JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   23 / 37

66K to 69K   out of 109.4K words



Ga mamakinsa murmushi yaga tayi tace " zaizo."

Anan shagon ta la'asar Amadu yabata biscuit da lemo, duk da yunwar datakeji taki amsa, duk k'iran da Amadu yake makama Isma'il a waya sai ace wayar a kashe, ga magrib ta duso, Jalal ne yazo gunsa, yace " yauwa Jalal zauna ka taya Aunty hira bari naje gidansu Ammar in dawo."





_Dad ya kallesu tare da matse kwallar sa_


Yace " Seemah bansan meya faru ba, nidai Amadu yazo mukai sallar magrib a massallaci tare muna fitowa yasanar dani komai, da sauri muka nufi shagon ni dashi.

Sai dai me? Shagon muka gani kamar ba kowa, hakan yasa na shiga ciki da sauri shi kuma ya zagaya, ina shiga na tadda Fatima tsirara ba kaya a kwance, kamar ma ta ruga ta suma, kana ganinta kasan ta karfi aka mata, na matsa da sauri na tallabota idanuna a rufe na riko zaninta na lil'iba mata, Amadu ya leko cikin tsoron abinda ya faru ya zube agun, nikam rungumeta nai na shiga wani irin kuka mai ban tausayi, ban farga ba naji mutane a waje ana hayaniya.

_Dad ya share kwallarsa_
_Seemah kam kukanta ya tsananta anan_


Amadu ne ya kallan yace " yi sauri ka fito da ita samarin garin nan ne bansan wa ya k'irasu ba."

Na d'agota tare da nad'a mata zani, ina fitowa aka fara jifansa da dutse, ganin zasu sameta yasa na juya sukai ta dukana, wani daga cikinsu ma bamusani ba ashe yasa kalanzir kawai sai ashana mukaga an kyasta, haka na d'aureta abayana dakyar mukasha zuwa gida.





Sai dai me? Bala'in dana tarar a gida a wuce nacan, Hajiya harta suma, Samira ma ciwonta ya tashi, sai numfashi kawai takeyi, tana ganina d'aure da Fatima kawai tayi baya luuuu, abinda ya firgitani agun tace ga garinku nan.


Kuka ma rahama ne, a wannan ranar hawaye ma kasa zubomin sukai, Kawo da jama'ar gurin suka had'u aka fara zancen yima Samira wanka, nan Kawu ya kalli Amadu a tsakiyar mutane yace " Amadu ka tabbatar da abinda ka fad'a cewar Isma'il shiya mata fyad'e?"

Da mamaki na kallesu ni kuma? Abinda ban tab'a zataba sai jinai Amadu yace wai eh, ya ganni da idanunsa.

Kuka sosai kawu yai, kowa ya shiga ala wadai dani, Abdul ya koma gida cikin taron jama'ar biki yace " bazai aure Fatima ba, d'an ankamata da wani a shago."

Tsinuwa kuka nashata, wani abin takaicin Fatima data farfado, sai kuma ba baki, ta kasa magana, duk yanda taso tai magana ta kasa, anan aka fara jifana akan lalai kafi namata da alama ma abu nasa na danne bakinta, yunk'urin ihun dataitayi yasa muryarta ta tafi.





Dad ya kallesu hawayensa sun tsanan ta yace ban tab'a ganin bala'i kiri kiri irinta wannan ranar ba, kowa ya gujeni, A lokacin na ba Fatima takarda akan ta rubuta min sunan wanda yamata fyad'e, tana kok'arin rubutamin, Tayi baya luuu, bakinciki harya gama cin jikinta, haka na kaita asibiti aka bata gado, sai dai kamar ba rayayyiya ba, tana kwance ne kawai sai numfashi, d'anginta suka sallamata aka watse da ala tir.


Fatima na asibiti har wata 2, Kawu da Hajiya sunyi sunyi inrabu da ita sai dai gani nake in na kyaleta mutuwa zatai d'an bakin ciki, alokacin ne kuma akace tanada ciki.


