JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   18 / 37

51K to 54K   out of 109.4K words



Duk da Jalal baiji dad'i ba amma sai ya daure yace " ahh ina my cute Meemah ta shiga ne? Wacce kesa mutum dariya ko bai saba ba?"

Murmushi tai tace " let me try."

Yace " amma I want to see you ya za'ai?"


Ajiyar zuciya ta kara saki ta kara rik'e wayar tace " My deen ni kaina inasan ganinka ga ba waya a hanuna, kawai nanda 20mins kazo nan sai in fito."


Ya saki wani sanssanyar murmushi yace " ok see u later."


Tai murmushi tare da katse layin, wani energy ne taji ya zo mata ta mik'e tsaye tare da karasawa bakin toiler d'in da Ammar yake.......










? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*





@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 3? 7?






Seemah ta shiga knocking d'in toilet d'in Ammar na tsaye jikin kofar tunaninsa d'aya ya ya zai kalli Seemah yanzu? A matsayin me? Ganin yaki bud'ewa yasa Seemah ta zame ta tsugunna a jikin kofar tare da cewa a hankali " Yaya nice fa? Nad'auka tsakanina dakai babu 'yar haka, ko me ya faru ya kamata in sani indai har abin ya shafeka."


Ammar shima ya tsugunna a jikin kofar ta ciki yana sauraranta, Seemah tai ajiyar zuciya tare da cewa " yaya please ka bud'e muyi magana? Please? "


Ammar ya motsa baki har zaiyi magana kuma ya fasa, Seemah ganin yayi shiru yasa tace " yaya kasan me? Ni yanzu na daina san Yaya Habib d'an haka mu koma kawai gidan Dad ni dakai muzauna."


Nan ma shiru yai sai dai yanda na kalleshi naga fuskarsa tad'an saki, Seemah tai murmushi sannan ta cigaba " yaya amma in muka koma wazai d'inga mana abinci? Kasan ban iya girki ba."


A hankali murmushi ya bayyana a fuskar Ammar, Tab'e baki tai ta cigaba " yaya nasan dai kaima ba wani abinci ka iya ba, to ya zamuyi?"

Murmushi sosai Ammar yai, jiyai zuciyarshi tayi haske, Seemah kam ganin yak'i kulata yasa ta mik'e tare da cewa " yaya nasan kanaji na amma tunda kak'i kulani, shikenan bari nai tafiyata."

Jin alamun ta mik'e yasa Ammar ya fito daga toilet da sauri, yana zuwa ya rungumeta ta baya, a hankali tace " Yaya?"

" wait for a moment please." Ya fad'a cikin wata murya dayasa Seemah tasha jinin jikinta, Ammar ya dad'e a haka kafin a hankali ya saketa, juyowa tai ta kalleshi tace " Yayana meke damunka wai?"
Murmushi yai tare da cewa Seemah.......wayar sa ce ta katsesu da kara, da sauri Seemah ta d'aga wayar ganin number Jalal, cemata kawai yai yazo, tace ok, sannan ta juyo ta kalli Ammar tace " yaya my Deen yazo bari in d'an fita waje ina zuwa." Bata jira amsarsa ba tai waje da sauri, Ammar ya bita da kallo zuciyarsa ba dad'i.



Seemah kam tana fitowa ta kara kallan inda taga wannan mutumin sai dai ganin ba kowa yasa tai tsaki tare da fita neman inda Jalal yake.


Jalal kam daga nesa ya ganta, murmushi ne ya bayyana a fuskarsa ya bud'e motar ya fita, kansa ya samu da d'aga mata hannu, tana ganinshi itama ta saki murmushi ta karaso a hankali cikin tafiyarta, tana zuwa kusa da shi suka kalli juna suka saki murmushi a tare kana ganinsu kasan suna tsantsar farinciki na ganin juna, Seemah ta kalli Jalal tace " My Deen ya jikin naka?"

Yace " Ahhh!!!! Ni sam na manta ma banda lafiya a jikina."

Da mamaki tace " ban gane ba?"

