JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   16 / 37

45K to 48K   out of 109.4K words

bansan meyasa naji haushin ba d'an kin had'ani da wani, na sani sarai soyayyar jini dake tsakaninmu."

Ta furzo iska ta sa hannu a goshinta tace " oh God my bros sai yaushe zamu dauka ne?"

Dariya yai, ta kalleshi tace " ji kafar yaya kamar wanda bata aiki?" Yace ni d'in? Gwalo tamai ta ruga da gudu, binta yai da gudu shima, suna gudu suna dariya.


Jalal kam jin yanayin jikinsa ba daidai ga magrib takawo kai yasa ya wuce d'akinsu ya bud'e, abin haushi 'yan d'akin suna zaune sun kure radio, jiyai kansa na juyawa haushi yasa shi ya fita tare da zama a waje, sanyin dake ratsashi yasa ya tabbatar zazzab'i keneman rufeshi, waya ya d'aga abin haushi ya rasa wama zai k'ira? Sagir ne ya fad'omai hakan yasa yai dialing number, ringing 2 Sagir ya d'aga tare da cewa " Jalal kaga Chairman d'in?"

Yace " Eh amma sagir please kana ina?" Sagir yace ina gida ya akai zaka zo ne?

Jalal yai shiru, Sagir yace " please kazo tun yaushe nake rokanka? Har cewa nai ka dawo gidanmu mu d'inga zama a d'akina ka k'i bansan meyasa kake haka ba.

Jalal kam sai nishi yake jiyake kansa na wani irin sarawa, ka karar disco duk ta isheshi, a hankali ya firta Sagir please kazo ka d'auken a wajen d'akinmu kaina...........

Jiyai kansa yayi kinkirikim, hakan yasa ya sauke hannunsa, Sagir ya saki kiran sunanshi, jin shiru yasa ya zari makulli da sauri ya fita.

Da gudu ya zuro motarsa, yana zuwa yaga Jalal a waje ya jingina da jikin bishiya, da sauri ya karasa kusa dashi, yanasa hannu ajikinsa yaji kamar wuta, da sauri ya d'auke hannunsa yace " Jalal meke damunka haka? Ya za'ai kanajin zazzabi haka bazaka gun likita ba, Jalal ya d'ago ya d'an saki murmushi yace " Sagir ka iso? Nagode fa."

Sagir ya kalleshi cikin tausayi, yace Jalal tashi muje asibiti, kai ya girgiza mai yace " muje chemist kawai, ina sha magani zai tafi."

Sagir ya amince da shawararsa, nan ya nemi taimaka mai Jalal yai murmushi yace " me kad'auken Sagir? Zan iya tafiya da kaina, is not a big deal."

Sunje chemist nurse d'in ya kalli Jalal yace " ya kamata kaje asibiti gaskiya, jikinka na burning dayawa."

Jalal yace bani magani kawai, nan ya bashi magani yana mamakin taurin kai irin na Jalal, Sagir ya kallu nurse d'in yace " haka yake indai Jalal ne."


Sun fito suka shiga mota Jalal sai kallan wayarsa yakeyi, da alama k'ira yake jira ko kuma yakesan yi.

Sagir ya kalleshi yace " ka tabbatar ba matsala?"

Jalal ya d'aga kai, Sagir yace " amma maganar me kukai da Chairman d'an da alama ba maganar aiki bane."

Jalal yai d'an karamin tsaki yace " banasan ma tunawa amma Sagir wani irin mutum ne Chairman?"

Sagir yai murmushi yace " mutum ne mai mutuncin gaske sai dai yanda na ga alama yana tsananin san family d'insa, yana girmama mahaifinsa sannan yanasan kanwar nan tasa."

Jalal yad'an tab'e baki, Sagir yace "amma maganar me kukai?"

Jalal ya maida kanshi jikin window baice komai ba.