Ganin zaman garin na neman gagararmu yasa muka dawo Suleja, anan ne har Fatima ta kawo watan haihuwa, tana haihuwa tace ga garinku, Hajiya kam da Kawu sun ma dainamin magana sam, yaya ma duk yanda yaso da in rabu da Fatima sai dai na kasa, haka na zauna agun gawar naita kuka kafin aje amata sitira.


Dad na zuwa nan yakasa magana Seemah kam jitai kanta na juyawa Ammar ya matso kusa da ita yace " Seemah, in ihu ne kiyi amma karki had'iye komai a ranki."

Kallansa tai kawai tai baya luuuuuu, Habib ma kuka yake sosai, Dad ya mik'e dasauri ya d'auketa yai waje da ita.






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

*_This Page is for you my dearest Friend Umma, and also my Swt kanwa Somaya=?
? Miss Hot Purple luv u soo much_*




No. 4? 9?



Jalal kam yana tsaye a gate d'in gidan su Habib, mai gadi ya kalleshi yace " Bawan Allah d'an Allah ka tafi na fad'ama Hajiya Seemah bata nan."

Jalal ya kalleshi sannan yace " naji ai baba kuma na yarda to so nake naji tana ina?"

Zaiyi magana sai ga Aisha ta fito da alama asibitu zata kai abinci ganin basket d'in kuloli a hannunta, kurama Jalal ido tai kamar tasan shi, can ta matso tare da mik'ama Bala basket d'in yasa a mota.
Ta kalli Jalal tace " Kamar na sanka ko?"
Jalal ya kalleta yace " anya kuwa? Amma da alama daga gidan kike, Seemah fa?"
Sai alokacin ta tuna shine yaja Seemah rannan da suka fita tare, ta sakarmai murmushi sannan tace " tana gidan Yayan Babanta amma yanzu ya Habib yai waya yace wai ankaita asibiti da alama batajin dad'i."
Jalal yace " mene? Meya sameta? Zazzab'i take?"
Dariya Aisha tai tace " wanne zan amsa daga ciki? Bayan nima bansan komai ba? Yanzu dai zanje asibitin sai ku tafi tare."
Jalal ya runtse ido sam hankalinsa ya gaza kwanciya, nan Bala ya fito da mota Jalal ya shiga gaba suka wuce asibiti.
Seemah kam bayan ta farfado sai ta hau rawar sanyi, nan likitan yasa mata drip sannan ya roki da abarta ita kad'ai da alama taji abinda ya firgita tane.
Abba, Dad, Kawo, Ammar, Habib, da Mamie suna zaune a d'akin da aka kwantar da hajiya, itama dai jikin ba dad'i a zaune kawai suke amma kowa da abinda ke ransa.
Sun isa asibiti, Aisha ta kalleshi tace " zamuje tare ne?"
Jalal ya tuna kalaman Dad na d'azu hakan yasa ya kakaro murmushi yace " Jeki kawai karma asan tare muka zo."
Ta kalleshi da mamaki amma bata tambaya ba ta ce to, sannan tai gaba.
Jalal kam zuciyarshi ta gama dakewa abu d'aya kawai yasa a ransa awannan lokacin shine bazai tafi ba tabbas sai yaga Seemah, saboda gobe yakesa ran zuwa Birnin/gwari d'an yaji menene tsakanin Dad da Abbansa.
Karasawa yai bakin d'akin da aka kwantar da Hajiya bai shiga ba kuma bai kwankwasa ba kawai a tsaye yake, sam baisan d'akin kusa da Hajiya nan aka kwantar da Seemah ba.

Bayan Aisha takai Abincin ta fito ne wajen bud'e kofa yasa Habib ya hango Jalal, ransa ya k'ara tunzura a zuciye ya fito waje yazo kusa da Jalal ko kofar bai rufe ba, a lokacin ne hankalinsu yakai kansa.
Habib na zuwa kusa da Jalal, kafin Jalal yai auni yaji an makamai naushi a kunci, dukan ya shigeshi d'an sai da gefen leb'ensa ya fitar da jini, Habib ya mik'e zai k'aramai wani Jalal ya rik'e hannun.
Daidai nan 'yan d'akin suka fito, Kallan kallo suka fara kafin Jalal yace " Ya Habib mena maka kuma?"
Fizge hannunsa yai da karfi sannan ya nunashi da 'yatsa yace " Jalal wallahi id'an har baka bar nan cikin minti 5 ba bansan me zan ma ba."
Kallansa yai da alamar tambaya yace " na maka wani abin ne? A iya sanina ban ma abinda zan cancanci duka ba."

