JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   11 / 37

30K to 33K   out of 109.4K words

kai abinda nacemaka please Habin banasan abinda aka birneshi da kyar a kara hakoshi."


Kallan mamakin kalamanta yake sai dai ya daure ya mike yace shikenan bari mu wuce.





Zaid bin Seemah yai a tsaye a jikin mota ya ganta, karasawa yai tareda mika mata wayarsa yace ur number is needed here!

Juyawa tai tace" bazan iya bada wa ba."

Zaid yace "Kefa kanwatace, d'an haka dole ne ki samin number dana bukata."

Murmushin mugunta ta saki sannan ta amshi wayar tasa number tai dialing ringing 2 ta katse tace gashi nasa in naje gida zan gani dan ban fito da wayata ba."

Murmushi ya saki yace " Amma Ammar yaci amana ta dabai tab'a nunan hotonki ba."

Kallansa tai tace " ko kuma mutuncin dake tsakaninku bai kai ya kawoba ba, tunda dai ko abokanansa sunsan hotonane akan screen d'insa."


Matsowa yai kusa da ita yace " Wow I really like ur Style dear. "


Mota tai saurin bud'ewa ta shiga tare da kulle kofar, Murmushi zaid ya saki sannan ya juya.


Habib ne ya fito fuskarsa d'auke da tambayoyi kala kala waya ya d'aga ya kira Dad tare da cewa " Dad munzo gidan Abba amma......"

Jiyai Dad ya katseshi yace " Habib meyasa kukaje? Meyasa baka tambayeni ba? Ina Seemah ba abinda ya faru da itadai ko?"

Habib da mamaki yace " Dad menene kake kokarin boyemin? Yaza'ai kace meyasa mukazo gun Abba?"


Dad kam duk ya rud'e yace " Habib, Seemah fa? Is she alright? "


Habib yace eh tare da kashe wayar, meke faruwa?











? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


*Bang=?+?*

*Bang=?+?*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 2? 3?




Nan ya fara nuna mata yanda ake tuki, tafara ja sunayi suna kallan juna wani so ne ke kara ratsa dukansu, bayan sun gama suka fito waje, Seemah ta hau saman bayan mota Jalal ya tsaya a gabanta ta kalleshi tace " wani irin farin cike ne ke ratsani Deen."

Kallanta yai cikin so sai dai kafin yai magana wayarsa tai kara yacirota, yana dubawa yaga Abbansa hakan yasa yad'an matsa kad'an da Seemah, bayan sun gaisa ne Abba yace " Zaka shigo wannan weekend d'in?" Kallan Seemah yai sannan yace " Wlh Abba bansanj ba tukun na ya jikin Zaheeda?"

Abba yace " Da sauki dama zancen kai kudin ka ne, a cikin kud'in da kake turowa akwai ragowa ina ganin ya kamata mukai karshen satin nan." Jalal jiyai kamar an d'au bokitin ruwan sanyi an shekamai a jiki, dakyar ya daure yace kud'i kuma Abba? Da wuri haka? Yad'an kara matsawa hakan yasa Seemah hankalinta ya gaza kwanciya, saukowa tai tare da zuwa ta bayanshi kad'an.
Abba yace " Jalal me za'a jira to? Munada d'akuna dayawa kasani Zainab ba irin yan matan zamani bace da zatace sai kaza take so,to me zamu jira?"

Idan Jalal ya kad'a yace " Amma Abba ita Zainab d'in ta fad'a tana so nane? Karfa ayi abinda bazaiyi dad'i ba, d'an Allah Abba a d'an tsagaita maganar kai kud'in ka ga........"

Abba ya katseshi yace "Jalal anya zaman Abujan nan bai fara lalatamaka dab'iun ka ba? Ka tab'amin musu akan al'amuran dana yanke a kanka? Yau kai ne da kanka?"


