JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   14 / 37

39K to 42K   out of 109.4K words

ya kalli Abba, shikansa yasan yauce rana ta farko daya tab'a musanta maganar mahaifin nasa yace " Abba dan Allah ka barni na auri wacce nake so, wlh yarinyar nan itama ba ruwanta."

Abba ya fusata yace " yau ni Jalal zaka kalla ido cikin ido kacemim wai in barka ka auri wacce kake so? Anya kuwa kaine Jalal?"


Kasa kawai Jalal yai da ido jiyake zuciyarsa na tafasa, Abba cikin takaici ya bar d'akin yai waje da sauri, Umma ta kalli Jalal cikin tausayi sai dai batasan me zatace ba itama ta fito, Zainab data fito daga d'akin Zahee jin hayaniya ta kalli Umma tace " Umma lafiya?" Umma takasa amsa mata kawai d'aki ta wuce.

Jalal kam jin zuciyarsa na zafi kawai yai saurin kiran Seemah, tana zaune kusa da Ammar tana ganin kiransa ta kalli Ammar tace "yaya saurayina ya kirani." Da mamaki ya kalleta sai dai kafin yai magana ta gudu d'aki, tana shiga ta d'aga tare da sakin ajiyar zuciya, jin shiru yasa tace Deen? Kanaji na?

Wani abu ya had'iya sannan yace " Meemah ya kika tashi?"

Ta kwanta akan gado tare da jan bargo tace " na tashi lafiya sai missing d'inka dake neman yimin yawa."

Bai san sanda ya saki murmushi ba yace " Na isa fa?"

Da sauri ta yaye bargon tace " da wuri haka? Hmm kunyi maganar? Sun yarda? Ya kukai?"

Dariya yasa sosai yace " duk ni kad'ai? Wanne akeso in amsa?"

Dasauri tace" ya kukai please? Fad'amin kaji?"


Murmushi yai yace bamuyi maganarba tukun yanzu na iso, tai ajiyar zuciya tace " ahhh jinai kamar zuciyata zata fito dan tsoro."

Ya kara sakin murmushi yace" da ina kusa dana ba ki......" da sauri ta sa hannu a goshinta tace " wayyo zafi" tai maganar cikin shagwab'a, dariya ya saki tace " Deen me na maka ka d'ana min?"


Dariya sosai ya d'ingayi yace " Ahhhh that's My Meemah you always make me laugh."


Tai murmushi tace " In mukai aure sau 10 zan saka dariya a rana."


Dariya ya sakeyi zai magana yaga Zainab a tsaye a bakin kofa idanunta sai zubar da hawaye sukeyi, kallanta yai sai yace ma Seemah" zan kiraki anjima." Tace okay miss u...... katse layin yai ya kalli Zainab, ya mik'e zai zo gunta da sauri ta juya da gudu tai waje , kai ya dafa yace " Ya Allah gani gareka."




Seemah kam kwanciya tai ta rungume pillow a kirjinta tace I miss you Deen Muah......sai kuma tai saurin liliba da bargo wai ita a dole kunya jitake in aka rabata da Jalal to lalai karshen rayuwarta yazo.


Mikewa tai ta sauka kasa ta zauna kusa da Ammar, kallanta yai yace " kingama waya da saurayin?"

Ta rufe idanta da hannu biyu sannan ta bud'e ido ta kama hannunsa tace " Ya Ammar ina tsananin san Deen, jinake in aka rabani dashi kamar........"

Had'a rai Ammar yai yace " bana ce karki kuskura kiyi irin wannan soyayyar ba?"

Ta kalleshi tace " ni kaina Yaya bansan ya akai nazama haka ba."

Ya mik'e tsaye yace da alama ma kinfi sanshi akaina, dariya ta saki tace kai yaya ka manta kai Special Oppa ne?
Ya harareta baice komai ba, ta taso ta rike hannunsa tace " yaya bansan meyasa Dad bayasan Jalal ba."

Da mamaki Ammar ya kalleta yace " ya ganshi ne?" Tace " a'a kawai daga fad'amai inada wanda nakeso naga ransa ya b'aci."


