JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   32 / 37

93K to 96K   out of 109.4K words

yace " kai kuma waye?"

Jalal ya dage ya wankamai mari tare da cewa " bakama san wanda kake nema ba?"wani irin ihu mutumin yai yace " ha ha ha! Yau ni aka mara? Ni Kumurci sarkin yaki, ba wanda ya isa yaja dani wanda kuwa yai gaggawar tabani to kuwa kabarinsa ne yake bukatar ziyararsa, ihuuuu sai ni Gatari bai sare namomin daji ihu ihuhu...."

Jalal ya kalli Zainab da ganinsa yasa ta mike da sauri tana hawayen tausayi, Jalal ya maida kansabkan mutumin yace " ba kumurci ba ko zaki ne kai baka isa kazo gidan iyayena ka dinga mana watsi da kaya ba."

Ya matso tare da nunashi da hannu yace " tun kafin in fasa ma baki ka koma ka sanarda wanda ya turo ka, in har yana san yamin wani abu to sai dai yazo da kansa bawai ya turo wasu tsolayen mutane kamar ka ba."

Yana kai nan ya fizgo hannunsa, yafara kokarin Jansa, Ammar ne ya matso ya kama dayan hannun nasa suka turashi waje suka rufe gidan.

Jalal ya kalli Ammar sukama juna murmushi, Zaid kam tafi ya fara yace " wow kaii Jalal ka burgeni dayawa."

Jalal ya girgiza kai sannan ya juya ya kalli Zainab, kusa dashi ta matso tace " yaya mai yasa ka fadi haka? In kuma ya turo wasu mutanen dayawa fa?"

Jalal ya kalleta duk ta canza ta rame, tausayinta ya kamashi, yace " ke kadai ce a gidan?"
Tace " nida kanwata ne to ta tafi islamiya ne."

Jalal yai ajiyar zuciya yace " shiga ciki zan gyara gun."

Kallansa tai tare da cewa " zan tayaka."

Jalal ya dago ya kalleta da sauri ta juya ta shiga ciki, da mamaki Zaid ya matso ya kalli Ammar yace " wacece?"
Ammar ya kalleshi yace " Zaid please keep quiet. "









?
*THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?
?=??
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 6? 8?


Kallan kayan yai gaba daya ma kayan sun tsufa kamar irin kayan bulan nan, yabi kwanukan Umma da kallo idanunsa ne suka ciciko, yanaji tun kayan auranta ne a gidan, sai yan kwanukan da aka dinga siya a hankali daga baya in an dan samu wani abun, Ammar ne ya matso ya dafa kafadar sa, jiki a sanyaye Jalal ya juya ya kalleshi, Ammar yace " Jalal me kake tunani?"

Jalal ya kalleshi sannan ya kalli kayan, yace " Ammar duba kagani, me nakeyi har kayan mahaifiyata suka kona haka? Kalli kwanukan da kayan sawarta?"
Hawaye ne suka gangaro ta ta gefen idansa yasa hannu ya goge, Ammar ya kalli kayan shima jiki a sanyaye, sannan yace " me kakeyi kamar ya? Jalal in baka da halin canza musu satowa zakayi ko me? Kayi iya naka kokarin suma sun sani Allah ma ya shaida, kudi kake dashi a lokacin ko me?"

Jalal ya runtse ido ganin kayan Abba ma duk sun kod'e yace " Amma Ammar ban nemi kudi bane a da sosai, ai da zan iya....."

Ammar ya jijiga mai kai, yace " Jalal don't make ur life hard, na sani duk dabansan yakai rayuwa ba da nasan da kanada hali bazakabar iyayenka haka ba, sai dai yanzu da ka samu aikin dayafi waccan nesa ba kusa ba sai kayi kokarin cika burin dake ranka."

Jalal yai shiru yana kallan Ammar, Ammar ya sakeshi tare da cewa " me kakeyi a tsaye? Munfara gyara gun ko?"

