JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   29 / 37

84K to 87K   out of 109.4K words

karasa ya zauna yana kallanta, ana gamawa ta mik'e da sauri ta karasa kusa dashi, Ammar ya kalleta cikin tsananin bege yasa hannu a hab'arda yace " Ahhh anya kuwa Seemah tace? Ba sai na shiga bincike ba?"
Ta ballamai harara tace " Yaya nifa nayi fishi dakai."

Yad'an saukar da kai kasa yace " Shikenan tunda bakiso ganina ba bari na juya na koma."
Ya fad'a tard da fara tafiya, da sauri ta karasa kusa dashi ta rike rigarsa ta baya tare da cewa " Wasa fa nakeyi yaya."
Ya juyo tare da sakin sansanyan murmushi yace " nima wasa nake, ya za'ayi in tafi in bar amarya ta?"
Ta d'an sadda kai kasa itakam ta kasa sabawa in yai irin wannan zancen bata iya mayar mai.



Zaid ne ya karaso kusa dasu yace " hmmm yau fa ba kanta Ammar yaga Seemah."

Seemah ta kalleshi tace " Yaya Zaid?"
Zaid ya girgiza kai yana nuna Ammar yace " wannan mutumin? in kinsan abinda yakemin kullum da dadd......"

Da sauri Ammar ya matso ya toshemai baki yace " To shigaban san magana banaji an tambayeka ko?"
Seemah ta kallesu tai dariya nan su Ya Habib suka matso aka cigaba da hira.


Jalal kam yana isa da kusan hour 1 sannan suka tashi zuwa kasar mu, a kasar Abuja suka sauka, ganin dare yayi yafara tunanin ko zuwa hotel.

Mota yahau ya wuce hotel yana shiga d'aki ya cire coat d'in jikinsa ya fad'a toilet, bayan ya fito ne ya kunna wayarsa sannan ya kira wata number, ringing biyu aka d'aga, Jalal yai sallama, da sauri mutumin ya amsa tare da cewa " Haba Malam Jalal tun wancan satin nake jiran kiranka amma shiru banji ka kira ba."


Jalal ya mik'e tare da zuge labulan window ya kalli waje tare da cewa " Director na amince da aiki a gidan tv d'inku sai dai inada sharad'i guda d'aya."
Ya saki wata dariya sannan yace " nagode sosai journalists Jalal tun kana Germany yanda naga kanada kwazo da kuma kwarewa yasa nake fatan yin aiki dakai, naji dadi."

Jalal ya kalli waje yace " bakaji conditions d'in nawa ba ai."
Ya kara sa dariya yace " Ai duk abinda zaka fad'a nasan bazai wuce kanasan adinga biyanka dayawa ba ko kuma akwai program dakake san yi."

Jalal yai wani murmusho yace " Indeed you are smart sai dai ba haka bane burina abu guda d'aya nakesan in fara gabatarwa kafin muxo kan wannan maganar."

Tattara hankalinsa yai gun Jalal yace " ina jinka."
Jalal yace " inaso ka gayyato mana Senate Abdullahi wanda yake kokari takarar zama shigaban kasa muyi hira dashi a program d'in dakasan yafi komai bunkasa ta tashe a gun mutane."

Shiru yai yace " Menene dalili......"
Jalal ya katseshi da cewa " karka damu ba abinda zai faru, kawai dai nasanshi ne ina kuma san inga na fara aiki dashi kafin in fara komai."


Ya jinjina kai yace " ba damuwa zan aika da takarda gayyata, inasa ran kuma zai hallarta dan mutum me shi mai san a sanshi."

Jalal ya daga gira yace " nasan da haka shiyasa banaji ta gunsa."

Suna gama waya Jalal ya kurama waje ido sannan yai murmushi yace " Malam Abdul sai mun had'u."






Sagir ya kira yace ya kawo masa abinda yace ta tattaromai yana hotel.








? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 6? 2?




