalal kai kuma lafiya?"

Jalal ya karasa kusa dasu tare da kara gaidasu, Dad da Abba suka amsa Dad ya kara cewa " Jalal lafiya?"

Jalal ya d'ago ya kalli Dad yace " Dad kayi hakuri, sai dai hankalina ya kasa kwanciya, so nake naji mai mahaifina ya maka ka shak'e mai wuya? Naso in bar abin sai dai sam hankalina ya kasa kwanciya menene dalilin da zaisa kama mahaifina haka? Saboda inasan 'yarka ne ko me?"

Dad ya kalleshi da mamakin Kallamansa yace " Banace kaje ka tambayi mahaifinka ba?"

Jalal yace " haka ne haka kacemin sai dai a tunanina kai da ka mai hakan kai ya kamata in tambaya d'an zai iya yiwuwa shi baisan me ya maka ba."

Ran Abba ya fara b'aci yanzu ya gano wannan shine d'an gidan Amadun cikin b'acin rai yace " kai bakaji kunyar zuwa ka tsaremu ka fara mana tambayar banza ba? Ko rashin kunya ce?"


Jalal ya kalli Abba yad'anyi murmushi kad'an yace " ta ya za'ayi tambaya ta zama rashin kunya? Kamar yanda Mahaifina yake a guna haka Dad yake a gun Seemah, taya zan mai tambayar banza?"

Yai ajiyar zuciya sannan yace " sai dai duk inda d'a na gari yake dolene yaji haushi in har aka cima mahaifinsa mutunci ko da kuwa mahaifin nasa d'an fashi ne."


Dad ya kalleshi sam baya jin tsanar yaran zaiyi magana Abba yace " ka koma gun mahaifinka ga sako zan baka, kace masa yaci darajar Isma'il ne yaje gunsa ba ni bane da nine da wlh sai ya kwana a prison, ka kuma fad'ama mahaifinka sharrin dayama Kanina in ma laifin nasa ne ya rufe ko kuma akwai wani abu daya sashi yimai sharri, ko kuma so yake yaga kanina ya tozarta, to ka koma kasanar dashi matsayin Isma'il a wannan lokacin ka kuma sanar dashi a company d'in d'ansa kake aiki."


Abba na kainan ya ja hannun Dad suka shiga d'akin suka rufo sukabar Jalal a daskare a tsaye, sai da yai ta maimaita kalaman da Abba ya fad'a a ransa kafin cikin tsananin b'acin rai ya juya ya fita.







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com



_For you Maman Shaheed, I sincerely dedicated this page to you=?
?thanks alot, Allah ya raya mana su Shaheed amin_



No. 4? 5?



Mamie ta ja numfashi tace " Habib bazan iya baku labarin abinda ya faru ba saboda ni kaina ban san kanun labaren gaba d'aya ba sai dai zan iya sanar daku abu guda biyu zuwa uku.

Da farko dai kamar yanda ka fad'a tabbas Isma'il ba shine mahaifin Seemah ba.

Sannan Mahaifiyarta wato Fatima fyad'e aka mata sai dai mu kanmu bamusan waye ba sai dai bayan an mata fyad'en mai shagon da akai fyad'en yace Dad ne ya mata.
Wannan kalma d'aya daya furta yasa komai ya ruguje saboda alokacin saura kwana 2 a mata aure, alokacin wanda zai aureta ya fasa, Isma'il kuma 'yan gari suka tsaneshi har wuta aka sa a gidan Hajiya da kuma shagon da akai abin."

Habib yace " mene?"

Ammar kam hawaye ne kawai ke zuba daga idanunsa, me yake ji haka?
Mamie ta kallesu tace " abinda na sani kenan, bayan abin nan ya faru Fatima ta fiskanci wulakanci ta kowani b'angare har cikinta ya kawo haihuwa tana haihuwa tace ga garinku nan."

Habib ya mik'e tare da rik'e kansa, da sauri yai hanyar kofa ya bud'e yana bud'ewa yaji mutum ya biyo kofar, da sauri ya kalli kofar Seemah ya gani ta fad'i rim, jin karar fad'uwa yasa Ammar da mamie suka juya suma.

Habib da sauri ya tsugunna, Ammar ya taso da gudu yazo kusa da ita ya shiga jijigata yana k'iran sunanta sai dai inaaa Seemah kam ta suma.


Ammar ya kalli Habib idanunsa na hawaye yace " yaya kodai taji komai?" Kallan kallo sukai da Mamie, Mamie ta d'aure tace " akaita d'akin su Zahra."