Murmushi ne ya bayyana a fuskar Jalal, nan ya sukunya suka fara kwashewa, Zaid dake waje yana waya ne yashigo da sauri yace " Jalal wasu mutane ne sunzo wai hakimi ya aiko ana kiranka."

Jalal yace " ni kuma? Dama akwai wani hakimi a nan garin?"
Zaid yace " to nidai gasu can a waje."
Ammar ya kalleshi yace " muje mu duba mana."

Zainab dake tsaye ta window tana kallansu, ta sulale ta zauna a jikin bango, hawaye suka zubo mata a fili tace " Allah na rokeka Allah kasa ba wani abun Ya Jalal yai ba."


Jalal na fita ya kallesu kayan fadawa ne a jikinsu, ya mika musu hannu suka gaisa, sukace " a cikin ku wanene Jalaludeen?an isar mana da sakon ya iso garin nan yanzu."
Jalal ya kallesu yace " nine, menene?"
Suka kalleshi dayan yace " Hakimi ne ke nemanka zakuje gurin sarkin birnin gwari tare."

Jalal yace " ban gane zamuje gun sarki tare ba a wani dalilin kenan?"
Suka hade rai dayan yace " kai dan gidan talakawa in an baka umarnin abinda zakace kawai shine to bawai ka dinga tambayar wanu abu daban ba."

Jalal zai yi magana Ammar ya katseshi yace " bakomai muje."
Jalal ya kalli Ammar fuska a hade, Ammar ya ja hannunsa gefe, bayan sun dan matsa ne ya kalli Jalal yace " Jalal calm down, muje sai muji me zasuce ai basu isadai su hukuntaka ba akan abinda bana gaskiya ba."

Jalal yai tsaki yace " ni rainin hankali ne banaso, me ya damen da wani sarki dazasuzo su sani a gaba?"
Yai shiru can yace " muje."
Ammar ya danyi murmushi.

Sunje gun hakkimi aka wuce dasu gidan sarki, Zaid ya kalli Ammar yace " amma dai ba hukuntamu za'ai bako?"
Ammar ya fizge hannunsa yace " kayi wani abun hukunci ne ko kuwa?"
Sunje shiga fadar hakkimi ya kalli Jalal yace " wadannan su tsaya a waje."

Ammar yace " ban gane ba?"
Jalal yamai murmushi yace " nima banasan mu shiga tare, at least in laifi nai I won't drag you down. "
Ammar zai sake magana, Jalal ya kalli Hakimin yace " muje."

Nan aka musu iso suka shiga, Sarki na zagaye da fadawa, sai dai bayan sun zauna yamusu umarni su fita,nan suka fita dukansu akabar Jalal da Sarki sai hakkimi.

Sarki ya kalli Jalal yace " kaine Jalal?"
"Nine Jalal." Yafada tare da kallansa.
Sarkin ya dan gyara nadin rawanin daya kusa rufemai baki ya kalli Jalal yace " an turo sunan ka daga sama ance kayi babban laifi na wulakanta Senate dakai shine aka bani umarnin hukuntaka ba tare da hukuma ta sani ba."

Jalal ya kalleshi yace " in kace Sama kana nufin....."
Kai sarki ya daga mai, Jalal yai wata dariya yace " lalai mutanen nan basa tsoron Allah." Ya kalli Sarkin yace " I don't think kanada shirin hukuntani."

Sarki ya kalleshi yace " meyasa kace haka?"
Jalal yai murmushi yace " in har hukuntani kakesan yi bana tunanin zaka aiko a kirani kuma har ka sanar dani ai aiko a hukuntani."

Hakimi ya kalleshi yace " kai gyara yanayin kalamanka ko ka manta a gaban Sarki kake?"
Sarki ya kalli Jalal yace " indeed u are smart, ba hukuntaka zan farayiba harsai naji abinda ya faru a kasata shekara Ashirin din daka fada a jarida ko gaskiya ne."