Ammar yai murmushi yace" that means ba saurayin naki bane baiso, bayasan kiso wani ne."


Tai shiru can tace kuma fa hakane to meyasa? Ya ce inazan sani? K'ila bayasan ki raba hankalinki ne, kina karatu ga soyayya.

Ta jinjina kai Ooooops Nagane maganar.








? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 2? 8?


Suna isa gida ta wuce da gudu d'akinsu tana zuwa ta fad'a gado ta cigaba da kukanta, Jalal kam sai kiranta yake a waya bata d'agaba, sam hankalinsa ya gaza kwanciya, Habib ma d'aki ya wuce ya zauna a bakin gado, ya rasa meke faruwa, da sauri ya d'au waya ya k'ira Sagir bayan sun gaisa ya tambayeshi ya labarin abokin ka kuwa? Sagir yace wa fa?
" Jalal mana, ni a wani gari yake ne?"

Sagir yai shiru yana mamakin tambayoyi sai can yace " a birnin gwari yake, yaron nan yallabai abin tausayi ne."

Habib yace " ayya iyayensa acan suke kenan?"


Sagir yace " eh nidai ban tab'a zuwa ba amma nasan talakawane sannan yana da kanwa da take kwance ba lafiya, yallabai yaron nan tare mukai makarantar jami'a ma tausaya mai kwarai, ga karatu ga sana'oi dayake saboda harkar makarantarsa dakuma iyayensa."


Habib yai ajiyar zuciya lalai Seemah batada hankali, amma a fili yace " na tausaya mai, iyayensa basa wani aiki kenan."

Sagir yace " gaskiya banaji, d'an inaji kamar mahaifinsa harkar ko gona yakeyi ne, bandai san takamaimai me yakeyi ba."


Habib yace " okay Allah ya rufa asiri, sai da safe." Yana kainan ya katse layin tareda rik'e kai, lalai Seemah yarinta na damunta, ai ko Dad bai hanaba shi bazai bari ta aure wani Jalal ba.

Seemah kam ganin kukan ya isheta yasa ta mik'e zaune tare da d'auko waya d'an ta fad'ama ya Ammar, ganin missed calls d'in Jalal ne yasa ta saki wani murmushi sannan ta mai text, tana gun ya Habib ne suna hira.

Jalal na ganin text d'in yai ajiyar zuciya tare da kwanciya.


?????????????????????????????????????????



Duk yanda Dad yaso hankalimsa ya kwanta yai bacci abin ya gaggara sai juyi yakeyi, tunaninsa d'aya yazaiyi ya warware wannan al'amarin ba tare da Seemah tasha wahala ba? D'an bazai yadda da auranta da wani bare ba, kar azo maganar aure abinda yake a b'oye ya fito fili.


*Washegari*


Da wuri Jalal ya shirya ya nufi tasha, yai sa'a yana zuwa ya samu motar dazata birnin/gwari, nan ya shiga suka d'au hanya........


Seemah kam ta tashi da ciwon kai sakamakon kukan data sha jiya, zama tai a kan gado, tana tunanin matakin daya kamata ta d'auka, Ammar da Junaid su kad'ai suka rage mata, da gudu Ra'isa ta shigo d'akin tace mata "Aunty kizo Uncle Ammar yazo." Cikin mamaki had'i da farinciki ta kalli Ra'isa, tace " Ra'isa dagaske kike? Ya Ammar d'inna ne yazo?" Kai ta d'aga mata, sam ta manta rigar bacci ce a jikinta da gudu ta diro daga kan gado tai falo tana zuwa ta kalli Ammar dake tsaye, ai da gudu ta fad'a kansa duk yanda yaso ya d'aure amma ina sai da suka fad'i kasa, Farida ta girgiza kai, wannan dab'iar fa? Seemah kam d'agowa tai ta kalli Ammar tace " Yaya sorry na yadda kai, amma yaya ya akai haka?"