Ajiyar zuciya Jalal yai zuciyarshi tai ba dadi yace " Abba ba haka bane kayi hakuri d'an Allah." Katse wayar Abba yai Jalal yanata Hello hello jin shiru yasa ya duba wayar, gaba d'aya jiyai jikinsa ba dad'i juyowa yai da niyyar ganin Seemah sai dai a bayanshi ya ganta idanunta taf da kwalla da sauri ta juya zata wuce, hannu yasa da sauri ya riko hannunta, tana tsaye batare da ta juya ba sai dai hawaye a hankali suka fara sauka daga idanunta, Jalal ne ya matso ta gabanta tare da kallan fuskarta, da sauri tai kasa da ido tana hawaye jikimshi ya karayin sanyi, dakyar ya daure tare da jan hannunta suka fara tafiya, gun zamanta ya bud'e mata ta shiga shikuma ya tsugunna daga setin kafafunta hanayensu na rik'e, yadaure yace " Meemah kinji komai?"
Kallansa tai da raunanan idanunta hawaye suka zubo ta luntse ido tare da had'iyar wani abu tace " Deen aure za'a maka?"

Shiru yai baice komai ba tace " dama a can England ana yawan cewa First love bai fiya kai mutum ga aure ba, Deen ban tab'a soyayya ba sai akanka, na d'ade da fara sanka amma sai yau Allah yai zamu fad'ama juna sirrin zuciyoyin mu ashe yau ne kuma rana ta karshe da......." da sauri yakai yatsarsa bakinta yace shiiiiiii Meemah don't say something like that. "



Kallansa tai hawaye nakara bin kuncinta hannu yasa yana share mata yana cewa " Meemah iyayen na ke san auramin ita, kuma bansan yanda zanyi in hana ba, d'an haka na taso ban iya musu ga mahaifina ba."


Hannunsa dake kan kuncinta yana goge mata hawaye ta rik'e kallanta yai da mamaki tace " Deen please don't live?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? me."

D'ayan hannunsa yasa ya kara damke hannun nasu yace " I won't live you Meemah, but ke kina tunanin za'a barki ki aureni?" Kallansa tai tace "menene da kai? Ni komai yamin naka."

Dariya yai yace "ba wannan ba, kinsan dai duniyar da nake ciki da wacce kuke ciki va d'aya bace."


Tace" Duk abinda nace inaso ahi akemin a gidan mu so karka damu da wannan, kai nake so ba wani abu naka ba."

Murmushi ya saki sai kuma ta fizge hannunta tare da hard'e su, ya kalleta yace " lafiya?" Tace " ba dai auran waccen zakai ba sai kuma kai tunani kara aure na ba?" Kallanta kawai yake yana mamakin kalamanta tacigaba" Jal nifa a tarihin rayuwata babu raba miji."

Kallanta yai ya guntse dariyar dake neman fitowa ya mik'e tsaye tare da cewa " Shikena da na d'auka ko mata uku gareni tunda muna san juna ba wani abun bane amma yanzu na gane." Yai maganar fuska a had'e.

Seemah ta kalleshi tace uku? Da sauri ta fara waige waige Jalal ya kalleta da mamaki wani shago taganu daga nesa da sauri ta fara tafiya, Jalal yasha gabanta yace ina kuma zaki? Bata mai magana ba kawai nunamai shagon tai, yace me kikeso? Alama tamai da ruwa, yace koma bari in siyo, nan ya karasa yace abashi robar ruwa, nan mai shagon yace naira 100, Jalal ya zaro ido yace ya pure water naira 5 shikuma wannan har 100? Mai shagon ya kalleshi da mamaki, wallet d'insa ya d'auko 200 ne a ciki ya mika tare da ansar ruwan, ya juya yana zuwa ya mika kata, ansa tai tasha sannan ta mikamai tace kuskure bakinka, yace bangane ba? Cikin shagwab'a tace nidai ka kuskure bakinka banasan tuna kalamanka dakai na mata uku.