Yana gama waya da Zaid ya kira Abbansa, bayan sun gaisa ne yace " Abba kun isa lafiya?"
Abba ya kalli Zahida dake kwance, yace " gamunan tun azahar muka iso, gaskiya asibitin nada kyau ga kulawa."

Jalal yai murmushi yace " Mai suka ce gama da ciwon ta?"
Abba yai shiru can yace " Sunce ba wani abu bane serious kawai dai tun tana karama ya dace mukaita asibiti sai dai barin kashinta da mukai har yai kwari haka shine zai sa a sha wahala kafin ta mik'e."

Jalal ya jinjina kai sannan yace " Dad ya dawo yau."
Gaban Abba ne ya fad'i yai shiru baice komai ba, Jalal ya cigaba " Bai tsaya taron kammala karatu Seemah ba naga yataho." yai ajiyar zuciya sannan yace " tunda ka duba komai na asibitin sannan Umma nacan ka dawo muje ka roki gafarar Dad hakan zaisa Allah ya dubi zuciyarmu ya ba Zaheeda lafiya."

Abba ya runtse ido sannan yace " gaskiya ne Jalal na auna naga gudin nan danakeyi ya isa haka, abinda yafi dacewa dani shine in nemi gafarar Isma'il ita kad'ai ce zatasa hankalina ya kwanta."

Jalal ya d'an murmusa kad'an yace " yaushe zaka taho nan d'in?"
Abba yace " gobe ma, mai zan jira?"
Jalal ya jinjina kai yace " inkazo gobe sai muje jibi."
" Allah yakaimu, amma ka kira Zainab?"
Jalal yad'an tsuke fuska kad'an yace " Zan kirata."
Abba yace " Jalal ba dan ni ba saboda darajar aure agun ma'aiki zaka duba, nasani sarai Zainab bata gabanka ba kuma santa kake ba, sai dai kada ka manta d'aura muku aure akai, hakkinta dake kanka yazama dole ka saukesu in dai kana neman rahamar Allah. "

Jalal yai shiru, can yace " Zan kirata Abba."
Nan sukai sallama.


A bakin gado ya zauna ya kurama sunan ta ido dake kan wayarsa, Zainab yasa ya dade yana kallan sunan kafin ya daure ya kira.

Zainab kam ita kad'ai aka bari a gidan hakan yasa ta d'auko kanwarta, suna zaune suna 'yar hira sama sama ita wani sa'in mantawa ma take tanada wani aure, ganin kiran Jalal yasa taji gabanta ya fad'i rabonta dashi har ta manta, mik'ewa tai ta shiga d'aki da sauri, ta zauna a bakin gado sannan ta d'aga wayar.

A hankali tai sallama, Jalal ya amsa tare da cewa ya gidan? Tace lafiya kalau, shiru sukai dan basusan me zasu cema juna ba, can Zainab ta daure tace " Umma tace yau zaka dawo kasar nan ko?"
Jalal yace "nama dawo ina Abuja ne."

Zuciyarta taji ba dad'i amma ta daure tace " Yaushe zaka dawo nan kenan?"
" Ina da aiyukan yi anan zan d'au lokaci kafin in dawo."

Ta jinjina kai a ranta tace " Lokaci? Shekara 2 tayi kad'an kenan?"

Jalal ya katseta da cewa "ba abinda kike bukata ko?"
A zuciyarta tace " me nake bukata kuwa banda inganka?"
Amma a fili tace " babu."
Yace " okay" batai auni ba taji ya katse wayar, tabi wayar da kallo idannunta suka ciciko da kwalla ya zatayi?


Jalal kam agoggon hannunsa ya kalla wanda yakai aka canza mai glass d'in kullum yanzu shi ne a hannunsa ko da wasa bazakaga yasa wani agoggonba bayan shi, murmushi yai yace " Yau nasan kina cikin farin ciki mai yawa."

Kan kujera ya zauna ya d'auko laptop d'insa ya bud'e yafara aikinsa.


