JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   4 / 37

9K to 12K   out of 109.4K words

macema yarinya."

Dariya tasake yi kad'an tace " in kuma na sake fa? Me zakamin?" Tafad'a tare da matse kafofinta dake d'an rawa.

Ya harareta yace" ko zaki gwada?" Ta murgud'a mai baki tace " oho kuma yau ina tausaya ma dan watan barin aikinka ya kama."

Jalal ya juya yana kallan titi ya zasuyi? Ganin zaman bazai mai amfani ba yasa ya fita tare da fara tsaida motocin da suke wucewa, sai dai abin haushi duk ba wanda ya tsaya kowa wucewa kawai yakeyi.

Seema dake zaune a mota ta makamai harara tace" kalleshi kamar na kwarai, kirjinsa takalla, da sauri tai tsaki tace "irin wad'an nan mutanen nafi tsana a rayuwa ta masu nuna su na Allah ne bayan kuma ba haka bane a ransu."

Jalal ganin abun yaki ci yaki cinyewa gashi magrib har tayi yasa ya dawo mota yai shiru, wayarsa ya d'aga wa zai kira to? Shi duk abokanansa ba wani abota bace ta kud da kud kowa in ya ganshi da yarinyarnan zarginsa zaiyi.

???????????????????????


Habib kam da rana ya k'ira Farida d'an jin lafiyarta, itakam cike da mamaki tace " Seemah ai tun wajen 12 ta taho gunka office." cikin tsananin mamaki yace " Farida mai kike nufi da wannan zancen? Wani irin Seemah tazo? Bayan ni ban ganta ba? Kuma wama zai kawota? D'an nasan bata iya driving ba."

Tsoro yakama Farida tace '"tare suka fita da Aisha bari na kirata inji."
Da sauri Habib ya kashw wayar ya kara k'iran wayar Seemah datun dazu bata dauka ba.

Farida tak'ira Aisha itakam nan ta sanar da duk abinda ya faru.
Farida cikin tsoro ta kashe kafin takira Habib yasake k'iranta, yace " ya sukai?" Cikin tsoro ta shiga fad'amai abinda akai.

Yana gama ji ya kashe wayar tare da jawo coat d'inshi take lankaye, yasa ya fita da sauri, nemanta ya shigayi sai dai abin tambayar? Wanene wanda auka tafi taren? Itadai Aisha batasani ba bare kuma su Habib.

Nan aka sanar da Security's na Company d'in aka shiga nemanta, har police station aka sanar mawa, ganin abun yaki cinyewa yasa aka baza cigiya gidan radio da Tv.



Hmmmmmmm




?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%



Jalal kam kansa ya dafe, can ya juyo ya kalli Seemah dake rik'e da ciki da alama yunwa takeji, shikanshi yunwa yakeji, fita yai daga motar ya rufeta yai d'an dajin, bishiyar mango yagani rigarsa ya cire ta sama ya hau kad'owa, ba laifi ya samo guda 5 sakosu yai a rigarsa ya koma mota, yana zuwa ya mika mata, ta kalleshi tare da hararsa tace " ce maka akai yunwa nake ji?" Kalanta yai yace " im ba yunwa kikeji ba ki barsu."

Yana gama fad'ar hakan ya bud'e mota ya fita, Seemah ta harareshi tare da jawo mango d'in nan ta shiga sha.
Shikam wayarsa ya d'auka ya k'ira Sagir, Sagir na d'agawa yace " Mutumin ina ka shiga?" Jalal yace " ba wannan ba da matsala fa, yarinyar nan fa na tare da ni."

Cikin rashin fahimta Sagir yace wacce? Jalal yace wace nad'auko jiya.
Cikin tsananin mamaki Sagir yace " What? Jalal meke faruwa? Dama kaine wanda kuka fita tare? Kasan yanda ake nemanta kuwa? Jalal in akasan kaine da......."
Katseshi Jalal yai yace " man mota ya kare inaso ka sanar azo a d'auketa ko kai kazo ka d'auketa, nan ya mai kwatance ya kashe wayar.