Muryar Abba ce ta katsesu yace " Habib meye hakan kake?"

Habib ya bugama Jalal wani kallo sannan ya wuce d'akin, kowa ya koma d'akin aka rufe kofar, Jalal yabi kofar da kallo, jiyai ansake bud'ewa Ammar ne ya fito yazo kusa dashi tare da mik'amai handkerchief, Jalal ya kalleshi da jajayen idanunsa sannan ya amsa, a hankali ya furta thanks.

Ammar ya kalleshi yace " please Jalal ka tafi."
Jalal idanunsa suka kara kad'awa yace " Ammar menai? ni Seemah kawai nakesan gani naji ance bata da lafiya, banaji zan iya tafiya ba tare da na ganta ba."

Ammar ya runtse ido shima idanunsa suka ciciko, yace " Banaji itama Seemah zata so ganinka a wannan lokacin."
"Meyasa? Taya akai kasani? Banaji itama akwai abinda zaisa takisan ganina."

Ammar ya dafa kai sannan yace " ni kaina daurewa kawai nake amma basan magana dakai nakeba, ka koma ka tambayi mahaifinka waye ya rad'ama suna? Da wa aka haifeku rana d'aya? Sannan wani irin sakayya yama babban amininsa?" Yai ajiyar zuciya sannan ya cigaba" wad'annan amsoshin sune zasusa kagane meke faruwa."

Ammar nakainan ya bud'e d'akin da Seemah take yasa kai, daidainan Jalal ya hangota kwance akan gado ana mata k'arin ruwa, daga nesa ya hango fuskarta jiyai kamar zuciyarsa zata fito, kofar ce ta rufe sakamakon turata da Ammar yai, Jalal yabi kofar da kallo idanunsa sunyi jaa ga sun ciciko, kurama kofar ido yai, ga magrib tayi.

Wucewa yai yaje massalaci, suma sun firfito sallah, bayan sunyi sallah kafin su koma shi ya rigasu isa, harya sa hannunsa zai bud'e kofar, yaji bazai iya ba tabbas bazai shiga ba harsai ance ya shiga, kuma bazai tafi ba harsai ya ganta.

Komawa yai ya tsaya a gunsa na d'azu, ga mamakinsu duk sun d'auka ya tafi sai dai ganinsa yasa suka d'auke kai suka shiga, Dad da Ammar sukai d'akin Seemah, suna shiga daidai nan ta bud'e idanunta a hankali, haryanzu jikinta zafi tsau kamar garwashi, ta kurawa Dad ido, ita kad'ai tasan me take tunani, kallanta yai tare da cewa " Swthrt kin tashi?"

Ta k'ak'aro murmushin da kana gani kasan yak'ene ga leb'enta ya bushe, a hankali tace " Dad tambaya nakesan yi?"
"Inajinki 'yar Dad."
Had'iyar wani abu tai sannan tace " Jafar da aka haifa rana d'aya da Ya Ammar, wanda mahaifinsa yama sharri ya kuma cutar da mahaifiyata, shine........?" jitai ta kasa karasawa sai motsa baki take tanasan magana amma kuka ya hanata, Ammar ya share hawayensa tare da matsowa kusa da ita yace " Dad zan bata amsa jeka kawai."

Dad ya mik'e jiki a sanyeye, Ammar ya matso kusa da ita ya zauna, tare da kallanta yace " Seemah sai me? Inshine Jafar d'in da kikeso? Meye zaisa ki k'ara tada hankalinki?"