Jalal ya kalleshi cikin rashin tsoro da sadaukarwa yace " zan iya fadama amma sai in har na tabbatar zaka taimakeni gurin bada hukunci ga wanda yai lefi duk matsayinsa kuwa."


Sarki yai shiru can yace " idan kuma na kasa yin hukuncin fa? Ko kuma sai ka gama sanar dani incanza shawarata?"

Jalal ya kalleshi tare dayin ajiyar zuciya yace " Ka sa a kulleni kamar yanda aka fadama."

Sarki ya kalli Jalal da mamaki yace " kamar ya?"
Jalal yai murmushi yace " haka nake nufu kasa a kulleni sannan ka sanar da wanda ya ya bugoma wayar ina da evidence akan laifin da Senate Abdul ya aikata, sannan in har baizo gobe ba na ba Abokina zai aika kuto."

Sarki ya kalli Jalal cikin tsananin mamakin kalamansa yace " Jalal ban fahimceka ba."

Jalal yai murmushi yace " kai ma mutum ne mai matsayi sannan akwai mutane dayawa da suke samanka kamar Senate Abdul, bazan iya sanar dakai komai ba tukunna, in ka amince da olan dina to in kuma ba haka ba shikenan sai in tashi in tafi."

Shiru sarki yai na wasu 'yan dakiku yace " Don't trust me, dan bansan me kake shirin yi ba, kar inje daga baya inga bazan iya ba inyi betraying dinka, daga baya kazo kace ban fadama ba."

Jalal yai murmushi yace " I don't trust you, sai dai daga sanda kace fadawanka su fita nasan at least kai ba kamar su bane hakan na nuna bakasan aji maganar da zamuyi."

Sarki ya jinjina kai yace " okay na aminta da shawarar ka sai dai baka tsoron Abdul?"

Jalal yace " inada 'yan uwa a waje tare mukazo dasu ba kuma na tunanin zasu bari wani abu ya sameni."

Sarki yace " shikenan zan kulleka kamar yanda ka bukata, zan kuma yi abinda kace in har baifi karfina ba sai dai inaso ka fadamin kalma daya, da gaske Abdul ne yai fyaden dayaja matsaloli da dama a shekarun baya?"

Jalal ya dago yace " Zan iya rantsuwa akan shine yai wannan fyaden."

Sarki yace " Na aminta dakai, ka birgeni sosai na dade banga wanda ya zauna dani yai magana kanshi tsaye ba haka kamar kai, ba ka tsoron in an gama in ma hukunci?"

Jalal yai kasa dakai yace " In har na gama abinda nakeson yi ba wani abu bane in ka hukuntani."

Hakimi kam ya zama kurma dan ya kasa sa baki a wannan al'amarin shikam sam bai fahimci me suke nufi ba shiyasa ma yai shiru kawai.







? *THE SEEMA[truncated by WhatsApp]
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No.6? 9?



Jalal ya fito daga fadar mai martaba gunsu Ammar ya nufa, Ammar na ganinsa ya taho da sauri, hannunsa ya rik'e yace " Jalal menene?"
Jalal yai murmushi yace " ba wani abun, kawai dai I am gambling with my life ne, I don't trust him sannan banida solution a wannan lokacin daya wuce in yarda dashi."

Ammar yace " Jalal akan Abdul ne?"
Jalal ya jinjina kai sannan yace " turowa sukai amin hukuncin da bazan iya sake magana ba, sai dai bazan iya ba."
Ammar yai shiru, Jalal ya dafashi yace " karka damu Ammar dolene musa mutumin nan ya biya laifin daya aikata tun a duniya, inba haka ba banaji Seemah zatayi rayuwar farinciki har abada."

Ammar kallanshi kawai yake, Jalal yai murmushi kamanta alkawarin dana maka ne? Na cewar kafin bikinka sai na sa Abdul ya tsugunna agaban Seemah ya nemi yafiyar abinda yai."