Dad yana zaune a wajen gidansa, motar Habib ta shigo, mamaki yasa ya kalli motar har Habib ya karaso ciki, yai parking, Dad ya kalleshi kallo d'aya zakamai kasan akwai abubuwa dayawa a zuciyarsa.


Yana karasowa ya gaida Dad, Dad ya amsa tare da cewa " na d'auka Ammar ne zaizo."

Habib yace " anan zai kwana yace, nasan anjima zaizo suna tare da Seemah ne."


Dad ya d'aga kai tare da murmushi yasani ai, da za'abar Ammar da a gidan Habib zai kwana.

Habib ne ya katseshi da cewa " Dad ina da tambaya?"

Kallansa yai yace tame fa?
Habib yace " Ummi mahaifiyar mu, ita ta haifi Seemah?"


Gaban Dad ne ya fad'i ya kalli Habib cikin tsananin mamaki, yawo ya had'iya sannan yai saurin kauda kai, yace " wani irin shirme kake fad'a? Bansha sanar daku sanda Maryam zata rasu ba tana haihuwar Seemah ta rasu? Ko so kake inyi ta tisa maganganu na?"

Habib ya dawo ta gaban Dad ya kalleshi, yace " a'a Dad akwai wani abun bayan abinda muka sani, akwai abinda kake b'oyewa bayanan."

Dad ya had'a rai kamar me, yace " karka kara tunanin ba mahaifiyarku d'aya da Seemah ba, inba sokake ranka ya b'aci ba."

Yana kai nan yai saurin yin haryar ciki, sai dayai nisa ya juyo yace ka gaidata in ka koma, sannan kace mata nayi missing d'inta.


Yana kai nan ya karasa ciki.
Daga yanda Habib yake kallan Dad zakasan bai aminta da kalaman da Dad ya fad'a ba, dole dole akwai wani abun da ake b'oyewa kod'an yanda dad yake saurin katse maganar in an fara.











? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 3? 3?




Jalal har sun d'anyi nisa sam haji hankalinsa ya kasa kwanciya juyowa yai ya kalli Sagir yace " Sagir please d'an taimaka ka ajiyeni anan, akwai inda nakesan zuwa."


Sagir ya girgiza kai yace " Kai Jalal, baka da lafiya na d'aukama zaka yadda na wuce dakai gidanmu, ina kuma zaka?"

Jalal yai ajiyar zuciya yace " gidan su Chairman akwai wacce nakesan gani."

Mamaki yasa Sagir yai baki sannan ya juyo cikin namaki yace " ban gane ba?"

Jalal ya juya kai yace " I don't know why but I feel that I must see her."

Sagir ya kalli Jalal yace " jalal me kake nufi da kalamanka? Wazaka gani? Ko ince wa kakesan gani?"


Jalal yai shiru, sagir yace badai Seemah ba ko? Jalal yace " Sagir bari na sauka nagode sosai."

Dasauri Sagir yace " a'a bandai san meke faruwa ba amma bazan iya barin ka katafi kai kad'ai ba."
Jalal ya kalleshi tare da cewa tnx alot.
Sun fara tafiya kad'an Seemah tak'irashi.

Murmushi ya saki tare da d'agawa, tace " My Deen!"

Jalal yai ajiyar zuciya tare da cewa " kina ina?" Tace gida d'azu muka dawo da ya Ammar.
Yace ganinan zuwa, yanajin karar datai tace " haba? Dagaske? Wayyo naji dad'i, ka kusa isowa?"


Murmushi yai yace " nad'auka zakice mezan zo yi?"

Tace "wa? Ni? Kaima kasan ko kullum zamu had'u bazan ce haka ba."
Yace " tsokanarki nakeyi bari inzo shaf shaf in ganki."

Sagir kam tuki yake amma gaba d'aya hankalinsa na kan Jalal meke faruwa? Soyayya suke ko me? Anma anya Seemah ce? Kodai wata ce a gidan?

Suna isa suka parking a gefen gidan, Jalal na mata flashing kafin wayar ta katse yaga ta fito, kamar irin tana waje tana jiranshi d'in ne.