Jalal kenan in ka ganshi yanzu bazaka ce shi bane da, kwarewa da kwazo sun canzashi, kaifin tunaninsa ya karo sosai fiye dana da, tunda yabar kasar nan ya fara karatu ya samu wani company na gidan radio yana musu aiki, in zasu dauko rahoto ko wani bincike dashi ake zuwa, hakan yasa ya samu experience dayawa akan harkar karatunsa, haka kuma kud'in da suke biyanshi mai d'an kauri ne, ga kud'in da aka basu na scholarship.
Sunso rikeshi acan amma inaaa ai ko da wasa bai tab'a sawa a ransa zai iya zama a wata kasar ba.









Seemah kam sun gama taro an d'au hotuna kala kala, sun koma gida abin haushi wai Dad har ya tafi Nigeria shida matarsa, haka suka baje a falo akai ta hira, Seemah kam ganin hirar taki karewa yasa ta sulale ta gudu d'akinta, tana shiga tana kokarin Zama a bakin gado tace an murd'a kofar, ta kalli kofar da sauri, Ammar ne ya shigo da sallama ta kalleshi tad'an had'a rai kad'an tace " Yaya baka kwankwasa bafa?"

Ya had'a hannunsa biyu yace " au amin afuwa." Ya fad'a tare da komawa ya rufe sannan yai knocking, tad'anyi dariya sannan tace shigo, nan ya shigo yana cewa " yanzu dai banyi laifi ba ko?"
Ta d'aga kai tare da zama, ya matso ya zauna kusa da ita sannan yace " ya kamata ki kwanta da wuri d'an nasan kin gaji gashi gobe zamu tafi."

Ta kalleshi sannan tace " Yaya?"
Yace " Ummm"
Ta girgiza kai tace " Shikenan ma."
Yad'an d'aure fuska yace " So kike muyi fad'a?"
Ta girgiza kai tare da cewa " ba fa wani abu important bane."

Ya harareta tare da kafeta da ido, tai kasa dakai tana wasa da 'yan yatsun hannunta tace " Yaya dama so nake ka tambayar min Dad a wani gari mahaifiyata take sunan kawai nake san ji."

Ya kalleta cikin tausayawa yace " Karki damu insha Allah kafin aurenmu zan kaiki har garin."
Kai ta girgiza mai tace " basan zuwa nakeyi ba nima kawai sunan nake san ji."
Ya kalleta kawai baice komai ba, cam ya wayence yace "Saura wata d'aya bikin mu ba wani abu da kikeso ko kike tunanin yi?"

Kallansa kawai tai sannan ta girgiza kai, alamar a'a, jikinsa yai sanyi amma ya daure ya shiga bata labari har sai da ta saki ranta, sun dad'e suna hira kafin Ammar yai shiru, kallansa tai tace " Yaya lafiya?"

Ya mik' e jiki a sanyaye ya tsugunna a gaban Seemah tare da rik'o hannayenta, a hankali ta d'ago ta kalleshi ta kasa furta komai, Ammar idanunsa na kanta, ganin bazata iya jure kallan dayake mata ba yasa tai saurin yin kasa da idanta, Ammar cikin wata irin murya mai ban tausayi taji yace " Seemah wani abu na damuna."

D'ago wa tai ta kalleshi idannunta sukayi raurau tace " Name fa?"

Ya kalleta a hankali yace " Tunda aka fara zancen auren mu ba wanda naji ya tambayeki ko kin amince da hakan, na sani sarai haryanzu son da kike ma Jalal bai bar zuciyarki ba haka kuma bana kaunar wani abu dazai sa in zama nine sillar tauye miki rayuwar farin cikin ki, Seemah ina tsoro......."

Hannu tasa ta rufe mai baki hawaye suka zubo mata a hankali ta shiga girgiza mai kai, tace " Ya Ammar na san sarai meke ranka haka kuma nice na zab'a ma kaina auranka bawai d'an ance ba, a'a sai dan nima na amince, kasani sarai bazan iya auran Deen ba bayan abinda ke tsakanin iyayenmu bazan tab'a bin san zuciyata ba akan farin cikin ka dana Dad, nasani kuma ko ince jikina ya bani da ace mahaifiyata nada rai itama wannan zab'in zata min."

