JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   34 / 37

99K to 102K   out of 109.4K words

ta kalli Dad tace " Dad a kaf duniyan nan bani da kamarka, ko dan garuwa wanda bashida kwabo ka ce in aura to tabbas shi din nan zan aura babu musu balle tambayar dalili bare Ya Ammar?."
Tai ajiyar zuciya sannan tai murmushi tace " Dad bazan boyema komai ba saboda a haka muka taso banaiya boye ma komai da gaske inasan Deen sai dai duk sanda nake masa bazan iya ture Ya Ammar in zabeshi ba koda kuwa bansan abinda ya faru da ba, balle kuma yanzu na sani."


Hannun Dad ta kama tace " karka damu Dad bazan bari hallacin daka mana nida mahaifiyata ba ya kare akan san zuciya ta ba."
Dad idanunsa suka dan ciciko, yace " Seemah na sani naso kaina dayawa dana hada auranki da Ammar, sai dai babban burina daya ne a duniyan nan, bai wuce inga zuri'ar Fatima da tawa sunyi aure sun hayayyafa ba."

Seemah tai murmushi tace " Karka damu Dad insha Allah wannan burin naka zan cikama shi, tunda na taso agunka ni nake neman abu agurinka baka taba neman wani abu aguna ba sai wannan, ka sha wahala sosai akanmu nida Mahaifiyata insha Allahu wannan burinaka nizan cikama shi."

Tai magana tana kokarin boye hawayenta, Dad cikin tsananin sanda yake mata yace " Seemah inhar auren Ammar bazai......"

Da sauri tasa hannu ta rufemai baki, tace " karka karasa Dad kafi kowa sanin yanda Ya Ammar ke sona, tun ina karama har kawo yanzu, hawaye wannan bayaso yaga nayi, nima kasan yanda na damu dashi, insha Allah zanyi kokarin juya soyayyar danake masa ta 'yan uwantaka ta koma ta......."
Kasa tai dakai bata karasa ba, Dad ya kalleta shima baice komai ba tunani yakeyi, anya ya kyauta ma Seemah kuwa? Jalal ma a yanda ya gani yana tsananin santa.

Katse mai tunani tai da cewa " karka damu Dad zanyi kokarin ganin na cire san Deen a raina sannan na maka alkawari zan kula da Ya Ammar sosai, inaji a jikina wannan shine abinda zanyi wanda zaisa dukda mahaifiyata batada rai zatai alfahari dani."

Idanunsa ne yaji suna neman zubar ruwa da sauri ya mike yai waje, binsa tai da kallo tare da yin murmushi hawaye suka fara zubo mata, tafara cewa " Is Okay Seemah, cool down."





Jalal kwance akan gago yayi shiru tare da kankame memory din daya cire na cikin camera din daya daukesu shida Abdul, nurse ne ya shigo ya kara dubashi tare da bashi magunguna, Jalal ya sha tare da mikewa ya zauna yace " wayata please. "

Nan nurse din ya mikamai, Jalal ya amsa tare da kiran Zaid, dan yasan wayar Ammar a kashe take.
Ringing uku Zaid ya daga yace " Jalal ya akai? Ina cikin shaukin kauna zaka kirani?"

Jalal ya girgiza kai yace " Zaid matarka zatai fama, ni ba Ammar please. "
Zaid yasa dariya tare da cewa " ai matar tawa kanwarka ce kaga sai kushirya yin faman dakyai."
Jalal yace " me kake nufi?"
Dariya Zaid yai tare da mikama Ammar wayar, Ammar dake tuki suna hanyar dawowa ya amsa tare da cewa " Jalal ya? Allah dai yasa ba wata matsalar bace?"
Jalal yace " Ba wata matsalar Senate din sun wuce dashi police station sai dai....."sai kuma yai shiru.

Ammar cikin damuwa yace " menene? "
Jalal yace " tunani nakeyi anya ya kamata mu bada evidence din nan? Naga kamar zuciyarshi ta karaya shi yasa nake tunani."

