JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   8 / 37

21K to 24K   out of 109.4K words

ki d'inga fad'o abinda ba'a tambayeki ba?"
Cikin sanyi jiki Seemah ta kalli Habib sannan ta kalli Farida, mik'ewa tai taja su Ra'isa sukabar falon....

Tana kaisu d'aki ta koma d'akinsu ta kwanta sai dai ta kasa bacci sam, fuskar Jalal take hangowa, nan yana dariya, can yana murmushi, can kuma ya had'e rai......ajiyar zuciya tai ta saki murmushi.......

g&g&g&g&g&g&g&g&g&




Washe gari da safe Habib ya mata waya yace ta shirya zasuje gaida kakaninsu, murna sosai Seemah tai, Farida da kanta tazo ta duba had'ad'un kaya a cikin na Aisha ta zab'ar mata wata atamface da aka mata d'inki zamani riga da siket ne yau ce rana ta farko da ta tab'a saka kayan hausawa, sai dai kayan sun karb'eta sosai, Aisha ta zauna ta d'aura mata d'ankwalli, Seemah tayu kyau sosai ita kanta dad'i takeji inta kalli kanta, tarasa dalilin dayasa Jalal ya fad'o mata, tunaninta d'aya inya ganta mezaice?

Sun fito Habib sai wasa ta yakeyi suka shiga mota, nan suka fara tafiya zuwa Suleja inda iyayen Dad ke zaune.

Suna tafi suna hira har suka isa sunyi parking a daidai gate d'in wani karamin gida flat house mai kyau, Habib ya kalleta yace muje ko? Kallansa tai tace " Yaya why am I feeling so nervous? " hannunta ya rike yace " keda zakiga kakaninki mai zai saki jin haka?"

Murmushi tai sannan ta saki ajiyar zuciya tare da fitowa daga motar.

Habib na gaba tana binshi a baya, suna knocking akazo aka bud'e, wani almajiri ne ya gaidasu sannan Habib yatambayeshi ina hajiya? Yaron yace tana d'aki, nan sukai hanyar d'akin.

Sallama yai, wata datijiwace ta fito fuska a sake tana cewa maraba da babban jika na, dariya yai yace " ya akai kika gani muryata? Kafin ki fito?"
Fuskar nan cike da fara' a takalleshi tace " haba Mai gidan ya za'ai in kasa gane ka?" Idanunta ne suka kai kan Seemah kallanta takeyi taki d'auke ido, cikin rawar murya Seemah tace "ina kwana Hajiya?"
Batare data amsa ba ta kalli Habib tace ku shigo ciki, amma ban gane waccen d'in ba, nan suka shiga suna zama Mai gidanta ya shigo cikin murna yana cewa yau munada baki ashe? Lale da zuwan mai sunana.
Ciki ya shiga shima tare da zama kusa da Habib, Seemah kam jikinta rawa yakeyi ganin hajiya ta kafeta da ido, Habib ne ya rik'e hannunta yace " Hajiya Seemah ce, Auta sai yau Allah yai zuwanta."

Ba Hajiya ba hatta Alhaji gani yai sun had'e rai sunyi dif, a hankali Seemah tace " ina kwanan ku?" Sai dai abinda ya basu mamaki ba wanda ya amsa, Habib cike da mamaki yace " Hajiya gaisheku take fa? Baku gane ta bane?" Fuskar nan ba a sake ba, kawo yace " lafiya ya kika baro yan gidan?"
A hankali tace lafiya.

Sunyi shiru dukansu, Habib na mamakin wannan al'amari shikam bai fahimci wannan abun ba, itakam Seemah kasa tai kawai da kanta idanta kawai ya ciciko da hawaye.






? *NWA*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 1? 6?


Jalal na shiga office ya shiga duba takardun d'azu wayar Zainab ce ta shigo hakan yasa ya tuna kalaman Seemah na in da gaske ne yabari ta katse sai ya k'ira, yana kallan wayar harta katse sannan ya k'irata yana d'agawa tace " Yaya ya zakayi?"
Cike da mamaki yace name fa?
Tace " dazu su baffana sukabar gidan nan dashi da Abba wai sun yanke auran mu zasuyi."