Ammar yace " amma Jalal......."
Jalal ya katseshi da cewa " ba abinda zasu iyamin nasan bazaka bari wani abu ya sameni ba."
Ammar ya makamai hararra yace " in wani abun ya sameka banaji zan iya yafema kaina."
Jalal yai murmushi tare da cewa "bama abinda zai faru."

Waya Jalal ya fito a ita ya kira Umma, ringing 2 ta daga cikin farinciki tace " Jalal kai nake nema ai tun dazu ai, albishirinka."
Jalal yace " goro."
Tace " Jalal jiya da daddare anma Zahida aiki yanzu ta fara magana a hankali."

Jalal cikin tsananin farin ciki yace " Da gaske? Yanzu Zahii tana magana?"
Umma tai dariya tace " dazun nan likita yasata ta fara gwadawa."

Jalal ya shiga cewa " Alhamdulila."
Umma tai murmushi tace " Sai dai muna bukatar abubuwa na amfani ga mahaifinka bayannan."

Jalal yace " bakomai zan turo a kawo muku ."
" toh Jalal Allah yamaka albarka."
Yace Amin.

Yana kashe wayar ya kalli Ammar cikin tsananin farinciki yace " Ammar Zahii tafara magana."
Murmushi sosai Ammar yai yace " Naji dadi sosai, Allah ya kara mata lafiya."

Jalal yace Ameen sannan ya furzar da wata iska yace "Yarinyar nan tun tana karama akace za'a mata aiki mai tsananin cin kudi, duk yanda Abba yaso ya tara kudin amma inaaa, ko kwatan kwata bamu isa hadawa ba, haka muna ji muna gani take a kwance ga kudi suka cigaba da karuwa."

Yai ajiyar zuciya, Ammar yai murmushi yace " Allah ya riga ya kaddara sai a wannan lokacin zata samu lafiya, amma naji kana maganar sako ya za'ayi?"
Jalal yace " shine ai, tana wani babban asibiti ne a kaduna na Dr Bilal to yanzu ga abinda ya faru."

Ammar yace " bakomai ni sai inje da kaina."

Jalal ya kalleshi yace " anya kuwa? Da so nakeyi ka nemo mana manyan 'yan jarida wadanda kasan masu amana ne ko ta hanyar su Dad ne, akwai abinda nakesan a dauka bayan Abdul yazo, sannan inasan a inda za'a kulleni a sa camera yanda zata dinga daukan komai dazai faru tsakanina dashi inyazo."

Ammar ya jinjina kai yace " Amma Jalal daukan evidence ba tare da mutum ya sani ba, ba illegal bane?"

Jalal yai dariya yace " a'a a law ai in har wanda ya dauki rahotan, dashi a cikin video din yazama legal, ai abinda ba'aso shine daukan shaida a boye ba tare da sun sani ba su dukansu "

Ammar ya jinjina kai yace " hmmm na gane yanzu."
Jalal yai murmushi yace " Zaid fa?"
Ammar yai tsaki yace " ya fita daga ganin wata yarinya ta fito daga gidan ya bita."
Jalal ya girgiza kai yace " Kaiii Zaid sai a hankali."

Jalal yacigaba" Ammar dan Allah ka taimaka kahe gida ka fadama Zainab nace ta koma gidansu, in komai ya kammala zanzo in daukota."

Ammar yace " gwara kam, zamanta ita kadai shima matsala ne bamusan me wannam mutumin zai yi ba."

Nan suka zauna Jalal a dinga fadama Ammar plan din yanda abin zai kasance, Kwarai Ammar ya gamsu, fatansu dai daya kar Sarki yaci amanarsu.

Nan Jalal ya koma ciki, shiru Ammar yai yana tunani baima san Zaid yazo kusa dashi ba, Zaid ya tabashi yace " Ammar me kake tunani?"
Ammar ya kalli Zaid yace " Zaid me kake tunani akan sadaukar da komai da Jalal yai dan ganin yaba Seemah farinciki?"

Zaid yai dariya sosai yace " Tsananin san da yake mata ne."