Dariya ce ta kamashi yace " haka kike da kishi? Tace ba kishi bane ba amma ai......... Dariya yasa tare da girgiza kai, komawa yai mazaunin driver yace " Yamma ta farayi kar a nemiki a gida."

Juya kai tai tana kallan window, Jalal yai murmushi ya tada mota, sun fara tafiya ya sa hannu ya anshi ruwab hannunta ya sha, kallobta bishi dashi tace "cewa fanai ka kuskure baki ba fa ka shanye maganarka ba." Kallan bakin jarkar yai saitin inda shatin jambakinta yake nan ya kara kafa rubar yasha tare da sakin wani murmushi shikanshi mamakin kansa yakeyi.

Fizge robar tai tace " bazaka amsamin ba?" Kallanta yai kad'an sannan ya maida kallansa zuwa titi baice komai ba.


Tafiya suka cigaba ba tare da kowa yayi magana ba haushi ya gama kama Seemah kara ta saka da sauri Jalal ya kalleta yace " Seemah menene? Da sauri ya gangara gefen titi tare da maida hankalinshi gaba d'aya kanta hannayenta ta sa ta rufe fuskarta, ciki damuwa ta sa hannu ya zare hannun data rufe fuskarta yace " Meemah menene?"

Idanunta a rufe suke yace " wani gurin ne ke miki ciwo?" A hankali ta bud'e idanunta tace" banasab ina maka magana kana k'in bani amsa, it hurt me."


Kallanta yai batare dayace komai ba ya gyara zamanshi tare da fara tuki, kallansa take rai a b'ace jitai yace " Wani sa'in ne bana sanin me zan ce miki, ban tab'a shiga ciki hali irin wannan ba inji wai bansan me zance ba sai a kanki."

Juyowa yai yad'an kalleta sannan yacigaba " Ban tab'ajin irin haka ba a tsawon rayuwata."


Kallansa takeyi jikinta yai sanyi, kalamansa sun tab'ata idanu ta lumshe tare da jingina kai tace " I will take ur word as ni ka fara so a duniya."


Kallan hanya kawai yake yana murmushi itama lumshe ido tai tana murmushi, wani irin so takema Jalal da ko suna tarr jitake tana missing d'insa, zuciyarta na bugawa a duk lokacin dayake kusa da ita, kalamansa kesa zuciyarta da ganganjikinta su yi lum cikin wani shauki, ya zatai in wani abu ya bemi shiga tsakanin............wayar Ammar ce ta katseta, basai ta duba ba d'an ringing d'insa daban ne a wayarta, d'auka kawai tai tare da gyara kwanciyar kanta zuwa kallan Jalal, tace " Yayana ya? Ammar yace " Seemah yanzu Zaid ya kirani wai a lalai shi ya d'auka number kice, murmushi tai tana kallan Jalal tace " Shareshi yaya shi wai a dole sai na bashi number ta shine na bashi ta ka."

Ammar yai Dariya yace " Kai Seemah, me yasa? Bai miki ba?"

Tana kallan Jalal tace " inafa zaimin bayan na riga na kulle zuciyata?bana kuma tunanin wani zai samu damar shiga." Kallanta Jalal yai wani farin ciki ma ratsashi bai tab'a ganin yarinya kamar Seemah wacce bata kunyar kalamanta ba, ko d'an ba anan ta taso ba? Sam bata kunyar fad'ar abinda ke ranta.

Da mamaki Ammar yace kamar ya? Tace " there is something like that. "
Tana kainan tace yaya bye zan k'ira anjima.









? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*





*FIGHTING*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 2? 4?