Jalal cikin b'acin rai ya mik'e yace " me?"

Zainab hawaye ya zubo mata tana tsananin san Jalal hakan yasa batasan wani abinda zai b'atamai rai ciki kuwa harda auranta gani take in bayaso to fa zata iya hakura sai dai batajin zata auri wani.....

Jalal ne ya katseta da cewa nagode kanwata bari na k'ira Abban, kana katsewa yak'ira Abba tare da fita daga office d'in, Bayan sun gaisa Jalal yace " Abba yanzu Zainab ta........"

Cikin fishi Abba yace " kai ko kunya bakaji ba Jalal? Yarinyar nan tun tana shekara 12 mahaifinta ya baka ita sannan alokacin ta dawo gidanmu take taya mahaifiyarka kula da kanwarka da kuma aiyukan gida, har kawo iyanzu, sannan duk sanda na maka maganar auranta sai ka wayance da wani abun, gashi ta girma mahaifanta nasan suga tayi aure, shine ko kunya dan munyi zancen auranku zaka k'irani ka nemi yin korafi?"

Jikin Jalal yai sanyi ya sani sarai Zainab nada hankali gashi tun tana karama take musu wahala, sai dai shifa bai tab'a jin santa ba banda na 'yan uwantaka, cikin sanyin murya yace " Abba ba haka nake nufi ba."

Abba yace " karka kuskura ka b'atamin rai, kai ba wata kakeso ba yanzu shekarunka 28 to me kake jira? So kake sai ka tsufa ko me?"

Jalal yai shiru dakyar yad'aure yace " Abba yahakuri."

Abba yai shiru can yace " Jalal karka manta ba komai garemu ba, da abinda zamuci a rana ma wahala yake mana cikin wannan tsananin kai karatunka har ka samu aiki, kaine gatanmu damu da kanwarka banaso zuciya tad'inga saka maka abinda bazai amfane ka ba."

Jalal yace " nasani Abba."
Abba najin haka ya katse layin dan zuciyarsa tafara raunana, yana katsewa ya kalli Umma dake zaune idanunta taf da kwalla tace " Alhaji kad'inga mai a hankali kasan wahalhalun dayasha a da, ni nasani Jalal mai biyayya bazai bijire maka akan auren Zainab ba."

Abba ya kalleta shima cikin tausayi yace "Har yau bana manta wahalar da yaron nan yasha, ga makaranta secondary ga aikin karfi dayake yi na tara kud'in makarantar dazai shiga jami'a da ita, ga rashin abinda zamuyi amfani dashi a gida, haka zai fasa asusunshi ya bani kud'in,a ciki za'ai amfani da na gida dana magani Zaheeda," ajiyar zuciya yai yace " Ni kuwa ina zan manta hajiya? Kawai ina tsoro ne, kar d'an yaje birni wata 'yar masu kud'in ta nemi jan ra'ayinsa."

Umma ta share hawayen dake gudu a fuskarta tace " Ai *Jalaludeen* namijin duniya ne, tun yana karami yake kula damu hakan kuma banaji yanda yake da dakkakiyar zuciya akwai yarinyar da zata nemi juyamai tunani."

Shiru sukai a hankali idan Umma yakai kan Zaheeda dake kwance idanunta a rufe suke amma hawaye da zubowa ta gefen idanunta kura mata ido tai a ranta tace Allah yabaki Lafiya....nace Amin.



Jalal suna gama waya da Abba yatsaya agun yai shiru kara text ne ka tseshi daga tunanin da yake, wayar ya d'aga ya karanta sakon, " Ka gama?"

Ido ya runtse sai kuma wata zuciyar tace " menene na damuwa? San Seemah kake?" Da sauri yace a'a mezanyi da wannan karamar yarinyar da shagwab'a da yarinta suka mata yawa, iska ya furzar sannan ya koma office ya d'auko takardu yai kasa, sqi daya gama sannan ya mata text akan ta sauko su tafi.