"Zuciyata tana rashin lafiya wazai damu da ciwon dake gangar jiki?"


Dariya Seemah tasa sannan ta rik'e hab'a tace " tooh? Oh ni? Yaushe my deen yazama malamin kalamai? "

Hararta yai yace " bawani malamin kalamai abinda ke damuna na fad'a"

Zagayawa tai ta shiga mota, shima ya koma ya zauna tare da juyowa yace " ya Ammar d'in?"

Tai ajiyar zuciya tace " I don't know, haryanzu bai cemin komai ba."

Jalal ya d'an matso da fuskarsa kusa da ita yace " ko dai bayasan ya fad'a miki ne? Ko sirri ne?"
Ta murgud'a mai baki tace " ba wani sirri tsakanina da yayana."
Jalal yace " naji, amma meyasami wayarki?"

Ta had'e rai tare da cewa " ba yaya Habib bane ya kwacemin waya."

Jalal ya koma ya zauna jikin kujerar, sannan ya daure yace " because of me?"

Ta kalleshi idanunta suka ciciko, tace " karkadamu Deen komai zai zo da sauki, ni takace, kaji?"

Murmushi yai sannan ya matso tare da d'anjan kumatunta, kai ta karkatar tace " ya kukai a Birnin gwarin?"

Jalal ya kalleta tare da neman zare hannunsa, da sauri ta rik'o hannun sa tare da kura mai ido, murmushi ya kakaro yace " karki damu kinji?"

Daga yanda yai maganar tasan akwai wani abun, sakeshi tai tare da cewa " Deen ina tsoron kar a rabamu da......."

Ya tsarsa yakai bakinta yace " please Meemah karki karasa, ba abinda zai fari sai alkairi."


Hawayen da take boyewa ne suka zubo, yasa hannu ya share mata sannan yace " banasan ind'inga ganin idanun dana fiso a duniya suna zubda hawaye, abin takaicin kuma nine nake sasu zubar da hawayen."


D'agowa tai ta kalleshi tare da girgiza kai, Jalal jiyai kamar shima hawayen zaiyi, da sauri ya bud'e motar ya fita, Seemah ta bishi da kallo, tare da kokarin fita, vibration d'in dataji wayarsa nayi yasa ta kalli wayar *ZAINAB* abinda taga ya fito a jikin wayar kenan kawai sai ta samu kanta da d'aga wayar, Zainab kam kai tsaye tace " yaya ya zakayi? Su Abba fa da gaske suke d'azu ya fita kaiwa abugo Iv na d'aurin aure, da alama next week d'in nan za'a d'aura."

Jikin Seemah ne ya shiga rawa, batasan sanda ta yarda wayar ba, duk bata hankalinta, bud'e kofar tai tafito, Jalal na ganinta ya taho, sai dai ko kallansa batai ba tafiya kawai take, ganin haka yasa Jalal yasha gabanta yace Seemah menene? D'agowa tai ta kalleshi, jitai kamar tasa ihu, matsawa tai gefensa ta cigaba da tafiya, Jalal ya riko hannunta ta baya yace Seemah? Janye hannunta tai kawai tasa gudu ta koma cikin hotel d'in, binta yai da kallo sannan shima yai ciki, sai dai inaa, sam bai ganta ba, securities sukazo sukace ya fita.







Dad ya isa Birnin gwari lafiya, bai sha wahala sosao ba wajen neman gidan, saboda unguwar kusan duk sunsan gidansu Jalal, tunda ya fara shiga lokon da kafa ransa yake a b'ace, mamakinsa amma lalai Jalal d'in nan yagama raina musu hankali, sai ma daya isa gidan, ba gate bane kawai koface ya d'an bubuga jiyai ance ana zuwa, ba'a dad'e ba wata yarinya budurwa sanye da hijabi tazo ta bud'e tare da mai kallan mamaki, sai kuma can tai saurin cewa " ina kwana?"

Lafiya dad ya fad'a tare da cewa nan ne gidansu Jalal? Kai ta d'aga tace " nan ne amma bayanan."