Nan Ammar ya d'agata cak yai d'akinsu Zahra da ita, ya kwantar da ita, Ammar ya tsugunna a kusa da ita a rik'o hannunta idanunsa na zubar da kwalla, fita Habib yai daga d'akin d'an duk da yanajin tausayin Seemah a ransa amma yanajin haushin abinda akama mahaifinsa akan ta ta mahaifiyar.

Seemah kam ruwa Ammar ya shafa mata a fuska, hakan yasa ta bud'e idanunta tare da jan wani dogon numfashi, Ammar ya kalleta yace " Seemah!" a cikin wani irin yanayi mai ban tausayi ta kurawa Ammar ido, alokacin abubuwan da suka faru suka shiga dawo mata.

Da sauri ta fizge hannunta tana girgiza kai cikin kuka mai ban tausayi kawai Dad take k'ira, Ammar ganin haka yasa tausayinta yak'ara kamashi ya mik'e tare da fita falo, Dad ya k'ira.


Daga can b'angaren Dad ya d'aga tare da cewa " Ammar ya akai?"

Ammar yace " Dad kazo da matsala fa."

" Matsalar me fa?"
"Dad kazo gidan Abba d'an Seemah na wani hali."

Cikin rud'ewa Dad yace " meya sami Seemar? Waya b'ata mata rai?"

Shiru Ammar yai kafin can yace " Dad bansan me zance ba."

Jin karar alamar sa makulli yasa ya juya da sauri ya kalli d'akin, da sauri yace " Dad kazo yanzu da matsala."

Yana kainan ya kashe wayar tare da saurin karasawa kofar d'akin ya shiga jijigawa, jiyai ansa sakata.


Hannu bibiyu yasa ya shiga bubuga kofar yana k'iran sunan Seemah.

Mamie, Zahra da Zaid da sauri suka zo jin ana bubuga kofa, nan suma suka shiga k'iranta.

Ganin ba alamar bud'ewa yasa suka tsaya jugum jugum Mamie tace " gashi babu wani makullin."

Ammar kam haryanzu bai gaji da bubuga kofar ba, yana k'iran sunanta cikin wani irin murya.


Sun dade agun kafin Dad ya iso da sauri yana zuwa ya kallesu yace " menene?" Shiru sukai Mamie tace "nice na fad'i abinda bai kamata ba kuma ina tunanin ta ji."

Gaban Dad ne ya fad'i ya sa hannu zai buga kenan yaji muryar Habib yace " Zaid d'an Allah kaida Zahra kud'an bamu guri."

Zaid ya kalli Habib cikin b'acin rai gani yake kamar rainin hankali ne hakan, a zuciye yai waje.


Habib ya maida dubansa kan Dad yace " Dad da alama Seemah tasan komai a kanta, menene dalilin dayasa zaku b'oye wannan babban sirri ga kowa? Sannan taya za'ayi a maka sharri saboda mahaifiyarta amma ka rik'e yarinyar da ba kaine mahaifinta ba."


Dad ya kalli Habib cikin takaicin kalamansa, kafin yai magana yaji Ammar yace " lalai ya Habib, wato kai abinda ya dameka kenan? Yarinya tana cikin d'aki Allah ne kad'ai yasan meke faruwa da ita a ciki anma kai abinda kake tunani kenan?"


Dad ya kalli Ammar kallon jin dad'i ga kalamansa, Dad yai baya sannan ya taho da gudu ya big'e kofar, sai dai bata bud'e ba, haka sukai tayi shida Ammar har sukai sa'a kofar ta bud'e, da sauri suka shiga ciki sai dai ba kowa a d'akin, ga mamakinsu kuma karar zubar ruwa sukeji daga b'an d'aki.


Ammar ya karasa da sauri tare da bubuga kofar toilet d'in.

Seemah kam tana cikin bathroom ta tsugunna a cikin ta saki shaya, ga bata cire kayan jikinta ba, ga ruwan sanyi ta sakar ma kanta, hakan yasa ruwa duk ya jikata jakaf, sai dai ko damuwa batai da jikinta ba kawai kuka takeyi, gani take wannan itace hanyar da ya dace da ita, ita kad'aice hanyar dazatasa takasa gane yawan hawayen datake zubarwa.


Kuka sosai takeyi sai dai ruwan dake zuba jikinta yasa baza'a gane ba.


Dad ya matsa jikin kofar ya shiga k'iran sunanta, tana jin muryarsa ta mik'e jikinta na rawar sanyi, sai dai bata bud'e ba, Dad ya shiga lalashinta, can cikin lallashi yace " fito Seemah inhar kika fito zan fad'a miki duk abinda ya faru a baya, na miki wannan alk'awarin."