Seemah kam takaice ya ishe ta kamar ita? Ace tayi hour 1 tana jiran d'a namiji ina....da sake, sai dai ya zatai tunda ta kori Bala, haka ta sauko fuska a d'aure, a kusa da motarta ta ganshi batace mai komai ba ta mik'amai key ya shiga itama ta zagaya tashiga ya ja mota suka fara tafiya, sunyi nisa ba wanda yama wani magana shi abinda ke damunshi daban itakuma takaicinta ko hakuri ma bai bata ba, cikin b'acin rai tace " Yanzu da gaske baka da niyyar bani hakuri?"

Kallanra yad'anyi sannan yamaida fuskarsa kan titi yace da nai me fa?

Takalleshi tace " mene? Ka barni a waje sama da hour 1 kace me? Dakai me?"

Jalal ya karasa gefen titi yai parking sannan ya juyo cikin b'acin ran abinda ake shirin yimasa yace " me? Na barki na hour 1? Ko kin manta aiki nake kika sani na fito? Ido ya rufe sannan ya ware hanayyensa ya nunata dasu yace " Seemah I am not in a good mood d'an haka kibini a hankali karki b'atamin rai."

Seemah yanda yake mata fad'a yasa ta tsorata tunowa tai d'azun nan fa suka gama hira da murmushi yanzu kuma menene hakan? Tad'auka zai bata hakuri komai ya wuce, cikin halin ko in kula tace " amma nikam kai wani irin mutum ne?"

Jalal ya juyo ya maka mata wani mugun kallo sannan ya fizgi motar a guje, ganin yanda yake gudu ta had'iyi yawo tace " amma ko me aka maka nina maka?mutum sai kace mai aljanu?"

Shidai Jalal bai kulata ba gudu kawai yake yana zuwa kofar gidansu kafin a bud'e yai kashe motar ya fito daga motar dakarfi ya rufo motar yai gaba, Seemah ta bishi da kallo baki bud'e tace " Ha ha Ha me kenan?"
Cikin takaici itama ta fito daga motar a kofa tacema Bala ya shigo da motar tai ciki.

Tana shiga tai d'aki ta fad'a gado batama kula Aisha na zaune ta baza tagumi ba, Aunty Farida ce ta shigo tace " Seemah kin dawo?" A hankali tace eh.

Farida ta karasa gun Aisha tace " wai ke wace irin soyayya kike yi hakan? Ba tunani ba kuma tsari?"
Aisha ta d'ago idanunta tace " Aunty yazanyi da san Muftahu?"

Farida tace " Shiyasa yake miki abinda yaga dama tunda ya kula ke kika damu dashi, yaushe rabon ya k'iraki? Sai ke kece uwar soyayya ko? To wlh indai haka zaki cigaba gaba ko a titi yaganki d'auke kai zaiyi yai kamar be ganki ba."

Seemah tayi shiru tana jinsu itama da alama ita take neman Jalal duk da ba soyayya suke ba amma ta kula shike jawo mata raini.


Farida tacigaba " kinsan me akecema *Hard to Get?*"
Kad'a kai tai alamar a'a
Ta cigaba bani wayarki nan ta mik'a mata Farida tace yasan duka layinki biyu? Tace a'a da Mtn kawai muke waya kinsan bana waya da Airtel sosai, Farida ta bud'e wayar tare da cire sim d'in Mtn d'in tace daga yau karki kuskura ki kara kiransa, duk san ki k'irashi dazakiji kar ki nemeshi, shikuma rashin ganin kiranki da farko zaiji dad'in kin kyaleshi amma ahankali abinzai fara damunsa, wannan shi ake kira Hard to get.

Seemah ma ta mik'e tana kallan Farida tace " kai Aunty kice shiyasa kika rikitamin yaya.

Dariya tai tace "Allah Aishan ce haushi take bani kuma wlh ki kuskura ki kirashi inji."tanakainan tafita.