Sagir yabi wayar da kallo, bai tsaya wani tunani ba ya zari key. ......


Seemah kam sai datasha guda 4 tad'aga na karshen zata sha sai kuma ta kalli Jalal dake tsaye a waje gashi da alama sanyi yakeji yanda taga yana takurewa,zuge glass d'in motar tai tace " ungo na k'oshi? " kallanta yai sannan ya juya kai gefe kamar bai jita ba, tai tsaki tace " mutum sai rainin hankali,"

Komawa tai ta zauna tace oho cikin wa? Can kuma tace ba dai poison yasamin ba? Da sauri ta kalleshi sai kuma tace " ah ai kayan fruit ne" can kuma tace in yai injecting d'in mango d'in fa da poison? Sai kuma tace "kaiii yaushe har ya fita dashi, Can kuma tace wayyo in kuma ya shirya fa? Da sauri ta bud'e motar taje kusa da shi ta mik'amai mango d'in, ya kalleta tare da juya kai, kallansa tai tace " wato magani kasa min na guba ko?" Kallanta yai kamar ya? Ta kara mik'amai tace " sha in gani." Kansa ya kara juyawa sannan ya mik'a mata rigar coat d'insa takalleshi tare da kallan rigar, sai dayai d'an nisa kad'an yace " nafi karfin nasama mutum guba, sannan kisa rigar d' an na tsane inga mace da irin kayan nan tana tallar kanta."

Ha! ha! ha! What? Talla? Leb'enta ta tad'an ciza sannan ta kalli coat d'in.


Mota suka koma ba wanda yai magana can Seemah tace " wai anan kake tunanin zan kwana?" Jalal baiyi magana ba" tace namanta da jakata ne nima ban fito da kud'i ba, bai kulata ba, ganin haka yasa ta mik'amai coat d'insa tace "nima nafi karfin sa wannan rigar."

Baiyi magana ba ya fita ganin kamar mota na nufosu.








By *Ayusher Mohd*
? *NWA*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *Ayusher Mohd*




No 7?


Seemah dake zaune a mota ta bishi da harara. Jalal kam yana ganin motar har tazo kusa dasu ta tsaya, Sagir da sauri ya bud'e motar yazo gun Jalal yace " Jalal tana ina?" Kallansa yai sannan ya kalli motar hakan ya sa Sagir yagane tana motar kenan, da sauri yakarasa motar ya bud'e baya tare da kallanta, ba tantama itace da sauri ya gaida ita, ita kanta kallansa take da mamaki ta amsa tare da tambayar " kai ma accomplice ne?"

Da sauri Sagir yace " a'a Ranki ya dad'e, yanzu ya k'irani na taho, amma ya akai haka?"
Kallansa tai sannan tace " kai waye da zakamin wannan tambayar?" Sagir yace " baki gane ni ba? Secretary d'in yallab'ai ne."

Kallansa tai tare da kauda kai gefe tace " maidani gida."
Da sauri Sagir yace " to ranki ya dad'e yanzu ma kuwa."

Fitowa tai nan taga Jalal a tsaye, ta harareshi tare da kauda kai gefe, Sagir ya kalli Jalal yace mutafi.

Jalal ya kalleshi yace ina? Sagir yace gida mana.

Kallan Seemah yai yace " so kake laifina ya shafeka? Na tab'a 'yar gwal kana tunanin zan bari laifina ya sha feka?"
Sagir yace to yaza'ayi Jalal?

A ranta ta na nata sunan *JALAL* *JALAL* *JALAL*

Jala yace " manka za muyi sharing a motar in yaso sai in maidata da kaina."

Sagir yai shiru amma shikam yasan tabbas da matsala, in har Habib yagansu bayaji Jalal zai tsira da aikinsa.
Seemah ta kalleshi tace " nidai ka barni na tafi, banasan tafiya da kai sai dai in kuma wani abun kake shirin yi min."
Jala ya watsa mata wani kallo yace " ni na ba kaina makulin motarki? Ko kuwa kidnapping d'inki nai? A iya sanina ke da kanki kika shiga mota kika kuma bani makulli, so I don't think kinada hujjar da zaki yanke hukunci akan wannan maganar."