Dad ya kara kallan wajen gidan yace " nasani iyayensa nake nema." Zuciyar zainab ce ta buga, badai laifi yai ba ko? Ahankali tace shigo, Dad yasa kafa cikin gidan, yabi gidan da kallo, Umma ce ta fito tare da cewa sannu da zuwa, ya kalleta yace yauwa, tace shigo, wani kallo yakarama gidan sannan yace
" basai na shiga ba dama zuwa nai akan ku jama d'anku kune, yasan matsayinsa, 'yata Seemah namata miji ya fita daga harkarta tun kafin rai yazo yana b'aci gwara ayi magana a mutunce."

Jikin Umma yai sanyi, tace " bawan Allah kayi hakuri mu kanmu kaga wace mukeso ya aura kuma ma wani satin za'ai auran, d'an haka ka kwantar da hankalinka."


Dad ya matso tare da ajiyema Umma envelope yace " nagode da fahimtarku, ga wannan kyautace ba yawa, ku bawa d'anku shawara d'an masani shine ya makallewa 'yata."

" ka koma d'an kuwa kayi zuwan banza."

Da sauri Dad ya juya jin furucin daga bayansa, juyawa yai ya kalleshi harzai yi magana sai kuma ya kura mata ido sosai, shi kanshi Abba kalansa yakeyi, a hankali Dad ya karaso kusa da Abba, Dad yace " malam kamar na sanka ko?"
Abba shima da mamaki yace " nima kamar na sanka,"

Dad ya d'an juya kai yace ya sunan ka? Da mamaki yace Ahmad.


Idanun Dad ne suka rik'ed'e cikin wani yanayi ya riko wuyan Abba ya jashi zuwa jikin bango, yace Amadu mai shago?


Idanu Abba ya zaro, Umma da zainab mamaki ya kamasu menene hakan.

Cikin tsawa da fad'a Dad yace " Amadu ne? Kai ne?"

Abba ya kara zaro ido yace " Isma'il?"

Matsashi sosai Dad yai har numfashin Abba ya fara rawa, da sauri Umma da zainab suka matso sunamai magana, Dad cikin masifa yace " Amadu? Kaine? Yama za'ai in mantaka? Mutumin dakajazama rayuwata, ka lalatamin rayuwata."


Umma najin haka tafarayin baya baya tana jijiga kai, idanunta na zubar da ruwa, zainab kam ganin yanda Abba yakeshan wahala yasa tai saurin tsugun nawa ta rik'e kafafun Dad.





? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 3? 8?



Dad ganin Abba na kakari yasa ya sakeshi sannan yace " me kakeyi a nan?"

Kafin Abba yai magana Zainab tayi saurin zuwa kusa dashi tace " Abba sannu." Hakan yasa ya gane wato gidan sa ne, cikin tsananin mamaki da takaici Dad yace " Jalal d'anka ne?"

" Eh" zainab ta fad'a sannan ta cigaba" amma malam menene hakan?"


Wani kallo Dad ya mata yace " dama ina 'ya'yan Amadu zasuyi tarbiya? In ba haka ba yaza'ai yarinya dake kid'inga shiga maganar manya?"

Da sauri tai kasa dakai itakanta batasan ya akai tai magana haka ba, jitai Umma tace " Zo ki wuce ciki."

Simi-simi Zainab tai ciki, Abba ya d'ago yace " Isma'il!!!" Dad ya nunashi da yatsa yace " karkaga wai na maka magana ka d'auka wai na yafe maka abinda kamin ne a shekarun baya, Amadu kaine mutum na farko kuma na karshe da bazan tab'a yafema ba, alhakina dama Fatima shine yasa ka kasa ci gaba, kuma wlh kaji na gaya maka kayi gaggawar fad'a ma d'anka ya barmin 'yata tun kafin na aikashi prison. "

Yana kainan Dad yai hanyar waje, Umma ce da sauri ta matso ta tsugunna a bayansa hawaye na zuba a idanunta sosai, tace " Malam d'an Allah kayi hakuri ka yafe mai, na sani......."