Ammar yai shiru nadan sakwanni sannan yace " Haka ne mu barshi kawai kodan Seemah ma ina tsoron kar tagani dan ko bata fadaba nasan abin zai zamar mata gyambo a zuciyarta."

Jalal ya jinjina kai yace " kuna ina yanzu?"
Ammar yace " muna hanya munkusa shigowa birnin gwarin ma, Jalal yace " nagode Ammar sosai...."
Ammar ya katseshi " Zaka fara ko?"
Jalal yai murmushi yace " Sorry amma me dazu Zaid yake nufi?"

Ammar ya girgiza kai yace " kasanshi ai, daga gani Zahida wai ita yakeso kuma yanzu."

Jalal yai dan dariya kaan yace " kaii Zaid sai a slow...."



Nan sukai sallama suka kashe.
Jalal na zama wani bafade yazo yace " mai martaba na nemanka."
Jalal ya mike suka fita tare, zaune yake a kasa, mai martaba yace " ya jikin naka?
Jalal yace " da sauki."
Sarki yace " ya ya ina abinda aka dauka nima na gani?"

Jalal yai shiru, Sarki yace " ya akai kuma?"

Jalal ya kalleshi yace " matsala aka samu ai, ashe bamu kunna recording ba a lokacin."

"OHHHH abin dai baiyi dadi ba amma ba komai naji ance ya aminta da lefin yimata fyaden a station din 'yan sandan."

Jalal ya kalli shi jiki a sanyaye, yace " mun gode sosai da taimakon da ka mana, zan wuce nima yanxu 'yan uwana suna hanya."
Sarki ya jinjina kai tare da cewa " Kuma Abujan zakuyi?naji shima can za'a wuce dashi "

Jalal yace " eh."
Nan yamai Sallama zai mike Sarki yace " Jalal?"
Juyowa Jalal yai ya kalleshi, Sarki yai murmushi yace " ka birgeni sosai, I wish ina da yarinya da na hadaka da ita, sai dai inaso kaje ka duba ko wani gun aiki ne indai har ya maka kanaso to ka sanar dani ni kuma zan nemar maka aiki a ko inane a doron kasar nan."

Jalal yai murmushi yace " na gode."
Nan yamai sallama ya fita, Sarki yai murmushi cikin gaskiya Jalal ya kwantamai a ransa.



Jalal gidansu ya koma ya dan shishigar da kaya, yana gamawa su Ammar na isowa nan suka shiga mota suka kama hanyar Abuja.







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com



No. 7? 3?



Sunyi nisa a hanya Zaid duk ya ishe Jalal da zancen Zahida, hakan yasa Jalal ya kwantar da kansa a jikin kujera tare da rufe ido kamar mai bacci, Ammar ma yasa earphone a kunnensa tare da maida hankalinsa kan titi, shikam Zaid sai zuba yakeyi, ganin shariyar tayi yawa yasa shima haushi ya isheshi yai shiru, sunyi nisa jin Zaid yayi shiru yasa Ammar ya lekashi ta glass din mota, ganin Zaid yayi bacci yasa ya zare earphone din tare da kallan Jalal kadan yace " Bacci?"
" Nope kawai idona na rufe."

Ammar yai ajiyar zuciya yace " Me ka tsara yanzu zakai?"
Jalal idanunsa a rufe yace " Ina tunanin neman aiki a kaduna ne so nake mu koma can gaba daya, banajin zaman Abujan nan yanzu."

Shiru Ammar yai hakan yasa Jalal ma yai shiru, sunyi shiru kawai Jalal jiyai Ammar yace " Saboda Seemah?"

Cikin mamaki Jalal ya bude ido ya kalli Ammar sai dai ya kasa magana, Ammar ya maida kansa titi tare dacewa " Hakane kenan?"

Jalal ya mike zaune ya kalli Ammar yace " Ammar."

Ammar ya dan kalleshi tare da yin murmushin karfin hali yace " Jalal menene matsayin Seemah a gunka?"

Jalal ya kalli Ammar cikin tsananin mamaki yace " Ammar meyasa kake wannan maganar?"