Seemah wani kululun bak'inciki ya kamata ta bugamai wani kallo, wani k'arin bak'incikin kuma ko kallanta baiyi ba magana ma yake da Sagir, jitai kamar tasa ihu d'an bakin ciki.

Shikam sun sa tiyo sun d'an zuk'i man motar Sagir suna gamawa Jalal ya kalli Seemah yace wuce muje ko? Takalleshi tace "in naki shiga fa?" Jalal ya kalleta yace "ko zaki gwada ne kiga abinda zai biyo baya?"

Sagir ya kalli Jalal yace "Jalal ka d'inga hakuri d'an Allah."
Sannan ya kalli Seemah yace " kiyi hakuri ranki ya dad'e haka yake hakuri muke dashi muma."
Jalal ya kalleshi yace " Sagir banaso karkasa yarinya karama ta rainani." Yanakainan ya juya sai dayaje wajen motar yace kizo mu tafi dare na yi.

Sagir ya kalleta yace " kiyi hakuri Madam haka yake, a hak bazaki gane ba amma Jalal mutum ne nagari sosai." Kallansa tai ta tab'a baki wayaga na gari, ju yawatai itama takarasa motar, ta bud'e ta shiga baya.

Jalal ya tada mota ya hau kan titi, sunyi nisa sosai ba wanda yace komai, can Seemah ta d'aure tace " dama d'an kawai ka ci mutuncina ka jani a motar? Ko d'an na cemaka driver?" Jalal yai shiru can yace " tambaya kike?"
Haushi ya kamata tace " ba tambaya nake ba, ina dai tausaya maka ne na shirin dakai ya ruguje."
" Bana tunanin yarinya dake harkin kai matsayin dazaki rugujemin shirina." Ya fad'a yana kallan titi.
Tad'an matso da kanta jikin kujera sannan tace "ina tausaya maka abin da zai faru dakai." Jalal yad' an waigo kad'an yace " bana tunanin kinkai shekaru 20 in case in ma kinkai bana tunanin kin wuce, kinga kuwa baki kai lokacin tausaya ma wani ba sai dai ke atausaya miki."

Turo baki tai kamar tai kuka cikin shagwab'a tace " Wlh kacigaba da abinda kakemin, karkuma kai tunanin tsoro nake ji."

Baisan sanda yad'anyi murmushi ba yace " da alama ke mammah girl ce."
Tanajin haka tai shiru, idanunta suka cika da kwalla, Jalal jin shiru yasa ya cigaba da tuk'insa, anfi minti 5 da maganar jiyai tace " Banda mahaifiya ai, ban ma santa ba zance." Itakanta batasan meyasata fad'amai ba d'an a zahiri ko 'yan skul d'insu basu sani ba.

Shiru yai jikinsa yai sanyi, tausayinta yakamashi da kuma maganar dayai, ya rasa mai zaici, shikanshi mamakin kanshi yai dayaji yace " Bakomai ita dama rayuwa haka take, mutum baya samin komai, Allah yajikanta."

Kallansa tai idanunta taf da kwalla, sun shiga garin Abuja ya kalleta ta madubi yace " kinsan gidan?" tace " bazan gane ba gaskiya ban tab'a zuwa kasar nan ba sai jiya."
Juya kai yai yace " bana tunanin na tambayeki ko kin tab'a zuwa."
Tace " What? Kai wai wani irin mutum ne da ba'a iya maganar mutunci dashi?."
Jalal bai amsa mata ba ya d'aga waya ya kira Sagir nan yamai kwatance, sun kusa isa gidan Jalal ya kalleta ta madubi a ranshi yace da alama bata tab'a shan wahala irin ta yau ba, dan yaga harta fuskarta ta canza.