Dad bai jira ta karasa ba yasa kai ba bar gidan, yana fita waje ya juyo ya k'ara bugawa gidan kallo, sannan yai gaba.



&&&&&&&&&&&&&&




Jalal kam a waje ya tsaya ya rasa meya faru da Seemah ta canza lokaci guda haka, to amma yazaiyi? Sun hanashi shiga, wayar sa ya d'aga kawai ya k'ira number Ammar sai dai tanata ringing ba'a d'aga ba, cilla wayar yai gefen kujera ya shafi goshinsa tare da cewa Ya Allah!


Seemah kam tana shiga d'akin ta tadda Ammar a tsaye ta jikin window da gudu ta karasa ta rungumeshi ta saki wani irin kuka mai tab'a zuciya, Ammar kamar ta sosa mai inda yake mai kaik'ayi shi kansa so yake yai kuka kamar haka, jiyai idanunsa ya shiga kawo ruwa, d'an kukan gar zuciyarsa yake tab'awa, Sam ya kasa cewa tai shiru sai ma shima kukan da yakeyi, sunfi minti 10 a haka kafin cikin kuka Seemah tace " Yaya ya zanyi?" Ta karasa maganar tare da d'agowa ta kalleshi, ganin yana kuka shima yasa ta shiga girgiza kai tana hawaye tace " yaya me yake damunka please? " hannu yasa ya goge hawayen yace " fad'a kukai da Deen d'in naki?"


Baya ta juya ma Ammar tace " yaya shikenan, rayuwata tazo karshe."


Da sauri Ammar yadawo tagabanta ya rike kafad'arta yace " Seemah me kike fad'a haka?"

Hawayene ya zubo mata tace " yaya aure za'amai nextweek."
Ta karasa maganar da fashewa da wani kuka, Ammar ya kama hannunta ya zaunar a kan gado, sannan shima ya zauna a gefenta ya juyota setinsa yace " Seemah?" Kallansa tai da mamaki jin yanda ya kararra gurin k'iran sunan, yace " Seemah!!" Tace " yaya inaji menene? Ka tsoratani."

Fasa fad'ar abinda yai niyya yai ya wayance da cewa "Seemah ki rage wannan soyayyar da kikema Jalal bana tunanin yana sanki kamar yanda kike sansa."

Hawaye ta share tace " kaima haka kake gani ko yaya? Na sani yaya, nasan nafi sansa akan yadda yake sona, in fad'ama gaskiya yaya ni na fara cewa ma ina sanshi."

Ammar ya juyo ya kalleta, hawayenta suka cigaba da zuba, tace " amma yazanyi yaya? Ina sanshi sosai, kome nakeyi yana raina, in ban ganshi ba ji nake zuciyata kamar zata fashe, in muna tare kuma ji make kamar kar mu rabu."

Tai ajiyar zuciya tace " ya Ammar banaji zan iya rayuwa ba Deen."

Ammar duk da kalamanta sun mai zafi a zuciya amma bai nuna ba murmushi ya kakaro ya matso kusa da ita yace " Seemah yaushe zuciyarki ta kamo haka?" Tace " ban sani ba Ya Ammar ni kaina ban sani ba." Ta karasa tare da sa kuka, jawota yai jikinsa yana shafa bayanta alamun lallashi.




Jalal ya dad'e agun ganin Seemah tak'i fitowa yasa ya juya gidansu Sagir, yai parking motar yashiga gun Sagir, d'akin a bud'e yake sai dai ba kowa a ciki, shiga yai ya hau kan gado ya kwanta tare da d'aura hannayensa akan goshinsa, tunanuka sun mai yawa a hankali hawaye suka ziraro ta gefen idanunsa, sam bai ji sallamar Sagir ba, sai da yaji an dafashi, kallan Sagir yai sannan ya mik'e zaune yace " Sagir ina kaje?"

"Ummanmu ce zasu fita shine na musu sallama"

Jalal yace " Amma bansan sunanan ba dana gaidasu ai."