Kodayake hakan ne d'an suna gama waya taji hankalinta ya kasa kwanciya, gyara fuskarta tai tad'an fesa turare ta sauko, a falo taga farida ta tambayeta Ammar tace ya fita yanzun nan inaji ya tafi, ta fito ta tsaya a waje.

Sagir ya fita daga motar ya kurama Seemah ido itakam dayake hankalinta baya kanshi bata na kula dashi ba, kawai juyawa tai tana neman Jalal, murmushi Jalal yai sannan ya fito daga motar tare da d'aga mata hannu, murmushi ta saki sannan ta karaso inda yake, Jalal ya kalleta ya saki murmushi itama murmushin tai tace " yau meya sameka? Nemana na ba zata haka?"

Ya kalleta yai ajiyar zuciya yace " meya sameni? Ahhh ni kaina ban sani ba, ko d'an d'azu bamu rabu ta dad'i bane? Kawai nakejin kamar ina tsananin san ganinki."


Murmushi tai sosai tasa hannu a kirjinta tace " wow naji dad'i sosai for this honour."

Tad'an rangwab'ar da kai tace " amma kamar numfashinka yana fita da sauri."

Murmushi yai yace " kawai maybe ko d'an kaina na ciwo ne."

Ai batasan sanda takai hannu goshinsa ba jin zaffin zazzab'i mai karfi yasa ta rik'ice, tace " My Deen ya haka? Meya sameka?."

Hannunta ya zare daga goshinsa yace " Don't worry ba wani abun bane, bari mu wuce."

Kallanshi tai idanunta sukai raurau kamar me shirin kuka tace " My Deen kaji jikinka kuwa? Yama za'ai kacemin karna damu?"
Kai ya kwantar a jikin kujera yace " karki damu in nasha magani komai zai dawo normal."

Sagir kam mutuwar tsaye yai, kawai kallansu yake, basu ankara ba kawai sukaji cikin muryar fad'a sosai ance " Seemah uban me kike anan?"

Da sauri ta juyo jin muryar Ya Habib, Sagir ma ya juya da sauri, Habib ya maka mata harara cikin zafin rai yace " ba magana nake miki ba?"

Jalal ya fito daga motar tare da kallan Habib yace " Chairman what do you mean by me takeyi anan?"

Habib ya had'e rai sosai wanda yasa cikin Seemah ya d'uri ruwa, ta kalli Jalal sannan ta kalli Habib tace " Yaya Deen bashu da lafiya please kamai a hankali."

Ran Habib ya kara tuzura yacw yace" kin wuce gida ko kuwa? Me yadaman da abinda ke damunshi?"

Zatai magana Jalal yace " Sorry Yaya zata shigo amma nan da minti 5."

Habib yace " what?"

Jalal yai murmushi yace " ban fahimci me kake nufi da metake yi anan ba bayan kafi kowa sanin meke tsakanin mu, bana tunanin kana zargin wani abun datake anan da ya wuce ganina."

Habib yace " mene?"

Jalal ya matso kusa dashi yai murmushi yace " yaya ka shiga ciki, yanzu kanwarka zata shigo sallama kawai zamuyi nima sauri nakeyi."



Habib sai hucci yakeyi ransa ya gama b'aci, lalai ma Jalal d'in nan, meya d'aukeshi?


Jalal ya juya kusa da Seemah ya rangwab'ar dakai yace " da alama dole muyi sallama yanzu, naga kamar yayanki jiranki yake."

Ta kalleshi hawaye suka zubo mata, kai ya girgiza mata yace " banasan kukan nan please. " ta kalli hannunsa tace " agoggonka?" Tai maganar cikin raunaniyar murya, da sauri yasa hannun a aljihu, idannunta suka sake zubar da kwalla, meya sami agoggon mu? Jalal ya kalleta yace " karki damu."


Share hawayen tai tana kallansa, yace ki shiga gida.