Ajiyar zuciya yai, shi kanshi yasan yayi laifi, Seemah ce ta katseshi da cewa dafatan ka fahimci kwatancen na gaji da wannan zirga_zirgan.

Jalal ya kalleta yace " to ko ke zaki zo ki jamu?" Tace ni driver ce? In fact ni ko mota ban tab'a tunanin koya ba."

Jalal yace " karki kuskura kisa a ranki wai d'an na ja ki a mota kina baya yana nufin nid'in driver d'inkine, sai dai hakan na nufin banasan zama guri d'aya......."
Katseshi tai tare da murgud'a baki tace " whatever banasan jin komai nidai ka kaini gida."

Jalal yad'anyi murmushi daga gefe sannan yai kwana, suna zuwa kofar gidan yai parking tare da juyowa ya mik'a mata key, ta amsa tare da kallan gidan, jitai yace " badai bakisan inda kika kwana ba?" Hararsa tai tare da d'an murgud'a baki kad'an tace " ce maka akai ban gane ba?"
Kofa ya bud'e batare da ya amsa mata ba ya juya ya fara tafiya, da sauri ta fito tare da cewa *JAL* cike da mamaki ya juyo jal? Meke nan? Daga inda yake yace " Jal? Da wa kike?"
Cikin wata murya tace " bazan iya fad'an sunan duka ba yamin yawa."
Murmushi yai kad'an yace " waya fad'a miki sunana? Kuma ni sunana in baza'a fad'a duka ba banaji zan iya amsawa."

Tad'an tab'e baki tace " ka ce baka da kud'i dame zaka karasa gida to?"

Yace " Don't tell me u are worried about me? "

Tace " wa? Ni? Allah ya sauwake."
Juyawa yai yacigaba da tafiya kawai yasamu kansa da murmushi.
Itama murmushin tai sannan tai knocking. ........

g&g&g&g&g&g&g&g&g&




Habib kam yakasa zaune ya kasa tsaye ko ruwa ya kasa sha masifa kuwa farida harta gaji itada Aisha, kowa yai jugum banda waya ba abinda yakeyi.

Mai gadi na bud'ewa cikin mamaki ya kalleta yace " kamar Hajiya ko?"
Seemah tace nice, nan ya bud'e mata yana cewa ina kika shiga Hajiya sai cigiyarki ake.

Bata amsa mai ba tai cikin gida, tana shiga ta murd'a kofar a hankali, tare da turawa, dukansu sun kurama kofar ido suna san suga wanene, ga mamakinsu Seemah ce ta shigo, da gudu Habib ya karasa cikin tsananin mamaki, yana zuwa ya rungumeta, ya shiga tambayarta Seemah ina kika shiga? Kinsan yanayin da kika sani? D'agowa yai ya kalleta yaganta tana lumshe ido, yace Seema are u alright?

Kafin ya kara cewa wani abun yaga tayi baya luuu ta fad'i.

Farida ta taho da gudu nan suka shiga jijigata, Habib yace a k'ira likita.

Sun kaita d'akin sun kwantar, Aisha taji wayar Seemah na kara, karasawa tai ta d'au wayar gani tai ansa *Special Bros* d'agawa tai jitai ance "Seemah na wato kinzo gun yaya kin manta dani ko?"

Aisha a hankali tace ba ita bace, Ammar da mamaki yace " waye? Ina Seeman?"

Aisha tace "hmm ta shiga toilet zan fad'a mata inta fito."
Yace alright yana kai nan ya kashe wayar.


Aisha tabi wayar da kallo ba shakka anaji da yarinyarnan kod'an yanda taga yaya Habib yayi.











By *AYUSHER MOHD*
? *NWA*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?







Na *AYUSHER MOHD*




NO 9?




