JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   24 / 37

69K to 72K   out of 109.4K words

na neman kufce mata, Seemah tasa kanta a jikin gadon ta shiga kuka mai tab'a zuciyar mai sauraro.

Dad kam tunda ta shigo yanajinsu, kawai dai yayi shiru ne, Hajiya tasa hannu ta d'ago fuskar Seemah tare da share mata hawaye.


Sun dad'e a haka kafin Ammar ya shigo da sauri, a firgice yake da alama yad'auka ko Seemah ta gudu me ko wani abun, ganinta kusa da hajiya yasa ya saki nannauyan ajiyar zuciya, Seemah ta kalleshi tare da mik'ewa.

Bayan Sallah asuba su Dad sun tafi massalaci, suna dawowa suka ba kamar yanda suka barta ba, da sauri Dad ya karasa tare da tab'ata sai dai inaaaa.... Allah ya d'auki ran abarsa.



_Allah yasa mu gama da duniya lafiya Amin_


Ba karamin tab'asu tai ba wannan rasuwa, abu goma da ashirin.
Sun dawo dukansu gidan Abba anan aka mata wanka, Seemah ma ta matsa dole itama ta dawo gida.


Jalal kam yana sallar asuba ya wuce tasha, a mota a zaune kawai yake zuciyarsa taf take da tunani kala kala.
Sun isa birnin gwari ya hau mashin ya karasa gida, yana sauka ya tsaya a kofar gidan tare da kwankwasawa, ba'ai minti 2 ba akazo aka bud'e, ga mamakinsa kanwar mamansa ce, tana ganinsa ta saki guda ya shiga tare da cewa " Goggo yaushe kika zo?"

Ai ba gama rufe baki ba yaga 'yan uwan Abba da Umma suna ta fitowa ya kallesu da mamaki yace " toh! Taran me ake haka?"

Goggo ta harareshi tace " Lalai wannan Angon ba kunya, watoma da alama bakasan a taru ayi zumunci a bikinka."

Jalal ya maimaita kalmar Ango?
Umma ce ta fito fuska d'auke da fara'a tace " Jalal me kake a tsaye bazaka shigo ka kwashe gaisuwa ga 'yan uwa ba?"

Ya d'anyi murmushi kad'an sannan ya shiga ya zauna sannan ya fara gaishesu, kowa sai tsokanarsa suke, ya mik'e tare da tambayar Umma ina Abba?, tace " ya fita d'azu zaije siyo kayan abinci." sai alokacin ya kuka da har fenti anyi a gida, badai da gaske suke ba?
Yace "Zaheeda fa?"
Tace " tana d'aki." Nan ya wuce ransa duk a dagule, kusa da Zaheeda ya zauna, ta kalleshi tare damai murmushi yace " Kanwata da alama kina cikin farinciki, ko duk ganin 'yan uwa ne?"

Muryar Umma yaji tace " Dad'i takeji zaka auri 'yar uwarta Zainab."

Jalal ya juyo ya kalli Umma yace " Wai Umma meyasa kuke min haka? Nifa ban d'auka abinnan da gaske kuke yi ba."
Umma ta had'e rai tace " baka sani ba mai ya kawoka to? "
Jalal yad'an furzar da iskar bakinsa yace " Zuwa nai muyi magana da Abba, ni banajin ma zan iya jiranshi ya dawo, Umma kawai fad'amin inda yake."

Umma ta kalleshi tace " Ba dai cewa zakai ya janye auren ba?"

Jalal yad'an juya kai yace " ni auran nan ba'a gabana yakeba Umma, abun da ke damuna yafi karfin wannan auran."

Umma ta kalleshi da mamaki tace " Badai......"
Jalal yai saurin cewa " Umma d'an Allah ina Abba?"
Tace" Yana lambun Basiru."
Jalal ya mik' e tare da kallan Zaheeda sannan ya juya, Umma ta matso kusa dashi tace " Jalal yanaga kamar ka fad'a? Sannan da alama akwai abinda ke damunka naga gaba d'aya fuskarka ta canza."