Ta share hawayenta sannan ta zare hannunta daga bakin Ammar tad'an yi murmushi tace " Karka damu Yaya nasani a hankali zuciyata zata manta da Deen sannan ka manta shima yayi aure? Maybe ma ya manta dani."

Ammar ya goge kwallar data zubo mai yace " Seemah?"
Mik'ewa tai da sauri tad'an juyamai baya tace "Yaya nafi kowa sanin babban farin cikinka a duniya bai wuce ka ganni ina cikin farin ciki ba na sani sarai da hakan sai dai nima bazan iya jurar ganinka cikin bakin ciki ba."

Ammar ya matso kusa da ita baice komai ba sai dai kalamanta sun mai dad'i sosai, juyowa tai ta kalleshi sannan tamai murmushi.

Kasa magana yai hakan yasa ta rangwab'ar dakai tace " Yaya baza'a barni in kwanta da wuri ba?"
Da sauri yai hanyar waje yana cewa " Inafa zanso hakan."
Ta kalleshi har ya fita, yana fita ta sulale ta tsugunna a katsa tare da rufe fuskarta da hannu biyu, hawaye ne suka gangaro mata ta d'aga hannu sannan tace a fili " Allah na rok'eka ka yayemin san Deen daga Zuciyata kakuma taimaken soyayyar danake ma Ammar ta 'yan uwanta ka ta juye ta koma soyayyar aure."

Nan ta shafa sannan ta zauna a gun.......




Washe gari da safe suka hau jirgi suka baro kasar England....
Nima nace Allah ya tsare...










? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 6? 3?



Jalal kam da safe ya shirya ya fita, gidan Tv d'in *KARAMCI* ya nufa yana isa ya kira director Abbas, nan ya turo aka shiga dashi ciki, sai da aka gama yawo dashi ya gama kallan ko ina kafin ya karasa cikin office d'insa, yana shiga yaga mutane guda uku, nan ya mik'a musu hannu suka gaisa, bayan sun nutsune Director ya kalli Jalal sannan ya kallesu yace " Shine wanda nake baku labari, wanda da kyar ya amince da aiki damu."
Suka kalli Jalal sukai dariya d'aya daga cikinsu yace " lalai munsha labarinka tunda ya dawo daga Germany bashida hira sai ta ka."

Jalal ya d'an yi murmushi kad'an sannan yace " naga ko ina ba komai yayi sai dai na duba programs d'inku kamar akansu ne zamuyi gyara sannan bakwa zuwa neman rahotanni da kanku, in har munaso gidan Tv d'innan ya zama ba kamarshi to sai mun dinga yawon d'auko rahotannin dazai sa hankalin mutane ya raja'a a kanmu."

Director ya kwashe da dariya yace " hakane kam, ya kuka ga Journalists d'in namu?"
Nan suka shiga tafamai sukace lalai munyi dace.
Jalal ya juya kai shi mamaki yake gani yai abin baikai abin dariya ba ko tafamai ba amma ya kasa gane meyasa sukeyi.


Nan ya fara tambayarsa akan program d'in dayace yanaso yai, Abbas yai murmushi yace " Jalal anyi dace shi da jiya dana kirashi ma cewa yai ko yau ne ayi saboda dama zab'e ya kusa yanasan ya nunama talakawa yanda yake kaunarsu."
Jalal yai wani mugun murmushi yace " gaskiya ne yanzu ka d'an kirashi muje ko gobe yanada lokaci."
Ba musu Abbas ya kirashi, PA d'insa ne ya d'auka nan Abbas ya mai bayanin dalilin kiran, PA d'in yace "ok ba damuwa in ya fito daga meeting zan kiraka."
Bayan sunyi sallama ya kalli Jalal tare da fad'amai abinda ya faru, Jalal yace " ba wani abu nizan koma yanda kukai naji, sai dai ina so ka fad'amai shirin da zamuyi dashi LIVE zamuyi, munayin shirin alokacin kuma mutane suna kallo ba wai sai mun gama anyi editing ba ko wani abun."