Ammar yai shiru can yace " tare muka taso da Seemah shekararmu Ashirin tare, shiyasa nake jinta a kowace gaba ta jikina amma ina mamakin ya za'ayi Jalal daya hadu da Seemah kwata kwata na wata daya yake neman sadaukar da rayuwarsa saboda ita?"

Zaid ma yazauna tare da cewa " nikaina ina mamakin wannan soyayyar, sai dai ita soyayya nasan a ganin farko ma take shiga zuciya, sai dai irin wannan soyayya ce ban sani ba."

Ammar yai shiru, a ransa yanata maimaita Shekara 20, da wata 1.
Can ya daure yace " Zaid me kake gani a naka tunanin? Dani da Jalal waye yafisan Seemah?"

Zaid ya kwashe da dariya yace " ina zan sani? Inba zuciyarku aka tsaga na duba ba?sai dai nasan dukanku kuna santa kuma dole dayane zai aureta."
Yanakainan ya mike yai hanyar waje, Ammar yai shiru yana tunanin da ni kaina ban sani ba.




Jalal kam agabanshi Sarki ya kira Abdul bayan sun gaisa ne yace " Senate na kama yaran kamar yanda kuka ce amma me za'amai?"
Senate yace " ni kawai ayi yanda za'ayi yabar kasarnan ko a turashi niger."

Sarki ya kalli Jalal wanda wayar a handsfree take kuma suna recording sarki yace " Amma yaran nada taurin kai fa, dan da alama akwai shaidu daya tara akanka ina tsoron kar ya yad'asu a kafafen yad'a labarai ba tare da mun sani ba."

Gaban Abdul me ya fadi yace " Wannan wani irin jarababben yaro ne? Me yake so danine?"
Sarki ya kalli Jalal sannam yace " nidai bansani ba amma yace tabbas in gobe bakazo ba yasa abokinsa ya kai shaidun kuto da kuma gidan tv."

Abdul ya mike yace " what? Nashiga uku wannan wani irjn jarababe ne? Ko kudi zan bashi mai uban yawa?"
Sarki yace " nidai bansani ba sakonshi dai daya ne tabbas gobe kazo ko kuma kaga takarda."

Abdul yai shiru can ya kalli PA jikinsa sai rawa yake yace " naji zanzo gobe dan Allah karka barshi yai abinda bai kamata ba."

Sarki yace " to shikenan."
Nan sukai sallama Sarki ya kalli Jalal yace " yaro wai baka tsoro?"

Jalal yai shiru can yace " ko inajin tsoro ai tunda na fara ban isa ingudu ba ballema banaji, ni yanzu taimakon da zakamin shine kataimaka kasa 'yan sanda suzo gobe dan nasan inhar ba mutum mai matsayi irinku bame bazasu zo ba."

Sarki yace " insunzo kana tunanin akwai abinda zasu iya yima Senate guda?"
Jalal yai murmushi yace " nima babban burina shine karsuyi komai din kamar yanda suka saba."

Sarki yace " Jalal u are really smart ko ni bana fahimtar komai da kake nufi sai dai kar ka bari smartness dinka ya lalata ma rayuwa."

Jalal ya kurawa wani gun ido baice komai ba.


Shidai abu guda daya yasani kuma yasa a ransa, dolene Abdul yaba Seemah hakuri sannan yaba mahaifinsa da Dad hakurin abinda ya musu, sannan in anzo bikin Seemah ace mahaifinta ya hallarta, ya sani ko bata fadaba dole ne kasan zuciyarta zaiyi radadin wannan al'amarin, ko bata nuna ba zataso ko da mahaifinta mutumin banza ne ace a tarihin rayuwarta ace mahaifinta dai ya hallarci bikinta.




Hawaye ne yaji yana neman zubomai, da sauri ya mike tsaye, Sarki ya bishi da kallo, ba shakka irin wadannan mutanen kasarmu take nema, sai dai a wannan lokacin bayaji akwai namijin da zai sadaukar da rayuwarsa saboda hukunta wanda yafi karfin hukuma.









? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na

32 / 37