Ammar yace " Jalal tambaya kawai na maka amma in kana ganin bani amsar zatai wuya mubar maganar kawai."

Komawa Jalal yai ya kwanta tare da kallan window yace " Ammar karka manta ankusa aurenku da Seemah saboda haka karka fara sa wani abu a ranka."

Gefen titi Ammar ya koma da motar yai parking tare da tattara hankalinsa kan Jalal yace " Jalal bazaka gane me nakeji bane a wannan lokacin, kawai dai ina daurewa ne nai murmushi na kuma ci abinci amma kasan zuciya ta jinake kamar I am useless, na ka sa yima Seemah komai kai kuma ka sadaukar da komai naka akanta, bazaka fahimci me nakeji bane."

Jalal ya kalleshi cikin wani yanayi yace " Ammar kenan, haka kake tunani a ranka? Ni a zuciyata nine nake useless mahaifina shine dalilin lalatama mahaifinka rayuwa, sai dai duk da haka baiyi tunanin komai ba ya rike Seemah kamar 'yarsa, kana tunanin wannan dan abinda nai yakai kwatan abinda mahaifinka yai?"

Ammar ya juya kai yace " Jalal ka manta ne? Mahaifina fa kace bani ba, na sani Dad yayi komai domin Seemah amma ni fa?."
Ya juyo ya kalli Jalal idanunsa suka kada yace " Jalal what about me?"

Jalal yai wani murmushi yace " Ammar taya zaka fadi haka? Kaine kuwa ka mata komai kasan tun da muka hadu da Seemah zancenta daya Ya Ammar, na tabbata da tun farko tasan kai ba Yayanta na jini bane da ko kallona Seemah bazatai ba."


Ammar kallan Jalal yake kawai, Jalal ya dafashi yace " nayi tunani mai yawa bayan naji abinda ya faru tsakanin iyayenmu, zance daya ne ya tsayamin na kuma tabbatar dashi, Ammar shine mutum na farko a duniyarnan da nakeji zai iya rike Seemah fiya dani, zai kuma bata kulawar da ya kamata, zai kuma sa ta manta abinda ya faru da mahaifiyarta."

Ammar ya runtse ido tare da kallan window, a hankali yace " Jalal I I I......"
Sai kuma ya kasa karasawa, Jalal ya kalleshi da mamaki yace " Ammar na san ya kakeji aranka saboda abinda naji kenan a lokacin da naji abinda mahaifina yai, sai dai abu daya na sa a raina, zanyi kokarin ganin na rage gaba da tsanar dake tsakanin mahaifanmu, inaji kamar in nai hakan ne zaisa mahaifanmu su koma kamar da."

Ammar yamai murmushi tare da cewa " Jalal na gode sosai."

Jalal yamai murmushi yace " Ammar ba wanda Seemah ta dace dashi kamarka, zaka kula da ita sama dani na shaida hakan."

Murmushi sukama juna, Ammar ya tada motar tare da hawa kan titi yace " Jalal nagode sosai, sai dai Seemah fa? Inaji ajikina kamar...."
Jalal ya katseshi da cewa " Ammar trust in ur self, Seemah yarinyace bata gama sanin menene so ba sannam karka manta macece ita, nina fadama ka sa a ranka ko shekara bazaku rufa da aure ba zakaga Seemah ta manta dani."

Ammar yadan harareshi yace " ce maka akai inasan ta manta dakai?"
Jalal yai dariya yace " to me kakeso?"
" taya zata manta dakai bayan amintarmu nanan?"

Jalal ya sakeyin dariya kadan tare da nuna Ammar cikin zolaya yace " yanzu ka aminta da amintarmu kenan?"

Ammar yai murmushi tare da cewa " Jalal bansan meyasa ba abinda bazan iya fadama Junaid ko Habib ba inaji a jikina zan iya fadama, banaji zan iya boyema komai."
Jalal ya dan furzar da iska yace " nima haka Ammar jinake kamar munyi shekaru dayawa tare."