Kallanta yai sannan ya runtse ido yace " Umma banaso 'yan uwa susan abinda ke damuna shiyasa nake kok'arin b'oyewa kibari inje gun Abba tukun."
Tai ajiyar zuciya tace " to sai ka dawo."


Jalal ya fito, sai tsokanarshi ake, shikam sai yake kawai yake musu, yana fita Goggo ta shigo gun Umma tace " Yaya Habiba nikam kamar Jalal baya farin ciki."
Umma ta kalleta tace " meyasa kikace haka?"
Goggo ta d'an rik'e hab'a tace " gaskiya bama haka Jalal yake ba sam, naga kamar ya canza, halayarsa ma kamar ta canza, Allah dai yasa ba wani abun bane."

Umma ta kalleta sai dai ta kasa bata amsa, Addu'arta d'aya Allah yasa ba zancen nan Jalal zaina Abbansa ba.



Jalal kam kai tsaye Lambun Basiru makocinsu ya isa, yanazuwa Basirun yace " yanzu kuwa yabar nan, ya koma gida."

Jalal ya juya yai hanyar gida, wayarsa ya rik'e wazai k'ira ya tambaya jikin Seemah?
Da sauri ya k'ira Sagir bayan sun gaisa yace "Sagir d'an Allah ka dubomin halinda Seemah ke ciki."
Sagir yace " to, nan sukai sallama."






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 1?




Seemah zaune take kawai, a rakub'e a jikin gado, sai kallan y'an uwa take suna zuwa gaisuwa, sam ko magana batayi bare cin abinci, duk ta rame ta canza a kwana d'aya.
Tana zaune tana jan carbi taji sallama, jin muryar yasa ta d'ago da sauri, Junaid ya kalleta tare da sakar mata murmushi, kuramai ido tai a hankali hawaye suka zubo mata ya matso kusa da ita tare da cewa " Kanwata ai saura kiris in kasa gane ki, wace irin jinya kikai haka?"

Kallansa tai kawai ga mamakinsa sai yaga ta fashe da kuka, kallanta yai da namaki, sai kuma can yace " Seemah mutuwa fa ba'a san a d'inga mata irin wannan kukan, bare Hajiya da batasan kuka addu'a kawai zamu mata."

Seemah ta d'ago a hankali tanasan mai magana, yace " anma wani irin cinwo kikai haka?"

Zahra ce ta shigo ganin Mutum yasa tai kasa dakai tare da gaisheshi, Junaid ya d'ago ya kalleta yace" Badai badai ba?"
D'agowa tai tare da nuna shi tace " yayana?"

Kallanta yai yad'an kanne ido yace " badai badai ba?"
Tace " badai yaya bane wannan?"

Dariya yai yace " na d'auka kin manta inkiyar tamu."
Tai murmushi tare da matsowa tace " yayana yaushe a gari?"
Yace "d'azu na shigo ya hakurin mu?"
Tace " Alhamdulila"
Kallan Seemah yai yace " Kanwata mey........"
Da sauri Zahra ta katseshi tace " tashi yaya muje ka gaida Mamie."
Ya mik'e tare da kallan Seemah, nan sukai waje, Seemah ta share kwalla Allah sarki rayuwa, a da tad'auka 'yan uwanta ne na jini yanzu kuwa ta gane ashe bata da alaka da dukansu, itafa? Inane cibiyarta? Suwaye 'yan uwanta?.



Jalal yayi sa'a a kofar gida yaga Abba, da sauri ya karasa gunsa, Abba ya kalleshi yace " Jalal kai nake jira ai, na shiga ciki aka sanar dani ka iso."
Jalal ya kalli Abba tare da cewa " Ina Kwana?"
Abba ya amsa tare da rik'o hannun Jalal yace " Nagode Jalal da baka bani kunya ba kazo tun kafin ranar bikin, nagode kwarai, Zainab ta koma gidansu acan zasuyi taron su."

Jalal kallan Abba kawai yakeyi, can yace " Abba inada magana mai mahimmanci dakai."
Kallansa Abba yai yace " Jalal wace magana ce haka da bazaka bari sai bayan biki ba?"