Abbas ya jinjina kai yace " zam sanar mai."
Jalal ya musu sallama ya fita, gun Sagir ya wuce ya tattara takardun dayasa Sagir ya had'amai sannan yace " Sagir gida nake nema ina tunanin zan fara aiki anan gwara in nemi gida."
Sagir ya kalli Jalal yace " Karka damu zansa a dubama amma wani iri kake so?"
Jalal yai shiru can yace " gida dai dabazai wuce daidai karfina ba, kamar falo d'aya da d'akuna uku, saboda ina tunanin in nace zan dawo nan sai an tilastani d'auko Zainab."

Sagir ya girgiza kai yace " Yanzu Jalal matar taka ce sai ma an tilastaka zaka d'auko ta?"
Harararsa Jalal yai yace " mubar maganar nan kar raina ma ya b'aci."
Sagir ya girgiza kai yace lalai Jalal, wayarsa ya d'auko ya kira Abba, b???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ayan sun gaisa ne Abba yace yanzu zamu taho inaji wajen magrib dai zamu iso, nan sukai sallama.





Su Seemah an dawo gidan Abba, kowa murna yakeyi,nan Dad ya sanar musu cewa ya shirya 'yar karamar walima gobe na taya Seemah murnar gama karatunta.


Dadaddare Abbas ya kira Jalal ya sanar dashi Abdul ya amince gobe da karfe 2 zai zo su gabatar da wannan shirin, Jalal ya saki wani murmushin farin ciki, Abba dake zaune yanacin abinci ya kalleshi yace " Jalal kai da waye naga kana farinciki haka?"

Jalal ya girgiza kai yace " ba komai, gobe in Allah yakaimu sai dai kai ka fara zuwa gidan su dad d'in ni sai zuwa la'asar zan karaso."
Abba ya jinjina kai yace " gwara hakan ma dama banasan muje tare insaka bada hakuri akan abinda bakama sani ba."

Jalal yai shiru baice komai ba, komawa yai kan kujerar da aka ware a d'akin hotel d'in dan masu aiki ya kunna laptop d'insa ya fito da takardunsa ya shiga dudubawa, har Abba yai bacci sai wajen karfe 1 sannan shima ya kwanta a kasan carpet d'in d'akin.




Jalal tun karfe bakwai da rabi ya fita sai dai ya samu wani driver da taxi ya sanar dashi karfe 1 yaxo ya d'auki Abba yakuma mai kwatancen inda za'akaishi, gidan Tvn Karamci ya wuce nan suka shiga shirye shiryen gun da zasuyi program d'in haka kuma tun jiya aka d'inga tallan shirin a gidan tv har yau da safe, komai ya shiryu yanda ya kamata.

Karfe 1 Abba ya fito duk da jikinsa a sanyaye yake sai dai inya tuno Zahida sai yaji bayajin shakkar ko ma menene.

Sukam gidan su Abba kowa yana cikin farin ciki, sani ne ba'ai ba amma Abba da Dad sun sa Mami da matar dad sun gama shirya komai na lefe yau ne kuma suke sa ran a nunama yaram tunda dai komai a gida ne, gida sai farin ciki akeyi, Abba ya karaso gidan ya tsaya a bakin kofa, mai gadi ya kalleshi yace " Malam gun wa kazo?"

Abba jiki a sanyaye yace " Isma'il nake nema."
Mai gadin yace " yana ciki zaka shiga ko a kirashi?"
Abba ya d'aga mai hannu yace " bakomai bari na shiga."

Nan Abba ya shiga harabar gidan ya tsaya yai shiru,; Ammar dake zaune a

29 / 37