Waya ta d'aga ta k'ira Ammar yana d'agawa cikin shagwab'a tace "yaya!!!!"
Cikin rud'ewa ya tambayeta " Seemah menene? Waya tab'amin ke?"
Takara shagwab'ewa tace " yaya an wulakantani yau."
" waya isa ya wulakanta min ke kanwata? Banaji an haifeshi, kinaso yayanki yazo yad'au hukunci?"
Ammar yai maganar cikin b'acin rai.
Seemah tasa dariya tace " Kai yaya ni kainan inajin dad'in kasancewa kanwarka, amma a yau inaji amai uzuri amma in har ya sake zan fad'ama kad'au min mataki."

Shima dariyar yai yace " kin hucce?" D'aga kai tai kamar yana ganinta tace " sosai ma." Hira sukai tayi sai dayaga ta ware sosai sannan sukai sallama.
Murmushi tabi wayar dashi sannan ta koma ta zauna a kan kujera.


Seemah kwafa tai sannan ta leko ta k'ira Sagir, tace zo kasamin number office d'insu abokinka, ta fad'a tana nuna landline na office d'in, Sagir ya karaso ya nuna mata tace tnx, yana fita ta kira number.

Manager d'insu ya d'aga tare da tambaya, Seemah tace " daga office d'in chairman ne, inaso a turomin Jalal yanzun nan." Tana kainan ta kashe.
Cike da mamaki manager d'in yabi wayar da kallo, Jalal?


Jalal kam ya dad'e agun kafin ya d'aure ya sauko, sai dai yana zuwa office d'insu Manager d'in yace " kaikuma ina ka shiga?" Jalal yace na d'an fita ne,
"Kayi sauri ana nemanka a office d'in Chairman." Manager d'in yai maganar yana kallansa.

Gaban Jalal ne ya fad'i sai dai bai bari Manager d'in ya gane ba kawai ya juya ya fita, yana zuwa ya bude kofar tare da kallan Sagir, yace " Ana k'irana ko?" Sagir yace bari in sanar sai ka shiga.
Nan ya mik'e daga mazauninshi yai knocking office d'in, Seemah ta bada izini ya shiga ya sanar mata yazo, tace ya shigo, nan ya juya ya fita.

Kallan Jalal yai yace " ka shiga."

A hankali Jalal ya karasa yai knocking ta bashi izini ya shiga da sallama, Seemah na tsaye jikin window tana kallan waje kallanta yai da mamaki yace " ke kika kirani?" Juyowa tai tare da yin murmushi tace " ayya shikenan ma je ka." Jalal da mamaki ya kalleta bangane ba.

Kallansa tai tace " nace ka tafi na fasa." Cikin b'acin rai ya fito tare da bugo kofar da karfi, ko Sagir bai kallaba ya juya ya fita, yana koma wa office d'insu ya sake had'uwa da Manager a kofar office d'in yace " Jalal kayi sauri Madam tace ka koma."
Jalal ya kalleshi yace " daga gunta fa nake tace in komo." Yace " kayi hakuri ka koma tace lalai kaje yanzu."
Jalal cikin mugun takaici ya koma, yana zuwa ko Sagir bai jira ya neman mai izini ba ya bud'e kofar ya shiga, tana tsaye jikin fridge d'in office d'in tana shan ruwa, ta juyo tace ka koma na fasa, Jalal ya kalleta wani takaici ya kamashi karasawa kusa da ita tare da fizge jarkar ya ajiye sannan cikin b'acin rai ya kalleta yace " am I a joke?"
Kallansa tai tace " bakaga ruwa nake sha ba?"
Jalal ya nunata da yatsa ya kara matsowa kusa da ita yace " bazan d'auki wannan rainin hankalin ba d'an haka don't you dare repeat that to me." Yana gamawa ya juya zai fita.

Hannunshi ta kamo tace " ka manta ni kanwar mai Company d'in ce?"
Yace " if u need respect then act right." Sannan ya juyo yace " Sakeni in tafi ko?"
Tace " waya baka damar tafiya?" Tafad'a tana hararsa.
Ya juya tare da fizge hannunsa sannan yace " ni naba kaina."
Yana kainan ya fita da sauri, kallansa tai da mamaki sai ta sami kanta da sakin wani sansanyar murmushi, sai kuma can tace "Not

4 / 37