Dariya Sagir yai yace " kana cikin tension ina zan fad'ama?" Ya cigaba " amma ya? Ka ganta?"

Kai Jalal ya d'aga alamar eh, Sagir yace " Amma kamar baka farin ciki, fad'a kukai?"

Ajiyar zuciya Jalal yai yace " nikaina bansani ba, da alama Seemah hard to get take neman yimin, sai dai ni a wannan lokacin batasan banasan muyi fad'a ba sam d'an ni kad'ai nasan me nake ji."


Sagir ya kwashe da dariya yace " Lalai Mr Romeo."






a&a&a&a&a&a&a&a&a&b&a&b&b&




Habib ya isa Suleja sai dai jikin Hajiya ba dad'i sosai kusa da ita ya zauna, ya kalli Kawo yace mu wuce Abuja kawai kawo a kaita asibiti, kaga Abba da Dad duk suna can, Kawo yace haka ne wannan ma shawara ce.


Hajiya ya kalla ya rik'e hannunta, jiyai itama ta kama hannunsa da karfinta tace " Isma'il bakasan mahaifin yarinyar nan ba kai kanka, taya za'ayi ka nemi had'a zuri'ata da jinin da bamu sani ba."


Idanu Habib ya zare da jin kalamanta ya kalli Kawo a zabure me Hajiya take fad'a? Da sauri kawo ya d'an matsar dashi ya zauna kusa da Hajiya yace " Amina kalle ni nam ba Isma'il bani Habibu ne me kike fad'a haka?"


Jikin Habib ne yafara rawa ya mik'e tsaye a rud'e yace " Kawo me take nufi da kalamanta?"



Kawo ya kalleshi cikin tsoron furucin da Hajiya tai, yanzu me za'a ce?





? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 3? 9?



Habib ya matsa kusa da kawo ya tsugunna agabansa idanunsa sunyi jaaa yace " kawo meke faruwa wai? Nine babban d'a agun mahaifina meyasa zaku d'inga b'oyemin abu? Gaba d'aya kun birkita min lissafi ance ba mahaifiyarmu d'aya da seemah ba? Dad yazo yace wai Ammar ba d'ansa bane, yanzu kuma Hajiya tana maganar ba'asan mahaifinta ba, in maganar mace takeyi da Seemah kenan take, gaba d'aya na kasa fahimtar abinda ke faruwa."


Kawo yai kasa dakai yace " Habibullah maganar da ake b'oyema........"
Amman da Hajiya ta shiga kwarawa ne yasa maganar ta tsaya, gaba d'ayansu suka mik'e suka nufi gun, hajiya amai takeyi sai dai da alama ba komai a cikin ganin yanda take kak'aro aman, Habib da sauri ya d'agowa yace kawo tayani mu kaita mota, nan suka d'auketa d'an ta galabaita sukai mota da ita, kawo ya zuba musu kaya a jaka suka ja gida suka rufe suka shiga mota.


A hanya ba wanda yai magana d'an Hajiya numfashi kawai take saki.



Dad kuwa harya kusa fita daga birnin/gwari wata magana ta Hajiya datamai randa yaje ta fad'o mai, lokacin har yaje fita daga gidan yaji muryar ta tace " Isma'il kasan ma mahaifin yarinyar ne? Itadai bazata tab'a yarda da yarinyar da ba'asan mahaifinta ba."

Tunano kalaman ne da Dad yai yasa ya kalli drivern sa yace mukoma inda muka fito nayi mantuwa.

Nan driver ya juya da kan mota suka koma, Dad sai tunanin abinda yafaru a baya yakeyi, bai tab'a tunanin zai had'u da Amadu ba, abinda yafi d'aure masa kai wai Jalal d'in da Seemah takeso d'ansa ne.

Ya zarfafa cikin tunani bai san ma harsun iso ba, sai da driver d'in yace " Alhaji mun iso. " lungun gidan Dad ya kalla ransa na kara tunzura d'an bakin ciki, haka ya daure ya fito daga mota ya nufi gidan.

Abba kam tun bayan tafiya Dad ya zauna

18 / 37