Sun isa gidan Jalal yai parking a waje sannan ya kalleta yace " zan wuce." Kallansa tai tare da d'aga kai alamar eh, Jalal na fita itama ta fito tare da Kallansa ta baya, sannan tai ajiyar zuciya ta shiga gida, a tsatsaye taga su Farida da Aisha, suna ganinta Farida ta hau cewa Seemah ina kika shiga? Ko kallanta batai ba ta karasa gun Bala ta mik'amai key tace ka shigo min da mota, sannan ta karasa inda suke, tace " sannunku da gida yaya fa?"

Wani kululun takaicine ya kamasu duka, Aisha ta zuciya tace " bakiji tambayarki ake ina kika je ba? Kinsan neman da muka miki ne?"

Wani irin kallo ta watsa mata tare da cewa " ke in kin fita nemanki ake? Me kuka d'aukeni? Jaririya? Ko me? Ko kuwa ban isa in fita ba?" Tana kainan ta kallesu tai ciki, Aisha tai kwafa tace " wlh Auntu na tsani yarinyar nan."

Farida ta bi Seemah da kallo tace " in muka duba kalamanta bata fad'i karya ba, in kika fita ba nemanki akeyi ba, meyasa ita bata isa ta fitaba sai muhau nemanta."

Aisha tai shiru, Farida tace " Aisha na kula Seemah ba yarinyar banza bace kawai yanda zatai responding magana ne bata iya ba, ita kawai abinda ke ranta take fad'a bata damuwa ko kalaman zasu b'atawa wanda aka fad'awa rai."


Aisha ta jinjina kai, nan sukai ciki gani za'a bud'e gate a shigo da mota.



Seemah kam tama shiga a bakin gado ta zauna ranta a b'ace, dasauri tai dialing number Jalal yana d'agawa yai sallama, ajiyar zuciya tai jin muryarsa sai taji duk bakin cikin ya tafi murmushi tai sannan ta katse layin tare da kwanciya ta rungume pillow, wani shaukin so ne ke ratsata, Aisha ce ta shigo tare da kallanta tace "Seemah me kikeyi hakan?" Bud'e idanu tai tace " Bazaki gane ba ko na fad'a miki." Aisha kam ta sani batasan Seemah sai dai wannan hali nata ma birgeta ko anyi fad'a da ita yanzu in har ka mata magana to komai ya wuce.


Zama tai a bakin gadon tace " nakula dai soyayya ke ratsaki." Seemah najin haka ta mik'e tare da cewa kun shirya da saurayin ki? Tagumi tai tace " inafa haryau bansan a ya muke ba." Seemah tai ajiyar zuciya tace a ganinki yana sanki? Aisha tace I can't tell d'an shekara 1 da suka wuce ne ya ganni a hanya yace ya sona, to ni tun daganan muka fara waya, sai dai bai tab'a zuwa inda nake ba sannan ba nemana yake ba.


Seemah ta kalleta tace " Just 4get him, d'an banaji yana sanki ko kuma mayb akwai wacce ya gani yanaso daga baya." Aisha ta kalleta tace " ni kaina inasan in manta dashi sai dai na kasa, amma ke kamar naga kwanan nan kina cikin wani yanayi.


Seemah tai murmushi tare da cewa " wani nake masifar so sai dai ni kaina nasan nafi sanshi." Aisha tace ya akai kika sani?

Seemah ta rufe ido tace " ni bai dameni ba d'an nafi sanshi abinda na damu da sani shine shima yana sona," tai ajiyar zuciya tace "that's all I need. "




Aisha ta kalleta gaskiya wannan boldness na Seemah da kuma halin ko in kula yana birgeta.



Jalal kam ya kwanta bacci sai dai sam ya kasa bacci sai juyi yakeyi shi kad'ai why is he feeling uneasy? ganun abun bazai kare ba yasa ya mik'e ya d'auro alwala tare da fara salolin nafila.





Da safe wajen karfe 10 Seemah dake kwance ta bud'e ido a hankali, sai dai abinda ta gani ne yasa ta kara lumshe ido, DAD ta gani ya na shafa kanta, bayan ta kara bud'e idon tau murmushi tace " Dad I miss u alot." Ita duk ta d'auka mafarki take jitai yace " kin tashi Sweetheart? "

Mik'ewa tai da sauri ta zauna ta zaro ido tace Dad? Dad ya kalleta yace " dafatan Princess d'ina tana lafiya."