Seemah ma tace nima dole inyi hakan.






? *NWA*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 1? 7?


Farida na fita itama ta kashe wayarta ta zuge jakarta tasata tare da kara kwanciya, Ammar takesan k'ira sai dai bazata kunna wayarta ba, daga bayama mik'ewa tai ta dawo falo ta zauna gun su Ra'is, ganin ansa wani indian series *JODHA AKBAR* a tv yasa tafara kallo, sai dai abin haushi tamaji gaba d'aya yawancin maganar dazasuyi sai sunce _Jalal_ jitake kamar da da ita suke haushi ya kamata ta canza tasha, Farida da Aisha dakw zaune suna kallo sukace Seemah lafiya? Aisha tace"Dramar fa tanada kyau sosai banaso ko kad'an a wuceni."

Haushi ya kama Seemah tace " meye wani Jalal in suna san abin ya birge mutane sai su nemo suna mai dad'i ba wannan ba."

Cike da mamaki farida tace " meye da sunan? Nikam ina san sunan har tunani nake in na k'ara haifar namiji a samai.......
Seemah ta mike tare da katseta tace " mene? Aunty badai wannan sunan ba gaskiya." tana kai nan ta juya tai ciki, Aisha ta bita da harara tace wlh Aunty wannan da kanwatace zaneta zan d'ingayi sam ta raina mutane.

Farida tace ya isa haka ni kaina abinda takeyi ba dad'insa nakeji ba amma akanta zan iyacemiki Habib zai iya rabuwa dani, d'an tun kafin muyi aure yakemin zancenta sannan sanda za'a kawo kud'i harda wani cewa zai nuna mata hotona ya tabbatar tana sona." Tai ajiyar zuciya tace " Bakisan abubuwan da akamin na takaici akanta ba daga baya dana gane san da suke mata ne yai yawa yasa nima nafara cusa kaina gunta kankice me tafara sona ko kunya Habib kecemin yaji dad'i da Seemah take sona nima nake santa d'an bazai iya zama da wacce batasan kanwar sa ba."

Ta kalli Aisha data saki baki tanajin zancen tab'e baki tai tace " tab lalai kice inyi a hankali mu rabu lafiya."
Farida tabi inda Seemah tai da kallo tace " Gaskiya kam."


Seemah kam d'aki ta shiga ta zauna a bakin gado tare da turo baki gaba masifar da Jalal yamata dazu, kwafa tai tace amma nima banza ce kuma dayamin masifar banajin nafad'amai abinda zai dameshi....



a&a&a&a&a&a&a&a&a&





Dad sam yakasa tsaye bare zaune abin duniya ya dameshi, ya zaiyi ya birne kar a kara tada maganar da akasha gwagwar maya a baya d'an binne ta? Tsoronshi d'aya kar lokacin da Seemah zatazo ace za'a aurar da ita magana ta tashi, ya zaiyi shikam, bayaso sam ran Seemah ya b'aci bare har taji wannan labarin da zai ruguza farin cikin rayuwarta, iska ya furzar sannan ya zauna a gefen gado tare da rik'e kansa, ya rasa ina zai fara jawo mafita.

Matarsa ce tashigo tare da zama kusa dashi hannu tasa da dafashi cikin salon jan hankali tace " Dad d'in Seemah me ke damunka ne? Wani ne ya b'ata maka rai?"

Hannunta ya ture daga jikinsa yace" dan Allah fita ina inasan nakasance ni kad'ai."
Kallansa tai tare da manna mai kiss na kissa a kunci, mik'ewa yai cikin b'acin rai yace in bazaki fita ba ni bari na bamiki d'akin.
Yana kai nan yai waje tabishi da harara tace " wlh badan kud'inka ba banga dalilin dazai zaunar dani kanamin abinda kaga dama ba.