Jin wannan kalaman yasa ta bud'e kofar a hankali, kofar tana bud'uwa Dad da Ammar sukai saurin shiga ciki, kallanta Ammar yai hawaye na zubo mai, kanta ya kalla sannan ya kalli yanda jikinta ke d'iga da ruwa, dukansu har Habib sai da sukaji tausayinta ya kamasu sosai.


A hankali sukaji tace " Dad kafad'amin abinda naji ba gaskiya bane, ka fad'amin kaine mahaifina, ka fad'amin gaskiya d'an Allah."


Dad ya share hawayensa ya matso ya rungumeta yana hawaye sosai, yace " Seemah ki kwantar da hankalinki."

Kai ta girgiza tace " Na fahimta dagaske ba kaine mahaifina ba kenan, mahaifiyata karuwa ce, tsintata akai?"


Kallanta Habib yai cikin tausayi da alama bataji komai ba kenan, Dad ya d'ago tare da share nata hawaye yace ki canza kaya Seemah zan fad'amiki komai, amma ko kusa Fatima ba karuwa bace, ba kuma tsintarki nai ba."


Kallansa tai ta kasa yin komai, sai hawaye da suke tsere a idanunta, Mamie ta kwallama Zahra ido, tana zuwa tace " taimaka mata ta canza kaya."

Dad ya kalleta yace " ki shirya ki fito fallo zan sanar dake komai."








? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*




@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 4? 6?


Zahra ta taimaka mata tasaka kaya, hannunta ta kama suka fito falo.

A falo kuwa Dad na zaune a saman kujera yayi shiru zuciyarshi na cikin damuwa, mami na zaune daga can b'angaren itama, Habib kuma da Ammar suna zaune a kasa, Zahra ce ta fito rik'e da hannun Seemah ta zaunar da ita a kasa kusa da Dad, hannu Dad yasa ya shafi kanta.

Kamar ba Seemah ba sam ta canza ga lab'anta duk sun bushi gwanin tausayi, Ammar ma ya kalleta tausayinta na k'ara ratsa gab'obin jikinsa.

Dad ne ya d'aure yai gyaran murya.


*TUNA BAYA*




Malam Isma'il wato Dad kenan, ya kasance malamin makarantar boko ne, a garin Birnin/gwari dake kaduna, yana zaune a jikin gidan mahaifinsa ne saboda rashin hali, gashi anyi sa'a dama gidan kawo gida ne babba, kawo matansa 3 ne, sai dai duk Allah bai basu haihuwa ba sai akan mahaifiyarsu Isma'il.

Hajiya 'yaranta???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? biyu wato Dad da Abba (Abubakar) anyi sa'a Abba tun yana saurayi ya samu wani babban mutum d'an kasuwa a garinsu yake d'aukansa suna yawan kasuwancinsu tare, ganin kwazo dasan aiki irin na Abba yasa ya aura masa 'yar sa wato Mamie(Bilkisu) sannan ya d'aurashi akan harkokin business d'insa dake Abuja, tun daga nan ya koma can da zama.


Dad an masa auren zumunci da mahaifiyarsu Habib wato Samira, duk da baso yakeyi ba sai dai a lokacin bashida wacce yake so kuma zab'in iyayensa shine zab'insa, bayan auransu ne Kawo ya basu b'angare d'aya suka zauna a gidan.

A kwana a tashi har Samira ta haifi d'anta Habib, sannan ta sake haihuwar Junaid sai dai akwai ra ta a tsakaninsu, lokacin da Samira take da cikin Ammar ne ranar Isma'il ya dawo daga makaranta yaga wata bus tayi parking a mak'otansu, yarane 'yan mata su 4 suka fito daga motar, kana kallansu kasan fulanuwa ne aka kawo su irin aikin nan na aikatau.


Isma'il ya kauda kansa tare da wucewa gidansu, yaje daidai zai shiga yaji ance " Malam Isma'il?" Juyowa yai da fara'arsa saboda ya gane muryar, ya kalleshi yace " Amadu kaine yau a gidan namu?"

Wanda ya k'ira da Amadun yai murmushi tare da cewa" wucewa nazo yi shine naga kamar ana sauke 'yan aiki na d'auka kaine ka d'aukarma Samira." Yai maganar cikin zolaya.

Isma'il ya d'an kallesu caraf suka had'a ido da d'aya daga cikinsu, d'auke kai yai yace " lalai kai dai yakamata ka d'aukarma matarka."

Sun dad'e suna hirarsu har 'yan matan suka gama shiga da kayansu suma suka shiga, Isma'il ya kalli Amadu yace " ni dama shagon ka naje na amso ma Samira kayan shayi, naga kamar wannan cikin na wahalar da ita sosai bata iya cin abinci."

Amadu yace " Hmm nima haka nake fama da Hauwa'u inata so in tambayeka dama haka masu ciki suke shan wahala."