Dariya sukai nan suka shiga hirar rayuwa.

Sun isa Abuja Jalal yace " Ammar saukeni anan."
" ina zaka haka?"
Jalal yace " inasan ganin Sagir ne akan gidan danace ya samomin, yanzu banajin zan zauna anan."

Ammar ya mai wani kallo yace " Jalal please kazauna a inda ka samu aiki taya zakaki zama anan bayan ka riga kasamu aiki, kai zamanka kawai kenan kana so kacemin in mukai aure zumuncinmu ya tafi kenan?"


Jalal yace " Ahhh to bari inji me Abba zaice tukunna, amma yanzu saukeni tukun."
Nam Ammar yasamu guri yai parking Jalal ya fita tare da cewa " oh ni wannan Zaid din taya namiji zai zake yai ta bacci haka?"

Jiyai Zaid yace " Idona biyu nadai barku kuyi magana ne."

Da sauri Jalal ya kalli Ammar shima Ammar ya kalleshi, Jalal ya hadiye yawu yace Ammar sai munyi waya ko?"

Ammar ya daga mai kai, nan Jalal yai waje, Zaid ya kwashe da dariya yace " au wai kunya kukaji?"

Ammar ya tada mota ya wuce baice komai ba.
Sunkusa isa gida Jalal yakirashi, nan Ammar ya daga, Jalal yace " Ammar yanzu aka kirani daga police station sun iso dashi nan Abuja, amma kana ganin ya kamata Seemah taje?"

Ammar yace " mu bari tukunna ya nemeta da kanshi."
Jalal ya jinjina kai nam sukai sallama.



Suna isa gida Ammar ya shiga ciki da sauri, falo ya duba baiga Seemah ba Zahra ya gani ta fito daga daki yace " Zahra tana ina?"
Zahra tace " tana kitchen, abinci takema."
Wani sansanyar murmushi yai sannan ya wuce kitchen fin da sauri, tana tsaye tana gurza karas a greater, Ammar ya lalaba ta bayanta ya rufe mata fuska, murmushi tai tace " Ya Ammar ka iso?"

Saketa yai ya dawo ta gabanta yace " ohh na dauka bazaki ganeni ba."
Tai murmushi tace " Yaya na fadama taya za'ai in kasa gane ka?"
Turamai kujera tai tace zauna yaya ka gani.
Ammar ya kalleta yace " taya zanyi inzauna ke kuma kina aiki?"

Tace " me? Zaka tayani ne?"
Kai Ammar ya daga mata alamar eh, tai murmushi sannan ta dauko albasa da wuka da kwano ta mikamai tace " To gashi."
Hararar wasa ya mata yace " hmmm wato wayau ko? Kin dauka bansan albasa yaji gareta ba?"

Tadan hade rai kadan tace " shikenan tunda ba tayani zakai ba kawo na karasa kayana." Tafada tare da kokarin dauke kwanon.

Ansar kwannan yai a sauri yace " cewa nai bazan yi ba?"
Tai murmushi tare da ajiyemai, can ta daure tace " ina kuka je?"

Ya kalleta yace " mun danje birnin gwari ne."
Ta kalleshi kadan tace " da Deen?"
Kai ya daga mata tare da kura mata ido, murmushi tai tare da saurin wayancewa tace " ahh Yaya albasar dai ba yaji ko?"

Daurewa yai shima yace " akwai amma kadan."

Suka kalli juna sukai murmushi.







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

_Ina bawa masoyana hakuri najina shiru da kukai, kuyi hakuri amma insha Allahu zanyi kokarin ganin na kammala littafinan acikin satinnan, nagode kwarai da san da kukema littafin nan....Luv U Ol d'_


No.7? 4?




Abdul zaune yana kallan uwargidansa kallan tsananin mamaki yace " Rabi kinsan me kike fada kuwa? Ban gani in sakeki ba ina cikin wannan yanayin ba?"