Dad kam falo ya fito anan yaga Junaid da Ammar suna hira, zama yai tare da cewa Ammar kunyi waya da Seemah kuwa? Nak'ira wayarta d'azu a rufe, Ammar yai ajiyar zuciya yace " Dad nikaina bansan meke damun kanwata ba, a iya sanina bata tab'a kashe wayarta sai dai in ba charge sannan kullum mukai waya sai inji kamar tana cikin damuwa."

Junaid yasa dariya yace " kaii Ammar gaskiya ina tausayama wanda zai auri Seemah d'an na kula dakai da Dad bazaku barsu ba, kuna jin ranta ya b'aci zaku bazama zuwa gidan."

Dad ya harareshi yace " dama kai na kula baka san kanwarka sosai shiyasa baka damu da ita ba."

Junaid yace " wlh Dad ina bala'in san Seemah banaji in wani abu ya sameta zan iya rayuwa, ai Dad tun tana jaririya kariga ka cusa mana santa shiyasa kowa ke kishin gata da so da muke mata."


Ido Dad ya lumshe yace " yanzu misali in wani abu ya sameta na tsanani zaku gujeta?"

Da sauri Ammar yace " Haba Dad ai bana tunanin akwai abinda zai sameta muna raye in kuma Allah yatsara hakan zai faru kaima kasan soyayyar da muke mata bazatasa mu gujeta ba sai dai muzame mata makafa."

Junaid ma yace " Dad adaina maganar nan."

Nan suka d'auko hirar abin dariyar Seemah datana yarinya.....

Dad kam hankalinshi duk baya kan hirar sosai.




?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%





Jalal bayan sunyi Sallar Magrib ya fito waje d'an d'akin nasu ba dadin zama su hudu ne a d'aki kwaya d'aya tun safe in ya fito basan komawa yake ba saj bacci, zama yai a wajen kantin wani abokinsa wayarsa ce a hannunsa yanata juyata, abinda yama Seemah d'azu ne ya fad'omai yace " did I go too far?" Kansa ya sosa yace nasan halinta ba wani haushi zataji ba, kafin gobe zatamin text ko bata k'irani ba.
Mai shagon ne ya kalleshi yace " Jalal tunanin me kakeyi haka? Ko dai ka fad'a ne?"

"Ina na fad'a kuma?"
Dariya mai shagon yai yace " kai Jalal gaskiya kaima sai a slow, nifa ban tab'aji kace ga budurwarka ba, duk matan dake sanka, ka manta matar nan mai mota....."

" naji ya isheni karma ka tado min da wannan bakin cikin"

"Amma Jalal matar nan kamar fa zata haifeka,"

Kai Jalal ya girgiza yace " ni dai d'an Allah kabarni, yauwa dan Allah Nafi'u ga tambaya, nasan ka namamajo ne kai, inajin 'yan matanka sun kai 5, d'an Allah ya keke gane mace na sanka."


Dariya sosai Nafi'u yai yace " lalai Jalal abin naka babba ne amma kafin ka nemi sanin ana sanka ai kanka zaka fara tambaya, kanasan wace kake so........"

D'aga mai hannu yai tare da mik'ewa yace kai fa matsalata dakai kenan, ce maka nai ni nakesan ji ko me? da zaka faramin zancen banza nifa banaji akwai wani guri a zuciyata na soyayya, aiki na shine a gabana burina inga......."
Sai kuma yai shiru tare da cewa na tafi, yana kainan ya wuce ya fara tafiya.

Nafi'u ya bishi da kallo yace " Jalal kenan ko baka fad'aba na kula kafara fad'awa san wata, d'an tunda nake dakai yauce rana ta farko daka fara tambayata akan soyayya.





Jalal yana shiga d'akinsu yaga ba kowa, tunani yai bari ya d'auko takardun dasuke aiki a kai ya duba kafin su dawo su cikashi da magana, sai dai me? Kaf ya duba inda yake ajiya ya rasa cike da mamaki yake tambayar kansa to ina nasa? Nasan dai tabbas na fito dasu daga office har nabiya gun Assistant Director na nuna mai nakuma fito

8 / 37