Habib ganin rainin hankalin yafara yawa kawai ya matso tare da fizgar hannun Seemah, tafiya suke da Habib anma kaba d'aya ta juya fuskarya kallan Jalal kawai take tana hawaye, shima shi kad'ai yasan me yakeji.







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 3? 4?



Ammar gidan Dad ya wuce kai tsaye, saboda ganin yanda Dad yai ta k'iransa, ya dade yana knocking kafin Dad yazo ya bud'e mai, yana ganin Dad yace " Dad saura kiris in b'ata ai gashi na iso a gajiye amma ka k'i bud'e min kofa."

Dad ta d'an hararesa sannan ya kamo kunensa da karfi ya jawo shi ciki, Ammar ya saki kara tare da cewa " Dad so kake d'an saurayin d'an naka ya rasa kunne daga nan ya rasa matar dazai aura?"

Dad yasa hanunnsa a hab'arsa ya d'an karkata yace " Wato tun safe daka iso sai yanzu zakazo ganin mahaifinka ko?"

Ammar ya dariya tare da cewa " Dad kasani kaima inda nake ai, balle na d'ade banganta ba, kasan me?"
Bai jira amsar Dad ba yacigaba" wlh yanzun ma gudowa nai ban bari munyi sallama ba ina tsoron kar inmuka kara had'uwa in kasa tahowa."

Dad ya girgiza kai yana wani murmushin farin ciki yace " Alhamdulila nasani ko yanzu na mutu Ammar bazaka bari swthrt d'ina ta wulakanta ba."


Dariya yai yace " yanzu dai ka huce kenan?"

Kara kama kumnensa Dad yai ya jashi cikin falon, Ammar ya rik'e kunnen yana cewa Dad yanzu in na kawo matar dazan aura taga anamin haka ai rainani zatai.

Dad ya sakeshi tare da cewa " ka kusa kawota ne? Na d'auka bakada wacce ta kwanta maka?"

Ya d'anyi kasa dakai yace " Dad anya lafiyata kalau kuwa? Narasa meke damuna, duk macen dana gani wlh sam bata birgeni, har addu'a nake Allah yasa in samu wacce zata dinga birgeni ko kwatan yanda Seemah take birgeni ne."


Dad ya kara sakin murmushi baice komai ba amma a zuciyarsa fal take da farinciki.

Ammar ya kalli Dad yace "Dad nasani abu kakesan fad'amin ko?"

Dad yai ajiyar zuciya yace " eh Ammar amma kuma ina tunanin, maganar nan dole sai Habib yana nam za'a yita, ka k'irashi kaji in zai saku damar zuwa to, inkuma sai gobema dai to duk d'aya ne."

Ammar yace ok bari na k'irashi, waya ya d'aga ya k'ira number Habib.


Habib kam bayan ya shiga da Seemah cikin gida, bai saketa ba sai da suka shiga d'akinsu ya saketa ta zauna a bakin gado tare da turo baki tace " Ya Habib wai meke damunka kwana biyu ne? Ko ka daina so nane?"

Had'e fuska yai yace " Seemah bawai san ki bane na daina sai dai bazan yarda kiyi abinda zai ja miki dana sani ba har karshen rayuwarki."

Cikin rashin fahimta ta kalleshi tace " San Jalal ne zai ja min dana sani? Ko kuwa me?"

Had'e fuska ya sakeyi yace " bani wayarki?"

Da sauri ta mik'e tsaye tace " ban fahimta ba?"

Habib yace " ki bani wayarki nace ko?" Seemah ta mik'e tare da turo baki gaba cikin shagwab'a tace " Ya Habib kasan dai bazan iya rabuwa da wayata ba ko?"

Matsoyai kusa da ita tare da fizge wayar yace " kanwata ajiye miki zanyi, sannan gobe kishirya mu fita yawo."