Isma'il ya maida jakarsa d'aya hannun yace " A'a wlh yanayi ne dai yake zuwa kaga Samira data haifi Habibu da Junaid ai duk batasha wahalar laulayin nan ba."

Amadu ya gyad'a kai yace " muje shagon in baka da har na kulli zance ganin Hauwa anma saboda kai zan koma."

Suna tafe suna hirarsu har suka isa Babban Shagon Amadu ya shiga ciki ya had'omai kayan shayi, Isma'il ya bashi rabin kud'in yace sauran sai karshen wata.

Haka Isma'il ya taho yan tafe ana gaidashi saboda ganin girmansa da mutane keyi, har ya isa gida.

Yanzun ma yazo shiga ya k'ara ganin 'yan matan sun fito sai dai ta d'azun nan tana matsar kwalla da alama kukan rabuwa sukeyi, wucewa yai ya shiga gida.


A kwance ya tadda Samira ta kasa komai, nan ya taimaka ya had'a mata shayi ta sha, da kanshi ya shiga gyara d'akin sannan ya taimaka mata ta kwanta a kan gado.


Ganin lokacin shiga makarantar su Habib da Junaid yayi ga kuma babban d'an Abba yasa Mamie ta ba Abba shawara akan akaisu England gun kanwarta, Abba yayi farincikin wannan shawarar ya k'ira kaninsa ya sanar dashi.

Ba Dad ba hatta matan gidan sun tayasu murna, su Habib sai murna sukeyi sukam, bayan sati biyu da maganar Dad dakanshi yakaisu Abuja suka wuce ta can.




Dad ya dawo daga Abuja a gajiye ya shiga gida anan ya tadda Samira ba lafiya su Hajiya da ragowar matan kawo na kanta, ya kallesu yace "Hajiya lafiya dai ko?" Hajiya tace " fita waje nak'uda ce."

Dad ya kalli Samira yaga yanda takeshan wahala yace " Kodai akaita asibiti?"

Hajiya tace " bakaji me nace ba?"

Jiki a sanyaye Dad ya fita ya zauna akan dakalin gidan, bai dad'e da zama ba sai gata ta dawo daga kai nik'a, a hankali cikin sanyin muryarta yaji tace " Ina wuni?"

D'agowa Dad yai ya kalleta ranar daya fara ganinta kaya daban daban ne a jikinta gashi tayi zanen baki duk a fuskarta yanzu kuwa ba wannan shirman a fuskarta sannan kayanta tsaf,ba shakka tanada kyau sosai.
Dad yace " ina gajiya."

Yana fad'ar haka ya kauda kai, matsowa tai kusa dashi tace " Malam menene? Naga kamar kana cikin damuwa."


Kalanta yai da mamaki, baisan sanda yai murmushi ba yace " Ta ya akai kika sani?"

Ta saki murmushi itama tace " kullum ina ganinka ai in na fito anma ba haka nake ganinka ba."


Dad yai murmushi yace "a ina kike ganina?"

Tai kasa dakai batace komai ba, yace " kije kikai aikenki kar a miki fad'a."


Ta d'ago ta kalleshi sannan tace to, wucewa tai ta shiga gida, ya bita da kallo haka kawai yaji damuwarsa ta ragu sosai, anma ya akai yarinya karama da bata wuce shekara 18 ba tagane yana cikin damuwa?

Yarinyar tana shiga gida ta kai markad'an sannan ta kalli matar gidan tace " Hajiya in d'an fita?"

Ta kalleta tace " Fatima ina zaki ke kuma? Naga yamma tayi."

Tace " yanzun nan zan dawo."

To sai kin dawo ta fad'a, da sauri Fatima ta juya ta fita, sai dai abin haushi tana zuwa taga ba kowa agun, waige waige ta fara yi sai dai bata ganshi ba, jitai anzo daidai kunenta ance " Fatima me kikeyi anan?"

Da sauri ta juya ta kalleshi, d'an gidan da take aiki ne ko ince d'an lele, da sauri ta matsa ya kalleta sannan ya kalli abokansa jitai sun kwashe da dariya, kifkif da ido tai tace " menene?"


D'an lelen wato Abdul yace " Abokaina kesan ganinki nace musu ankawo mana kyakyawar mai aiki shine nakeso su ganki ko zasu kyasa kamar yanda na kyasa."


Kallansa tai da mamakin kalamansa tace " mene?"

Dariya suka kara kwashe mata dashi, kana ganinsu kaga tantirai, Fatima kam ba abinda ta tsana irin Abdul ya shigo gida ya d'inga nanik'e mata kenan ita kuma batasan haka.

Cikin takaicin abin yasa tai

21 / 37