JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   7 / 37

18K to 21K   out of 109.4K words

ko?"
Da saurin tace " haba yaya ni d'in? Bafa san sa nake ba wlh."
" dagaske kenan akwai wanda kike so?" Ya fad'a yana jiran amsarta.
Tace " wlh yaya a'a kawau bansan meke damuna bane jiya da yau."
Yace " uhmmm kanwata u look suspicious, da alama akwai wani abu a kasa."

Saurin katse labarin tai da cewa yaya ina wannan budurwar ta ka?
yace" Seemah kedai bari ta rainamin hankali ashe bani takeso ba kud'ina takeso, kai mata akwai matsala."
Cike da mamaki Seemah tace " yanzu yaya duk yanda take nuna maka da kulawar datake baka dama ta karya ce?"
Yace " u have to be carful."

Dariya tai tace " ai ni yaya wanda zan aura sai ya bani jinin jikinsa saboda tsabar soyayya sannan sai ya amince akan duk abinda nakeso."

" tab lalai zanso ganin wannan saurayin, da alama Ammar ne zai nemo miki saurayi mai halayyarsa d'an inba wanda yake sanki kamar shi ba banajin zaki samu abinda kikeso."
Turo baki tai tace " Dama ai nasan duk cikinku Ya Ammar yafi sona gashinan ka fad'a da kanka."


Dariya yasa yace " Seemah tun kina karama baki ga yanda yake ji dake ba, sanda kina yarinyafa indai kika zazzabi to shima sai yayi. "

Murmushi tai tace " nima ai shiyasa duk nafi sanshi."

Sun dad'e suna hira kafin suyi sallama, Seemah tabi wayar da kallo number Jalal ta bud'e tace in k'ira? Wata zuciyar tace ki k'ira kice me? Wata kuma tace ki k'ira ko muryarsa kyaji.

Dialing ta d'anna har ya kusa shiga ta kashe da sauri sannan ta bud'e gub text, ta rubuta " me kake yi?" Tana gamawa ta goge ta sake rubuta " Kana office?" Nan ma ta goge ido ta rufe tace " what should I do?" Kara d'aga wayar tai tasa " kana ina?"
Bata sani ba hannunta yai sending ihu tasa tara da danne kanta da pillow tace ya zanyi, me zai ce.

Jalal ya fito zaije masallaci yaji text ya shigo da mamaki ya kalli number sannan ya bud'e text d'in, tambayar ta d'aure mai kai dialing d'in number yai

Seemah najin ringing takalli wayar sai datai ta ajiyar zuciya tare da furzar da iska tana cewa Cool Down kafin ta d'aga wayar, Jalal da mamaki yace " Waye? Kuma bangane tambayar inda ta dosa ba??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????."

Cikin takaici Seemah ma tace " waye ban gane maganar da kake yi ba, kasan number daka k'ira dai ko."

Jalal yai murmushi yace " Au kece?"
Tace " nice sai me? Karkuma kai tunanin na tambayeka ne saboda wani abun ko na damu naji kana ina, na tambayeka ne d'an ina wani guri so nake ka maidani gida."

Kai ya girgiza sannan yai murmushi yace " da alama dai damuwar ki kai dani, tunda a tunanina dai ban tambayeki ba."

Mik'ewa tai tsaye tace " inji wa? Ni na damu dakai? Ha ha ha, ko a mafarkina."

Murmushi kawai yakeyi tana gamawa wata dabara ce ta fad'omai yace " au to shikenan dama na d'auka kin damu danine yasa kika k'ira har zanyi tunanin k'iranki nima akai akai amma tunda ba haka bane shikenan."

Da sauri tace " a'a ba cewa nai bandamu dakai ba gaba d'aya amma da gaske ne zaka d'inga k'irana?"

" zancen k'ira kuma ai ya roshe tunda ba damuwa kikai dani ba, sai anjima." Yana kai nan ya katse layim tare da sakin wani sansanyan murmushi yace " yarinta ke d'ibanta ko gatane ya mata yawa?"





Seemah kam wayar tabi da kallo tare da fad'awa gado rigim kamar wacce ta suma a hankali tace " shikenan na bada kaina, dama ya rainani gashi na kara bada wata kofar." Sai kuma tai shiru can ta mik'e zaune tare da d'aura pillow akan cinyarta tace amma shima menene namin wannan tambayar?

Juyawa tai kawai taga Jalal a tsaye ya juya baya sai kuma ya juyo cikin salon soyayya yace " saboda naga kin damu dani."
Kwanciya takara yi ta rufe kanta cikin bargo tana cewa No! No! No!...........


Jitai an yaye bargon kad'an Aunty farida ta gani kallanta tai kamar me bacci tace " ya akai Aunty?" Farida tace " Bake bace dama? Inatajin ana kamar magana ne nama d'auka kece."