Yana kainan yai hanyar waje, zubewa tai a kasa tafara kukan shagwab'a tana bubuga kafa, tasani indai tafara wannan kukan to kome takeso sai an mata shi koda kuwa ba'a san yi mata, sai dai mamakinta yau Habib ko juyowa baiyi ba, duk da kasan zuciyarsa kukan na tab'ashi sosai sai dai bazai bari rayuwarta ta salwanta ba saboda yarinta ba.


Yana shiga d'aki ya kashe wayar ya bud'e drawer ya sata sanna ya zauna a bakin gado yana tunanin mezai wa Seemah dazai sa ta manta wani Jalal.

Wayar Ammar ce ta shigo ya d'aga wayar kamar bayaso, Ammar yace " Dad ne kesan magana da kai amma yace in akwai abinda kake ka bari......."

Katseshi yai da sauri da cewa ganinan zuwa yanzun nan, yana kainan ya katse wayar tare da yin waje da sauri, tunaninsa d'aya "Dad ya sauko zai sanar dashi komai."

Da sauri ya fito falo yai hanyar waje, Farida data fito daga kitchen rik'e da tire ta yanka kayan marmari aciki, ganin ya fito da sauri yasa ta shiga k'iransa sai dai inaaaa hankalinsa yayi waje sam bai kula da ita ba.

Ajiyar zuciya tai sannan ta koma kitchen d'in.



Habib da kanshi ya shiga mota ya fara driven ya fito yabi inda da Jalal ya tsaya da wani kallo ganin basanan yasashi yin tsaki.


?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%


Jalal kam bayan Seemah ta shiga gida Sagir ya shigo motar tare da kallansa yace " Jalal sam ban fahimce meke faruwa ba, dan Allah kamin bayani."


Kansa ya rik'e dayakeji yana sara mai ya juyo a hankali yace " muje Sagir zan fad'ama."

Nan Sagir ya tadda mota suka d'au hanya, sunyi tafiya mai nisa kafin Jalal yace " Sagir ina san Seemah." Juyowa Sagir yai ya kalleshi sannan ya maida kansa titi yace " Jalal amma kasan........


Wani irin murmushin kafin hali Jalal yai yace " I am not worthy ko?"

Sagir yace ba haka bane, ni a guna you are far much more worthy sai dai su a gunsu.........

Jalal ya kwantar da kansa yace " Nasani Sagir, su sunfisan 'yarsu ta auri wanda yake the same class da su."

Yai ajiyar zuciya sannan yace " Sai dai abinda ban fahimta ba shine, na d'auka in mace da namiji suna san junasu shikenan, na farko ita yarinyarnan tasan banida hali kuma a hakan ta aminta dani, na biyu yarinyar nan tana sona, so ni ina tunanin kamar abinda akeyi baya dacewa."


Sagir ya d'an kalli Jalal yace " haka ne Jalal abinda kafad'a haka yake sai dai yanzu rayuwar da ake ciki kenan."

Jalal ya furzar da wata iska sannan cikin kakkausar murya yace" Sagir kasan me? " sannan ya saki murmushi yace " a farko nayi tunanin kamar da wahala a barmu tare da Seemah sai dai d'azu zuciyata ta sanar dani wani abu, bazan rabu da Seemah ba duk tsanani da abinda zasu ce, sannan bazan yarda su wulakantani ba, wannan alkawari nama zuciyata."

Sagir ya kalleshi yace " Jalal please nidai shawarata d'aya shine ka hakura da yarinyar nan, ni yaushe ka fara soyayya haka dakake jin zaka jure komai na abinda za'a maka? "

Jalal ya maida kallansa jikin window yace " yanzu nafara shiyasa nakeji kamar nafi kowa kamuwa da soyayya."


Dariya sosai Sagir yai yace lalai Jalal.........



Nima nace Lalai.............







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 3? 5?




Habib yana isa gidan da sauri ya bud'e mota ya fita ko kofar bai rufe ba, yai cikin gidan da sauri, bayan ya shiga da Sallama suka amsa mai yasamu guri ya zauna, Ammar na kasa kusa da Dad yana daddana waya, Habib shima ya karasa bangaren dake kallan

16 / 37