Jalal ya girgiza kai yace " Abba banajin zan iya runtsawa sai naji abinda ke faruwa."
Gaban Abba ne ya fad'i ya kalleshi cikin tsoro yace "Jalal me kakesan ji?"
Jalal yai ajiyar zuciya sannan yace " Abba meye tsakaninka da Dad d'in Seemah?"
Da sauri Abba ya juya baya gabansa ya cigaba da fad'uwa, Jalal ya kalleshi sannan ya matso ta gabansa, yace " Abba bai kamata ka cigaba da b'oyemin wani abu ba, me ka musu suka tsaneka haka? Meye tsakanin ka dasu dahar suke tunanin kafisu sannin abinda si basu sani ba?"

Abba ya had'iyi yawu sannan cikin tsoro yace " Jalal banasan maganan nan na kuma hanek da karamin."
Ga mamakin Abba kawai gani yai Jalal ya tsugunna a gabanshi, yace " Abba d'an Allah ka fad'amin bakasan yanda nakeji a zuciya ta bane a wannan lokacin."

Abba yai ajiyar zuciya yace "naji zan sanar dakai abinda yafaru amma da sharad'i sai ka min alkawari."

Zuciyar Jalal ta matsu taji komai yace " na ma Abba koma akan menene."
Abba ya kalleshi idanunsa sunyi ja, yace " tun ranar da Isma'il yazu gidan nan nasan sirrin nan dole ne ya bud'u, in har kuma kanasan insanar dakai sai kamin alkawari tsakaninka da Allah cewar ko menene tsakanin mu bazai hanaka auren Zainab ranar Asabar ba."

Jalal ya d'ago da sauri ya kalli Abba yace "Abba me kake nufi?"
Abba yace" bazan sanar dakai ba har sai ranar da aka d'aura muku aure da Zainab."

Jalal ya mik'e a zabure yace " Abba d'an Allah......"
Abba ya katseshi da cewa " In har kanasan kaji to sai ka jira ranar auranka, alkawari na maka kaima kamin, haka ya kamata mu barshi."

Abba na kainan ya wuce cikin gida, Jalal bai kula bane amma hannun Abba rawa yakeyi.

Jalal ya naushi bango da hannunsa yana huci ya rasa mai zaiyi.
Wayar Sagir ce ta katseshi, ya d'aga da sauri tare da cewa " Sagir ya Seeman?"
Sagir yai shiru, Jalal yace Sagir ya kai shiru?
Sagir yace " Jalal kakarta ta rasu."
Jalal yafara " *Inna lilahi wa ina ilaihi Raji'un*"
Nan ya kashe wayar tare da silalewa ya zauna a dandaryar kasa, hannu biyu yasa ya rufe fuskarsa zuciyarsa na k'una, wani hali Seemah take ciki? Ance in tambayi Abba mahaifinta shikuna yace sai na auri Zainab, idanu ya runste sai ga hawaye sun zubo, Seemah ya zanyi?

Mutane sai wucewa suke suna kallansa.
Ya dad'e a gun kafin ya mik'e ya fara tafiya, wayar Ammar ya d'aure ya k'ira, daga gun Ammar dake zaune gun amsar gaisuwa ganin k'iran Jalal yasa ya mik'e yai gefe tare da d'agawa, Jalal yai sallama Ammar ya amsa, Jalal yace " Ammar ya hakuri? Ya kuma jikin Seemah? Tanacin abinci kuwa?"

Ammar yai shiru can yace" Jalal baka fahimci abinda muke nufi bane? Ko kuwa idanunka ne suka rufe?"
Jalal yai shiru, Ammar ya cigaba " abu d'aya muke buk'ata agunka ka tambayar mana mahaifinka waye mahaifin Seemah shikad'ai mukesan ji daga gareka."yana kai nan ya katse wayar, tare da kasheta gaba d'aya.

Jalal ya samu wani dakali ya zauna kamar maraya, kalaman Ammar kawai yake tunawa........






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 2?