Jan bargon ta sakeyi tace bani bace.
Farida ta fita tana mamaki to daga inane?






? *NWA*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 1? 5?



*_Washegari_*
Habib ya nutsu a office yana aiki, wayar Dad ce ta shigo da sauri ya d'auka tare da gaidashi, Dad yace " kunje Sulejan?"
Munje d'azu Habib yai maganar cikin damuwa, cikin tsananin tsoron abunda zai faru Dad yace "ba dai abinda ya faru a can d'in ko?"

Habib najin haka yace " Dad ka fad'amin gaskiya kama su Hajiya laifine? Ko Seemah ce ta musu?" Jikin Dad yai sanyi abinda yake tsoro kenan shiyasa ya hanata zuwa kasar cikin sanyin murya yace " zanzo nan da 2wks amma karka fad'ama Seemah zanzo inje Sulejan sannan sai mu dawo da ita.

Kafin Habib ya kara wata maganar Dad ya katse layin, da mamaki yabi wayar da kallo, meke nan?


Seemah kam tun safe take a kwance akan gado ta kasa tashi, tanaji Aisha ta tafi skul, Aunty Farida ma tace zata fita daga nan zata duba ko an gama d'inkinta, itakam tana cikin bargo banda san ganin Jalal ba abinda ke damunta, ganin abin bazai cinyeba yasa ta mik'e da sauri ta fad'a toilet tai wanka, kayan Aisha ta duba ta d'auko wani had'aden material dinkin yayi kyau sosai ta saka sannan ta d'aura d'ankwali simple taduba mayafin daya shiga da kayan tasa ta fito, a waje taga Bala suna hira da nai gadi tace " Bala kaini gun Yaya."
Nan suka mik'e suka fito, Suna isa ta kalli Bala tace ka hau taxi ka koma gida kabani key d'in akwai wanda zai maidani." Da mamaki ya kalleta alamun tsoro ya bayyana a fuskarsa yace " Hajiya ai......" katseshi tai dacewa kuma karka fad'awa kowa inda nake zan koma gida da wuri.
Ta amshi key d'in tare da mik'amai 500naira tai ciki.

Inda suka had'u jiya tai tana shiga elevator ta d'aga waya tama Jalal text " Rooftop. "
Jalal dake zaune suna meeting na sabon project d'in da zasuyi jin karar text yasa ya d'aga waya yana gama karantawa ya d'ago suka cigaba da meeting d'insu.

Seemah kam ganin har minti 10 bai zoba yasa ta kara mai text tace "inajira fa." Jalal ya karanta text d'in suka cigaba da meeting sai dai wannan karan sam hankalinshi yarabu kashi biyu, yanzu ne yagane waye ke jiransa, manager ya kalleshi yace " Jalal kanaji kuwa naji kayi shiru bayan kaike bayani tundazo."

Kallansa yai yace sry mu cigaba, nan suka cigaba sai dai yanzun ma yana yi yana kallan wayarsa, ganin hankalinsa ya ki kwanciya yasa ya kalli Manager yace " please ina zuwa."
Yana fad'ar haka yai waje da sauri, ido suka bishi dashi suna mamakin yau Jalal ne ke neman excuse ana meeting?




Jalal kam da sauri shima ya nemi elevator ya hau yana tsayawa ya fito da sauri tare da karasawa kusa da kofar, sai dayad'an tsaya kad'an kafin ya bud'e kofar a hankali, sai dai yaga wayam ba kowa, cike da mamakin ko harta tafi, ya shiga ciki yana fubawa, a zaune ya ganta akan d'an karamin baranda d'in da akai agun ta sa kanta a cinya, ji take kamar tasa ihu, kamar ita ace tazo neman Jalal amma ya shareta?

Kallanta Jalal yai tare da jingina da bango idanunsa na kanta, Shi kansa baisan tunanin me yakeyi ba, Seemah kam ganin ba ha za yasa ta mik'e da niyyar tafiya tana d'agowa tayi arba da kafar mutum daga d'an nesa kad'an da ita kallansa tafara daga kafa ahankali takai kan fuskarsa zuciyarta nata harbawa, tana kallan kwayar idanunsa ta lumshe ido ya d'auka ko shirmen da takeyi ne na ganinsa, karkatar da kai Jalal yai tare da cewa " kin k'irani kuma bakice komai ba."
Idanu ta zaro a ranta tace dama shine? Hancinta tad'an ja da hannu kamar me mura tad'an juya kai tace ka ga dama kazo? Dana d'auka bazaka zo ba ai.

Kai Jalal yad'an jinjina yace " alright tinda bakiso nazo ba bari na juya." Ya fad'a tare da yin kamar zai tafi, da sauri tace " ina kuma zaka?" Juyowa yai tare da had'e rai yace " inda na baro mana."