Ammar yai murmushi sannan ya kalleta sai yanzu yaga kayan baccin dake jikinta, shara shara ne ana hango half-vest d'in data sa, yace " d'aga ni to, d'an naga alama neman karya wannan yayan naki kike."

Tai dariya tare da d'agashi tace " yaya tsaya d'an mintsineni a fuskata kad'an, so nake inji ko mafarki nake."

Dariya sosai tai sannan ya matso ya kama kumatunta da karfi sai datai kara, yace " ya? Yanzu kin gane?" Kara shigewa jikinsa tai sannan tace "yaya kamar kasan ina tsananin nemanka." Yai ajiyar zuciya tare da kallan gefe yace " yazanyi da kanwata? Ai in tana nemana dole jikina ya bani."

Ta zaro ido tace " dagaske kake yaya? Saboda haka kazo?"

Dariya yai har da zama akan kujera yace " lalai kanwata bata girma ba haryanzu zolayar ki nake."

Turo baki tai tare da harararsa sannan tace yaya bari nai sauri nai wanka zamuyi magana.

Ya d'aga kai, ta juya da sauri, Ammar ya bita da kallo fuskarsa d'auke da murmushi, wani sanyi ke ratsashi dayaga Seemah.



Jalal an isa gida lafiya a waje ya tadda Zainab tana wanke-wanke, kallanta yai cike da tausayi tana ganinsa ta mik'e da sauri tare da gyara hijab d'in dake jikinta, yana mamaki shidai ko a d'akinta take tanaji da hijab take zama, bai tab'a ganinta ba hijab ba, katseshi tai cikin murna tace " yaya? Kaine? Sannu da zuwa."

Murmushi yai yace " aiki kike?" Tai kasa da kai ya kalleta yace " sannu zainab, ana sanyi kina wanke-wanke a wajen nan?"

Ta kasa kawai dakai tana wasa da 'yan yatsun hannunta, umma ce ta fito tace " kaima dai ka mata fad'a Jalal, duk yanda nai da yarinyarnan tabarni nai amma bata yarda sam hanani komai takeyi."


Tausayinta ya kara kamashi, jiyai tace " Umma ina zan bari kiyi aiki? Bayan kema hutu kike bukata? Kullum kina gun Zaheeda kina kula da ita."


Umma tai dariya tace Jalal kajita ko? Jalal kam kallanta yake cike da tausayi, Zainab ta d'ago ta kalleshi ganin yana kallanta yasa tai saurin yin kasa da ido, tace " yaya ka shiga ciki sanyi akeyi." Kallanta yai ko rigar sanyi babu a jikinta sai hijab amma wai shida yake sanye da jacket tama cemai ana sanyi, matsowa yai kusa da ita yazare Jacket d'in ya mik'e mata yace " kisa" ta amsa tana kallansa, Umma ta saki murmushin farin ciki ya sani ko Jalal baisan Zainab bazai wulakantata ba, Jala kam yama gani ta amsa ya matsu kusa da Umma yace Umma mushiga, nan sukai ciki.


Kusa da Zaheeda ya zauna idannunsa sunyi jaa, itama idanunta na kansa, sai dai kana ganin alamun fuskarta kasan tana farincikin ganinsa, murmushi ya k'akaro tare da shafa kanta yace My Zahee kinyi missing d'ina ko? Idannu ta lumshe alamar eh, ya had'iye wani abu sannan ya juyo ya kalli Umma yace Umma ina kwana? Tace lafiya lau Jalaludeen, ya aikin?

Yace Alhamdulila, Umma ya jikin Zahee? Takalli Zaheeda tace gatannan dai jiya iyau, sai dai kwanan nan jikin baya wannan tashin.

Jalal ya kalle Zahee yace " Abba fa?"

Tace " yafita wai akwai wani mutumi dake neman masu mai lambu, shine sukaje shida Sani, Jalal ya gyad'a kai, yace " amma Umma kema ya kamata kid'inga hanashi wannan sana'ar da ba amfani take mai ba."


Umma tai shiru tace " kaima kasani bayasan zama guri d'ayan nan."