Rungumeshi tai tare da cewa Dad yaushe kazo? Ya shafa bayanta yace " nayi missing daughter ta dayawa shiyasa nazo in ganta mukuma tafi tare."


Dagowa tai cikin mamaki tace " Dad satina fa d'aya?"

Dad yace tashi kiyi wanka kiyi breakfast ni zan d'an fita im ma dawo sai muje yawo, murmushi ta saki tare da dunkule hannunta ta bar babbar d'an yatsa tace " Dad u are the best."

Dad ya mik'e tare da cewa sai na dawo tace " ok" shima yace ok.

Farida ya tadda a kasa yace bari in wuce, tace Dad bakai breakfast ba? Yace naci abinci a jirgi zani Suleja ne.


Bayan Dad ya isa Suleja ya fito ya shiga gidansu, Hajiya na zaune a tsakar gida ta baza tagumi yai sallama, tare da shiga amsawa tai tana kallan hanyar kofar.

Dad ya shiga yana cewa " Hajiya meyasa ake barin kofar nan a bud'e." Kallansa tai cikin wani farincikin ganin d'anta shikanshi jira yake yaga ta mike sai dai abinda ya bashi mamaki gani yai ta koma ta had'e fuskarta, shiyasan laifin amma gani yake yanzu ai yaci ace an daina.

Karasawa yai ya zauna a kusa da ita tare da gaisheta, ta amsa fuskarnan a had'e, kofar band'aki aka bud'e mahaifinsa ne ya fito Dad cikin farinciki yace kawo ka fito.

Kawo ya karaso ya zauna Dad ya gaida shi, sai dai kawo bai amsa ba sai fad'a daya biyo baya, Isma'il ni zaka cima mutumci? Har kaine zaka turomin yarinyar nan gidana? Dad ya kalleshi tare da cewa " Kawo naga wai ai yanz....."

Katse shi kawo yai yace " Yanzu me? Ka d'auka zamu manta? Ko kuwa d'an ka raina mu? To wlh bari kaji ko mutuwa nai bana bukatar yarinyar nan ta min zaman makoki."

Dad idanunsa suka kad'a yace " Haba Kawo in muka duba abin nan yarinyar nam ba itace mai laifi ba me ta sani?"


Hajiya ta katseshi" haka zaka ce? Yarinyar da dalilinta ya ruguzamana farinciki, ya sa mukai hijjira daga garin mu, kacemin me? Ba ruwanta?"

Jikin Dad yai mugun sanyi yace " Dan Allah kubar maganar nan."

Kawo ya mik'e cikin fad'a yace " kai wai wani irin mara zuciya ne? Ko kuwa san Fatima ne ya maka yawa? To wlh bari kaji na fad'ama, magana ma sai tazo aure, kai kana tunanin zaka iya boye maganar ne har karshen rayuwar ka?"


Dad ya runtse idanu da karfi, meyasa kowa bazai fahimceshi ba? Suna tunanin abinda ya faru shi bai ji zafin abin bane ko me?




Hajiya tace " sannan kayima yaranka waya su dawo Nigeria na hana zaman kasar wajen, dama d'an kar muga fuskar yarinyar yasa muka ce kabar kasar amma yanzu tunda kai dakanka ka aikota har cikin gidan mu sai ka shirya shirin dawowa, karkuma ka kuskura kamin musu akan maganar nan."



Dad yace " naji zan dawo amma maganar karatun Seemah fa?" Kawo yace " kai wannan ya dama ba mu ba."
Sunyi shiru kafin dad yace
" Dama abinda ya kawoni shine ina tsoron kar Seemah ta iso lokacin

11 / 37