Cikin wani salo da ita kanta bata san ta iya ba tace " karka tafi plz."

Kallanta yai cike da mamaki me take nufi? Karasowa yai kusa da ita sannan ya zauna kusa da ita kad'an yace " me kike nufi da kar in tafi?"

Kallansa tai sannan ta juya ta kalli gabanta tace " banda abokin hira so nake muyi hira da kai."

Murmushi ya saki yace " ni abokin hirar ki ne? Ko kim manta ke kikace ba'a iya hira dani?"
Baki tad'an turo tace " ai dagaskene wani sa'in ko wace magana zaka fad'a sai ka fad'i wacce zata kona ran mutum. "

Yace " Ahhh tunda haka ne mai kuma zai sa a nemi yin hira dani?"

Ta kalleshi tace wannan kuma ai........sai kuma tai shiru, fuskarsa ya karkato inda take yace " wannan kuma me?"
Da sauri tasa hannu ta rife fuskar ta tace " yaushe kake tafiya gun matarka?"

Dariya yad'anyi kad'an yace " me kika gani?"

Ta sauke hannunta tare da cewa " nasan dai kamar ba a nan suke ba ko? Amma ka dad'e dayin auren ne?"

Ajiyar zuciya Jalal yai yace" banajin yazama dole in sanar dake sirri na."

Hararsa tai cikin jin haushi tace " rike zancenka banamaso." Tafad'a tare da juya baya tacigaba" laifinane ma dana kawo kaina."
Mik'ewa yai yace " bari in tafi naga kamar fad'a kike ji, bana tunanin da bakina na tab'a ce miki inada aure." Ya juya ya fara tafiya da sauri ta mik'e tasha gabansa tace " me kace? Banji da kyau ba."

Jalal ya kalleta yace " amma ke yarinyace sosai ko?"
Tace " me ka gani?" Yace " me kika gani kika ce inada aure? Bayan bana tunanin na tab'a fad'amiki hakan da kaina?


Ta harde hannu tace hmm ni bansan ya ake gane mai aure ba sannan naga bakafi sa'an yaya Ammar ba to naji a Nigeria da wuri akema mutum aure shiyasa nai tunanin haka.


Dariya yad'anyi kad'an hakwaransa suka fito yace " a da kenan ko? Mu ma yanzu ba kowa bane ke aure da wuri."

Murmushi ta saki ganin ta kasa rufe baki yasa Jalal yace " menene na farin ciki d'an banida aure?" Juya mai baya tai takarayin murmushi itakanta takasa controlling d'in kanta Jalal ya dawo ta gabanta tare da matso da fuskarsa saitin idanunta ta zaro ido tare da d'anyi baya ya kara kallanta sannan ya d'aga yad'an kalli kefen fuskarta yace " Don't tell me you. ..?"
Da sauri cikin rawar baki tace " tell you what?" Duk ta rikece ya kara kallanta tare da kankance ido yace " anya?"
Seemah ta kara had'iyar yawo ta girgiza kai tace " anya me? Me kake sakawa a ranka wai?"

Jalal ya nuna ta da yatsa sannan yace " u? Sannan ya nuna kansa yace me?"


Seemah ta shiga hura iska tace " bafa haka bane kadaina wannan tunanin."

" u look suspicious, badai abinda nake tunani gaskiga bane?"

Saurin juyawa tai tare da tsugun nawa ta toshe kunnenta da hannuwanta biyu, Jalal yai murmushi sannan ya tsuguna kusa da ita yace " a bar maganar nima naga kamar it doesn't make sense."
D'agowa tai tace " ko? Ka gani kaima ko?"

Ya d'aga kai alamar eh yace " bari na koma office."

Seemah ta kalleshi tace " zuwa naifa in ka gama abinda kake ka kaini inga gari." Kallan daya mata ne yasa tace " Please." Murmushi yai yace " shikenan bari inje in dawo ki jirani a nan.

Itama murmushi tai tace to.


Mik'ewa yai ya fito, sai dai har ya isa office murmushi bai bar fuskarsa ba.





? *NWA*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MOHD*




No. 1? 1?





Bai sake kulata ba har suka isa gida, mai gadi ya bud'e gate kallanta yai yace " a nan za'a bar motar?" Kai ta d'aga hakan yasa ya shiga da motar, yai parking, kallansa tai tace " mezance? Godiya zanyi ko me?"
Jalal yad'an matso kusa da ita sosai, ya kai bakinshi kefen kunnenta a hankali yace " ki rik'e godiyar ki ko rashin ta, ki kama hanya ki kwashi kayanki d'an banaji ko tsinke zan d'aukar miki." Juyo da fuskarta tai ta kalleshi sai kuma ta saki murmushi tace " na hutasheka ko ka manta munada masu gadi da masu aiki a gidan, kai dai nake tunani ko kanada kud'in da zai maidakai."
Tana kainan ta juya da niyyar bud'e kofa, hannunta Jalal ya fizgo ta koma ta zauna tare da juyowa, Jalal yace " me kika ce?" Seemah tad'anyi shiru kawai tana kallanshi, fuskarnan tasa a had'e haka kawai sai taji ba dad'i rau rau tai da ido tace " Jal jiya ka banni da yunwa da wahala yau kuma hannuna kakesan b'alawa? Da alama yau ne rana ta karshe dazan yi amfani da hannun, oh ni Allah sarki ni."