Jalal ya runtse ido yace " amma Umma kima ganin yanda kafarsa d'aya take? A dalilin me zai d'inga zuwa yanama wasu aiki bayan shi kanshi yana neman hutu? Sannan inya gama kwata kwata nawa suke bashi? Ya wuce dubu 1 ko 2?"


Umma tai shiru, Jalal yacigaba " Umma please ki taimaken ki hana Abba wannan yawon, in kuma lalai sai yayi sana'a ne, to ina ganin in na d'au albashi wannan watan mufara gina karamin shago a wajen gida inyaso in muka gama sai muji me yakesan ya zuba."


Umma ta kalleshi tace ka manta yace " bayasan kasuwanci?"

Cikin zafin rai da takaici Jalal yace " Umma wai menene dalilin dazaisa yak'i kasuwanci? Bayan muna halin rashi ne?"


Umma ya share kwallar data zubo mata tace " Jalal wani babban al'amari ya faru a shagon mahaifinka ne a shekaru masu yawa da suka wuce, 'yan garin nan suka sama shagon wuta, basu san me ya faruba bakuma su duba halin da maishagon yake ciki na bakin cikin abinda ya faru a shagonsa ba."


Jalal ya mik'e cikin b'acin rai yace" nasan wannan Umma, duk dabansan abinda ya faruba amma nasan wannan nasan kuma akan abunda ya farune kafarsa d'aya ta zama haka, sai dai tunda kinki sanar dani abinda ya faru bansan me zance ba"

Yai ajiyar zuciya yace" amma kome ya faru bakya ganin shekaru masu yawa sun wuce da za'a ajiye wannan al'amari?"


Umma ta kara share hawayenta tace " Jalal d'an Allah karkama mahaifinka zancen kasuwanci, ba'abinda ya tsana irinshi."


Jalal ya kalli Zaheeda da yaga hawaye na zuba ta gefen idanunta, sama ya kalla d'an boye hawayesa, ya tsugunna kusa da ita ya saki dariya" ha ha ha Zahee karki damu hira kawai muke da Umma ba wani abu bane kinji."

Umma ta kalleshi cikin tsananin tausayi, ganin yanda yake neman faranta ran kanwarsa yasa taji zaman yana neman ya gagareta, da sauri ta mik'e tai waje, Zainab da ta taho kawomai kunu da kosai, duk taji abinda sukai, ita kanta hawaye take sosai, ajiye kwanon tai ganin Umma ta fito, har zata bita taga kamar be dace ba, nata hawayen ta goge sannan ta shiga d'akin da fara'a, tace " Yaya kanaba Zahee labari ne?"

Ya juyo ya kalleta yace " sannu zainab. " ta zauna a d'aya gefen Zahee itama tana bata labari.




?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%

Seemah da sauri ta wanka ta zura kaya ta fito, akan dinning ta sami Ammar da ya Habib, taje kusa da Ammar ta zauna ta gaida Habib, Habib yace " baxan amsa ba tunda dai baki zauna kusa dani ba."

Ta kalli Ammar tace " Sorry Ya Habib naga tsohuwar zuma, kasan tafi zaki."

Ammar yasa dariya yace " Yaya sai dai kai hakuri kasan ni special ne."

Habib ya girgiza kai yace " lalai Seemah ni zaki ma haka ko? Shikenan nima zan rama."

Ta kalli Ammar tace " ya Ammar I miss you alot."

Ya shafa gefen fuskarta yace " ban yarda ba, bayan banga kin rame ba sai kiba danaga kinyi?"

Zaro ido tai ta kalli Habib tace " Ya Habib da gaske ban rame ba?"

Habib ya harareta yace " sai kiba dakikai kamar me...."

Ahhhhh ya zanyi? Ta mik'e ta shiga zirya tace ya Ammar ya zanyi? Kasan fa banasan nai k'iba? Noo bazanyi breakfast ba, ta kalli farida datai sakwalo tana kallanta, taje ta rik'e hannunta tace " Aunty azumi zan fara."


Habib da Ammar kam banda dariya ba abinda sukeyi.........



? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 3? 0?