Wata dariyar rainin hankali tamai tace " me? Kana tunanin soyayya ce tasa na aureka?"
Tai wata dariyar rainin hankali tace " are you naive or fool? Kai kana tunanin duk mutanen dake kusa dakai saboda suna sanka ne ko suna san kudinka? "

Abdul cikin mamaki ta kalleta yace " Rabi da kikazo na dauka abu na farko da zaki fara tambaya shine meya faru a shekara 20 din? Da gaskene? Sannan ki tambayeni halin da nake ciki a gidan yarin nan amma......"
Katseshi tai cikin fada tace " so kake inzauna ka fadamin wani shirme dakai a baya? Ko ce maka akai na damu da halin da kake ciki? Takardata nake bukata dumin inasan barin kasar nan cikin gaggawa kafin laifinka ya fara kokarin shafata."

Abdul ya kalleta cikin tsananin mamaki yace " me ne? 'Ya'yan mu fa? Ko kin manta da 'ya'ya a tsakanin mu?"

Rabi ta saki wata dariya taban haushin mai sauraro tace " 'ya'ya? Ahh haka ne ashefa kai baka sani ba ko? Amma ina mamakin ina hankalinka yake, sai dai kayi hakuri 'ya 'ya nawa ne ba ka da hadi dasu."


Abdul cikin mamaki yace " me kike nufi nufi da kalamanki? "
Tai tsaki tace " malam inka ga dama ka saken in bakaga dama ba kai ta ajiye da sakinka zan koma dubai da abokinka Marfuz wato uban 'ya'yana inka ga dama ka aiko mana da takardar saki can." Tana kainan ta mike, cikin zafin rai ya riko hannunta yace " marfuz? Abokina? Me kike nufi?"

Hannu tasa ta fizge hannunta da karfin gaske tace " matsalarkace, tana kaiwa nan tai waje."

Kai ya shiga girgizawa ya tuna shine sanadiyar arzikin marfuz kuma shine abokinsa da ya dinga zigashi akan abubuwa marasa kyau ciki kuwa harda fyad'en dayama fatima.
Ihu yasa cikin tsananin takaici ya rike zuciyarsa dake kuna tare da tsugunnawa a kasa, lalai kuka ma rahama ne, jiyai sam ya kasa kuka, sai wani irin zafi da zuciyarsa keyi.

Guard din dake bakin kofa ya kalla yace " dan Allah......."
Ai bai karasa ba yaji numfashinsa ya rike, nan guard din ya matso da sauri ya shiga danna mai baya, dakyar numfashinsa ya dawo.

Abdul sam ya kasa cin komai, a zaune kawai yake shikadai yasan me yakeji.


Jalal kam ya zama celebrity a gari ko ina ka duba kaga hutunshi a magazine ko a jarida ansa Jarumin da baya tsoron hukuma sai gaskiya, duk shirin dayace zaiyi kuwa a gidan tv to lalai zakaga mutane sun zako akan ganin me jarumi kuma matashi zak gabatar.

Biki ya matso, sai dai Zahra ce kadai take shirin bikin amma sam Seemah batasa baki a harkar in Zahra tazo mata da xancen ya zasuyi kaza, kya kacinta kawai tace to, dama ba fita take ba inba gidan Ya Habib taje ba, yau saura sati daya biki, gida ya fara cika, hakan yasa yau Seemah ta tattara kayanta kamar yanda Dad yace akan ta koma gidansa saboda matarsa tazo itama, ta gana cikin gada kayantane ta ci karo da agoggon ta kurama agoggon ido tai nan fa ta fara tunano rayuwarsu ita da Jalal, kallan agoggon take ta kuma zarfafa cikin tunani, Ammar dake tsaye a jikin kofa ya taho da saurinsa zai nuna mata katin biki na dinner daya amso, ganinta a zaune tasa a goggo tana kallo yasa ya tsaya, hannu a harde tare da jingina da jikin kofar, basai Seemah ta fadamai ba yasan agoggon da take kallo me yake nufi dan kuwa agoggon dake hannun Jalal kenan kullum, ya kuma gansu iri daya sak, jiki a sanyaye

34 / 37