Yanda tai maganar ne yasa Jalal ya saki hannunta da sauri yace "haka ake b'alla hannu a garin ku?"
Hannunta ta kalla tare da langwab'ewa tace " shikenan hannuna....." da sauri Jalal yad'an tab'a hannu kara tasa kad'an tace " Jal hannuna......" rud'ewa yai sosai yace menene? Da gaske ciwo yake?

Dariya sosak Seemah tasa tace " amma kanada saurin shiga." Kallanta yai shima baisan sanda yasa dariya ba, yace amma wlh yarinyar......bakinshi tai saurin toshewa da hannunta tace " basai ka karasa ba."

Hannu yasa ya ture hannunta sannan yakara yin dariya tare da girgiza kai....kallansa kawai Seemah take ta karkatar dakai tana murmushi.

Jalal ya kalleta sannan yace " Na tafi." Ya fad'a tare da bud'e kofa, itama da sauri ta bud'e kofar ta d'aura kanta a saman mota tace " Sai yaushe kuma?" Tsayawa yai tare da juyowa ya kalleta yace " Saurayin ki ne ni da zaki tambayeni sai yaushe?" Da sauri ta d'auke kanta sannan tai d'an juya kai tace " ce maka akai haka nake nufi?" Murmushi yai yace " bari na turo miki mai gadin dan da alama baisan kinada kaya ba."
Yana kainan ya cigaba da tafiya, Seemah ta bi bayanshi da kallo har ya fita, a jiyar zuciya tai tare da cewa " not bad."
Mai gadi ne ya karaso tare da kwasar kayan, Seemah tai ciki da sauri, jin gidan shiru yasa tai d'akinta.

A kwance ta taradda Aisha da alama waya take kallanta tai taga yanda ta wani shige bargo tana wani kashe murya, Seemah tai tsaki sannan ta yau gado ta kwanta tare da rik'e wayata da alama game takeyi.

Aisha ce ta taso tazo kusa da ita bayan ta gama wayar tad'an tab'ata, Seemah ta mik'e tare da kallanta tace "lafiya?"
"Seemah d'an Allah inada tambaya, misali saurayinka kullum badai shi ya k'iraka ba sai dai kai ka k'irashi sannan wani sa'in in ka k'irashi ma sai yace yana wani aikin ne zai k'iraka, kuma fa bazai k'iraba, dan Allah me hakan yake nufi?"


Seemah ta mik'e zaune ta kalleta tace " me kuwa yake nufi, banda ke kike sansa ba shi yake sanki ba? Sannan alamace ta yana buk'atar ki barshi ya huta."
Ta mik'e tare da d'aukan towel sai datakai wajen toilet ta juyo ta kalli Aisha tace " narasa meyasa mata bakwa sanin 'yancin kanku, har akwai namijim daya isa ink'irashi ya dizgani haka? Ba'a haifeshi ba." Tana kainan ta bud'e kofar toilet ta shiga.

Aisha ta bita da kallo idanta kamar tai kuka tace " mene? Alamace ta me...? " sai kuma tai kwafa tace " Allah ya nunamin sanda soyayya zata rufe miki ido...

Seemah kam wanka take amma tana mita a ranta.....

?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%?%




Da daddare suna zaune dukansu a falo a na hira Seemah na kusa dasu Ra'is tana koya musu homework, Habib ya kalli Seemah yace " D'azu ba dai abinda ya faru ko?" Tace name fa?
Yace" da kuka fita siyayya, naga kamar guy d'in nan basan zuwa yake ba."
Murmushi ta saki tace " Auu wannan? Ya kula dani yanda ya kamata kuwa, yaya a haka ne zaka ganshi kamar mara kirki amma a zahiri he is not a bad guy."
Habib da mamaki ya kalleta yace " ya akai kika sani? Bayan a tunanina yau ce had'uwar ku ta biyu?"

Da sauri tai kasa da kai tace " hmm kawai nima yau d'in ne naga kamar......."
Farida ce ta katseta tace " kodai kanwata ta fara san wa..........

Cikin wani irin tsawa Habib yace " banasan haka Farida, ke meyasa sai ana maganar mutunci sai

7 / 37