Dad zaune kusa da Abba dayazo ganin gida, Dad ya kalli Abba yace "Yaya haryanzu banji kace komai ba?"

Abba ya kalleshi fuska a had'e yace " Meyasa baka fahimta ne Isma'il? Taya zaka had'a jininka dana....."

Dad ya katseshi dacewa" Haba Yaya meyasa bakwa fahimta ne, Seemah 'yatace akoda yaushe, duk da a baya nima nayi tunanin kaita gidan marayu, amma daga baya na gane haka Allah ya kaddaramin, kuma inaji a jikina Seemah Amanace Allah yabani."


Abba ya kalleshi cike da tausayi yace " Nafahimci abinda kake nufi amma kai kana tunani su Hajiya zasu yadda da wannan fatawar taka?"

Dad yace " nasani yaya shiyasa nake rokon ka daka taimakamin, Yaya banaso wani abu da zai d'aga ha kalin Seemah."

Cikin takaicin hali irin na kaninsa Abba ya m'ike yace " Seemah Seemah Seemah!!! Haba nagaji da yanda ka damu da yarinyar, anya ma kana kaunar 'ya'yanka kamar yanda kake santa? Ko dai akwai wani abu dabaka sanar dani ba? Bana tunanin akwai mutum irinka a duniya, mahaifiyar yarinyar nan tajaza maka masifar da bazaka tab'a iya wanketa ba amma kai kamar mara tunani."


Hawaye ne suka taru a idan Dad ya mik'e shima ya kalli yayan nasa yace " Yaya alokacin kunki fuskarta ne amma ni kad'ai nasan halin datake ciki."

Cikin takaici Abba yace " Nikarka karamin zancen wata mata can da banasan in tunama nasan ta, sannan ni haryau ban yarda ma........"


Cikin zafin Rai Dad yace " haba yaya! D'an Allah karka kara furtamin kalaman nan."

Abba a zuciye ya bar gidan, Dad ya zube a kasa kawaa yasa kuka kamar karamin yaro, gyambun dake birne a zuciyar sa ya famu, kuka yake sosai bai masan sanda Habib ya shigoba, dayake Abba a bud'e yabar kofar, Habib ya tsaya a bakin kofar yana kallan mahaifinsa jiyai kawai jikinsa ya d'ebi rawa baisan sanda shima hawaye suka fara zubomai ba, kallan mahaifinsa yake cikin wani yanayi mai wahalar fahimta, meyasamu dad? Me akamai? D'an da alama kukan daga zuciya yake fitowa bawai ciwo yaji ba ko rashin lafiya bane.

Habib a hankali ya karaso kusa da Dad ya rungumeshi ta baya baice komai ba sai kuka shima da yakeyi, A hankali Dad ya fara kokarin saita kansa, ya juyo da fuskarsa kan Habib, baice mai komai ba Habib ya rungumeshi yace " Dad menene yakecin zuciyarka haka? Menene ke damunka da har zakai irin wannan kukan? Dad ni babban d'ankane kuma Abokinka ko kamanta haka kake cemin in ina cikin damuwa?"



Dad ya kalleshi kawai girgiza mai kai yake, Habib ya kakaro wani murmushi yace shikenan Dad na d'auka munyi shakuwar dazamu d'inga raba matsalolinmu.

Mik'ewa yai ya fita Dad ya bishi da kallo cikin tausayi sai dai yana tsoron furtama Habib maganar.




Jalal kam ganin zaman da yake ya isheshi yasa ya mik'e da sauri yai waje shima, ya fara neman Zainab, yana tunanin ita kad'ai ta rage masa a mafita yasani inya sanar da ita abinda ke ransa zata goyamai baya.


Sai dai duk yanda yaso nemanta bai sameta ba, haka ya gaji ya koma gida, yana shiga ya ganta a tsakar gida tana shara, cike da mamaki ya karasa gunta yace " Zainab inasan magana dake."

Jiyai Umma tace " bazata ba, Jalal yaushe ka zama haka? Nasani sarai abinda kake tunani."


Jalal yace "

14 / 37