A goggon dake d'aure a hannunsa ya kalla, sannan ya jawo wayarsa dake gefensa, number Seemah ya kurama ido, ya bude gun da nufin aika mata da sako, sai dai sam ya rasa mai ma zai ce mata, a goggon wayar ya kalla karfe 1 na dare, ya runtse ido da nufin yai bacci sai dai inaa, sam ya kasa sai ma wani irin ciwo dakan ke yi masa, zama yai, yaji zaman ba dad'i ya mik'e tsaye can kuma ya kwanta, tunawa yai ashefa daren jiya baccin awa d'aya da rabi ya samu.

Shawara d'aya ya yanke, a yanda yakejin San Seemah a ransa yana tunanin zai iya sadaukar da farincikinsa ita ta samu, indai har auren shi kad'ai ne mafitar da zaisa Seemah ta san mahaifinta ta kuma yi farinciki da ganinsa, to ba shakka zai iyayin abinda ya fi wannan, sannan shi yasani bai isa ya take hukuncin mahaifinsa ba, sai dai a da yaso gwadawa ya rok'eshi akan ya hakura da auran sai dai bukatar Seemah yasa bazai iya tambayar hakan ba.

Ya rik'e kansa dake rad'ad'i tare da rufe ido, ya dad'e yana tunani kala kala kafin Allah ya taimakeshi bacci yai gaba dashi.

Washegari.........

Ranar Alhamis kenan ya kama kwana d'aya da rasuwar Hajiya sannan a d'aya b'angaren kuma yau ne ake shagalin kamun Zainab, sai dai itama Zainab ba wani farin ciki take sosai ba ga kawayenta sai tsokanarta suke, wai basuga tana waya da angon ba bare ma har yazo ganinta, murmushi kawai takeyi a ranta tace " inafa zanganshi bayan ba nice a ransa ba?"

Jalal kam da bacci ya d'aukeshi sai karfe 10 ya tashi, shi kansa yayi mamakin ganin karfe 10, da sauri ya mik'e Alhamdulila yaji ciwon kan ya tafi, ya fad'a toilet yai wanka sannan ya zura kaya ya fito, yayi mamki daya shiga cikin gida ya taddasu suna ta hidimar su ta biki, wasu kuma suna shirin wai tafiya gidansu Amarya, Jalal ya had'e rai sannan karasa ya gaidasu Goggo ta kalleshi tace " Ango anya ma kuwa kaje ganin Amarya?"
Ya d'ago ya kalleta yace " Goggo sai kace ban santa ba? Ganinta kuma name?"
Goggo ta shiga tafa hannu tace "lalai wannan shine bagidajen, kai an fad'ama ko a kauye ana haka ne?tsaya ma anya kuna d'an tab'a wayar nan kaji matsalarta?"

Jalal ya kalleta yace "Goggo kenan, wace matsala zata samu yarinyar dake gidan iyayenta?"
Goggo ta shiga salati sannan tace " oh ni yau me nake ji haka? Ni ko d'akin da aka gyara muku ma banga kaje ka gani ba."

Jalal ya kalleta zaiyi magana karar wayarshi ta katseshi, Manager d'insu ne hakan yasa ya mik'e tare da cema Goggo yana zuwa, yana fita ya d'aga wayar, Manager yacemai "Jakal ya? Ka tura takardar kuwa?"
Jalal yace " oh God wallahi na manta amma bari na musu sending yanzu."
Ran Manager ya b'aci yace " Jalal wai me ke damunka ne? Sam ka daina maida hankali akan aikin ka sannan yanzu kayi tafiya ba rubuto takarda nakasa fahimtar ka yanzu."
Jalal yai kasa dakai baice komai ba, ganin haka yasa Manager ya katse wayar.
Komawa yai kan dakalin kofar gidan ya zauna, Umma ta aiko yazo yaci abinci, ya kalli d'an aiken tare da cewa " banajin yunwa sai dai anjima."
Daga bayama mik'ewa yai ya tafi can bayan gari ya zauna shi kad'ai.