Kai ta shiga jijigawa tace " akwai komai kuwa yaya."
Hannu tasa a saitin zuciyarta tad'an buga kad'an tace " taya za'ayi zuciyata taso wanda d'ansa ya taimaka wajen ruguza rayuwar mahaifiyata? Meyasa nakejin zuciyata tana zafi?"

Kuka ne yaci karfinta hakan yasa ta kasa karasawa, Ammar ya share kwallarsa yace " Seemah please kidaina please Seemah."

Kuka take sosai ta kasa tsagaitawa, dakyar ta daina sai kuma ta shiga ajiyar zuciya akai akai.


Jalal kam har karfe 12 yana nan a tsaye, harsu Kawo da Abba da Habib suka koma gida sukabar Dad agun Hajiya, Ammar agun Seemah.

Kowa mamakin yanda yak'i tafiya yakeyi, gashi a tsaye yake ko gajiya baiyi ba ne ko me? Dad yana tsaye ta window yana kallansa, har bacci yafara d'aukan Dad, Ammar kam gun Seemah ya koma, ya kalleta yace " Seemah, Jalal fa na waje tun kafin magrib yake a tsaye a waje."
Kallansa tai cikin mamaki idanunta suka ciciko tace " Yaya?"

Jinjina mata kai yai yace " ko na karshe ne ki ganshi kuyi sallama."
Ta share hawayenta tare da cewa "Ya Ammar?"

Mik'ewa yai ya fito tare da kallan Jalal da kana ganinsa kasan dauriya ce kawai yakeyi ta jaruman maza amma tabbas ya gaji, ya kalleshi yace ka shiga.

Jalal ya d'ago ido tare da murmushi yace " tnz Ammar."

Sai dai me? Sam ya kasa d'aga kafarsa jiyai kafar tamai nauyi, sai Ammar ne ya taimaka mai ya shiga d'akin, a tunanin Ammar Dad yayi bacci, sai dai Dad jin magana yasa ya lek'o ta window yana kallansu har Jalal d'in ya shiga.

Kusa da Seemah ya zauna, sam ta d'auke kai daga kan Jalal, Ammar ya fita ya basu guri.

Jalal ya kalleta baisan sanda hawayen da yake b'oyewa suka zubo ba, a hankali yace " Meemah ya jikin?"

Jin sunan Meemah da yak'ira sai da zuciyarya ta amsa, batasan sanda?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ta kalleshi ba, idannunta na hawaye, yace " ya akai kika rame haka a kwana d'aya? Bakya cin abinci ko? Hala shiya haifar miki da zazzab'i."

Ta had'iyi wani abu sannan ta kalleshi tace " meyasa kazo nan? Bayan banasan ganinka?"

Jalal ya girgiza kai hawaye ya zubo mai yace " ta ina zakik'i san ganina bayan zuciyarmu na tare?"

Ta share hawayenta tace " a da kenan."
Jalal kalmar har ransa ta tab'a amma ya d'aure yace " bana tunanin a da ne, tunda haryanzu zuciyoyinmu basu rabu ba."

Mik'ewa tai ta zauna fuskarsu na kallan juna ta goge hawayenta tace " Deen I can't be with you ko da kuwa sanka shine zai zama ajalina, mahaifinka ya cuceni, ya cuci mahaifiyata, ya cuci Dad d'ina bama haka ba ya cuci duk zuri'ata data Dad banajin zan iya yafe mai."

Jalal ya kalleta cikin mamaki, idanunsa ya zaro yace " Meemah me kike nufi da kalamanki."

Hannu tasa ta fara dukan kafad'arsa tana kuka tace " Meyasa zuciyata bazata tsaneka ba why?"

Jalal ya rik'e hannunta yace " Meemah me mahaifina yai?ban gane ba?"

Ganiyai jikinta ya shiga rawa, duk ya rud'e tare da K'iran sunan ta, ai ganiyai tayi luuu gab'a d'aya jikinta.

Da karfi yake k'iran sunanta yana hawaye, Amnar ya shigo da sauri, ganin haka yasa ya fita k'iran likita.

Abinda yaban mamaki, Jalal nagani ya tsuguna yana kuka kamar mace, a raina nace baka fara bama d'an saurayi.







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 0?


Jalal ganin Seemah a sume ya rasa inda zaisa kansa kuka kawai yake, yarasa meke faruwa shikem, addu'a kuwa duk wacce tazo mai yi yakeyi, kallanta yakeyi zuciyarshi sai kuna takeyi, Ammar ne yashigo da likita da sauri, nan likitan ya shiga duba Seemah, ya samu ta dawo daidai ya kalli Ammar da Jalal yace " ba nace kar a tada mata hankali ba? A barta ta samu nutsuwa ba? Ina tsorace muku abinda zai faru inbaku kiyaye dokukin nan ba."

Yana kai nan yai waje, Jalal ya kalli Ammar da idanunsa da suka sha zubar da kwalla, yace " Ammar am.........."
Ammar ya katseshi da cewa " Jalal please get out."
Jalal ya kalleshi cike da tausayi yace " amma......"
Ammar ya d'aga mai hannu tare idanunsa taf da kwalla yace " Jalal kake kawai please. "
A hankali Jalal ya karasa kusa da Seemah ya kalleta cikin tsananin tausayi da bege sannan ya juya harya kai kofa yaji muryar Ammar yace " idan kaje katambayi Mahaifinka waye mahaifin Seemah, shikad'ai ne abinda muke bukata yanzu daga gareka."

Juyowa Jalal yai cikin tsantsar mamaki bai fahimci inda kalaman suka dosa ba, me suke ba Dad bane mahaifin Seemah ko me?"

Dad ya gani a bakin kofa, wani irin kallo Dad yamai, Jalal yai kasa dakai tare da cewa " Yahkuri na sab'ama umarnink......"
Hanya Dad ya nuna mai alamar yai waje, hakan yasa Jalal ya taka a hankali yai waje, yana fita yazauna akan dakalin gun, tare da rik'e kansa dake wainawa, agogon hannunsa ya kalla karfe 2 na dare ya buga, mik'ewa yai a hankali bayaji zama ya kamaceshi dole gobe da sassafe ya dira a birnin/gwari d'an jin me mahaifinsa ya sani dangane da abinda ke faruwa, kofar d'akin Seemah ya kalla tausayinta ya kara ratsashi, da alama yau tasan ba Dad bane mahaifinta sannan me ake nufi da Abbansa ya sani?
Da alama Abba ne kad'ai yasan amsar tambayoyin nan.



Seemah kam sai karfe hudu ta bud'e ido a hankali, Ammar ta kalla dake zaune akan kujera yana bacci, ta mik'e a hankali tare da yaye bargon da aka rufa mata, tai bakin kofa, a hankali ta bud'e kofar gudun karta tasheshi.
D'akin Hajiya ta shiga, Dad na zaune shima yana bacci, ta karasa kusa da Hajiya tare da rik'e hannunta da hannuwanta biyu, Hajiya ta bud'e idanunta ta kalleta, Seemah hawaye suka zubo mata tai kasa da ido tace " Hajiya kiyi hakuri nasani dolene ki tsaneni, ko nice akama d'ana haka dolene in tsani duk masu hannu a harkar, sai dai nasani a kasan ranki baki tsaneni ba."
Kallanta Hajiya tai da alamar tambaya, Seemah ta matse kwalla tare da kakaro murmushi tace " da kin tsaneni nasan da kin tilastama Dad ya rabu dani, da bazaki bari har ya rainani izuwa yanzu ba."

Ta zare hannun hagunta ta share hawayen dake mata gudu tace " Nagode Hajiya da taimakonki, nagode sosai Allah ya saka da alkairi."

Hawaye ke zuba a idanun Hajiya a hankali tasa d'ayan hannunta akan Seemah sai dai abinda takeji a kirjinta mai nauyi yasa ta kasa magana, Seemah ta girgiza mata kai tace " A'a hajiya basai kince komai."

Tai ajiyar zuciya sannan tace " Hajiya na rok'eki ki yafema mahaifiyata da ni, d'an Allab ba dan mu ba."

Seemah na kawo nan taji kuka

23 / 37