Rana bata karya, a yau ne ranar asabar uku ga mutuwar Hajiya haka kuma a wannan lokacin ne aka gama d'aurama Jalal aure a massalaci, kana ganinsa zakaga ya rame sosai, sannan sam ya canza Umma kam harta gaji da fad'an rashin cin abincinsa, ana gama d'aurin aure ya wuce gida ya shiga d'akinsa, abokai 'yan uwa da iyaye sai cigiyarsa sukeyi a d'au hoto sai dai an nemishi an rasa, shikam yana kwance cikinsa na mai wani irin ciwo, agoggonsa kawai yasa a gaba yana kallo.

'Yan d'aurin aure sun watse, Abba ya taho gida shikanshi farincikinsa ragaggene d'an yana tsoron abinda zai faru a yau tsakaninsa da Jalal.
Yana isa kofar gida kuwa yaga Jalal a tsaye, kallan mamaki yamai yace " Jalal meye hakan? Kasan dole ne a nemeka amma shine kayi tahowarka gida ko?"
Yai kasa da kai yace " Yahkuri Abba banajin dad'i ne."
Abba yamai kallan tausayi duk ya canza, Jalal yace " Abba jiranka nakeyi, akan alk'awarin dakamin."

Abba ya d'ago a tsorace yace "Jalal!!!."
Jalal yace " Abba d'an Allah na rok'eka daka cika alk'awarinka na fad'amin d'in dakace zakai."

Abba yai shiru sannan yace " muje d'akinka."
Nan suka juya suka shiga soro inda d'akin Jalal yake.



A b'angaren Seemah kuwa tunda ta tashi da asuba, taketa maimaita wannan ranar a ranta, lungun gado ta samu ta rakub'e duk yanda Zahra tai da ita inaa abin yaci tura ga maza duk suna gun karb'ar gaisuwa, agoggon hannunta ta cire tare da rungumeshi a kirjinta, idanunta sun kad'a sunyi jaa.
Kalma d'aya ke yawo a ranta " *Deen an d'auramai aure da wata.*"
Daga karshe Zahra da Aisha sai zuba mata ido kawai sukai.



Jalal zaune a kasa, Abba nakan katifarsa dayake kwanciya, Jin kwankwasa kofar yasa Abba yace " Shigo."
Jalal yabi kofar da kallo, Umma ce ta shigo rik"e da tire, da samiru d'aure a kai, ta ajiye a gaban Jalal, Abba yace " Jalal bismilla."
Kallansa Jalal yai yace "Abba amma ni......"
Abba ya katseshi yace " in har kanaso kaji sai kaci abinci, bansan inkaci wannan abincin kuma sanda zaka karacin wani ba."

Jalal ya kalleshi da mamaki, Umma ta zauna a gefen Abba tare da bud'emai kwannon shinkafa da miyar da akai, nan Jalal ya fara cin abinci sai daya cinye tass sannan Abba yace " Habiba kema ki zauna ."
Nan Umma ta zauna Abba ya kalli Jalal cikin tausayawa sannan yafara bashi labari tun daga farko........................
Har sai da yazo kan ranar da Fatima tazo shagonsa, Jalal hawaye kawai yakeyi na tausayawa Fatima.
Abba yai ajiyar zuciya yace " Nafita kiran Isma'il ne a lokacin dana bar d'ana a shagona shida Fatima akan su jira ni, na fito naga maza guda 5 sun nufo shagon, karasawa nai kusa dasu tare da cewa d'an Allah ina sauri ne amma in kunje akwai d'ana a shagon sai ku bashi kud'in.
Sai a lokacin na kuka da kamaf abu suke sha, jin warin abin ma yasa na gane wiwi ce, na d'an ja baya sannan nace " hmm kuyi hakuri nad'auka shagona zaku.
Ogan cikinsu dana kula shi bayashan komai ya matso kusa dani yace " Amadu Tambaya, Fatima wai na shagonka?"
Na kalleshi sai a lokacin na gane Chairman d'in garin mune wanda ake tunanin nad'awa a satin, kuma yaron gidan da Fatima ke aiki, kuma mijin da zata aura nan da kwana biyu. na kalleshi nace " Chairman nemanta kake?"
Yace " Eh yanzu abokaina sukace tun d'azu suka ganta a shagonka." sam har kasan zuciyata na d'auka ko k'iranta ake ko

24 / 37