JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   30 / 37

87K to 90K   out of 109.4K words

harabar gidan ne ya kalleshi da mamaki ya taso yazo kusa dashi, hannu ya mik'amai suka gaisa, Ammar yace " wa kake ne....."
Kamar Jalal dake d'auke a fuskar Abba ne yasa Ammar kasa karasawa, A ba yai d'an murmushin yak'e yace " Isma'il nanan kuwa bawan Allah?"

Ammar ya kara kallansa yace " yana ciki anma....."
Abba ya katseshi da cewa " Amadu sunana mahaifin Jalal."
Da sauri Ammar yai baya cikin mamaki yake kallansa, Abba yai murmushi yace " Ka ganeni kenan d'an saurayi, da gani kai sa'an Jalal ne nasan bazai wuce Ammar ba ko?"

Ammar ya kalleshi idanunsa sunyu jaa, Abba yai jinjina kai cikin kalar tausayi yace " ga kamanan ai nagani."
Ammar ya daure dakyar yace " muje yana ciki."

Abba ya gyad'a kai sannan yabi bayanshi.

Sun isa kofar falon, Ammar ya kwankwasa, Abba, kawu, Dad, da Habib suna zaune suna hirar yanda suke tunanin auren zai kasance, jin kwankwasa kofa yasa suka maida hankalinsu kan kofar.

A hankali Ammar ya murd'a kofar ya shigo, kallanshi sukai sai dai gani sukai shima yana kallan kofa, hakan yasa suka maida hankalinsu kan kofar d'an da alama wanine zai shigo.

Abba ne ya matso a hankali kansa a kasa, Dad ya kura masa ido, gani sukai Dad ya mik'e cikin b'acin rai ya nuna Abba yace " Amadu me kakeyi anan?"

Abba ya d'ago idanunsa da suka ciciko, Abban Zaid ma ya mik'e a zuciye yace " kai ko kunya bakaji ba ka zo gidan nan?"

Abba cikin wata murya yace " Ku bani izinin shigowa dan Allah."
Dad zaiyi magana kawu ya katseshi da cewa "ya isa haka, bakon mu ne bako kuwa ku menene ba'a wulakantashi."
Kawu ya kalli Abba yace shigo ko?
Jiki a sanyaye Abba ya shiga gwiwowinsa ya sa a kasa ya sadda kansa kasa, duk yanda yaso ya b'oye hawayensa sai da suka zubo ya share tare da d'agowa ya kalli Dad yace " Isma'il na fi kowa sanin yanda ka tsaneni haka kuma nafi kowa sanin dalilin tsanar dakamin, naci amanarka na kuma yaudareka, nasakaka a kuncin rayuwar da duk farin cikin da kake ciki bazai d'aikema wancan bakin cikin ba."

Ya goge hawayen dake zubo mai yacigaba " Na rok'eka ka yafemin ba wai dan ni ba sai d'an darajar ma'akinmu, Isma'il naga ishara kala kala akan cin amanar abotar danai, yarinyata tana kwance ko mek'ewa batayi haka magana tun tana karama take a kwance."
Ya kara goge hawayensa yacigaba " ga yaron da nakeso Jalal san da yakema Seemah ya wuce duk yanda kuke tunani saboda ita ya canza karatunsa sannan mun mai aure amma inaa babu alamar shakuwa ko wani abun tsakaninsu, wannan abun danai yasa d'ana haka cikin yanayin daban tab'a tunani ba sam yadaina farin ciki......."

Kuka ne yaci karfinsa, kowa yai shiru Ammar ya share kwallarsa, Dad kam kansa yai kasa dashi Abba ya d'ago cikin tsananin kalar tausayi yace " Isma'ila ka yafemin ni nasan abinda na gaji tun bayan faruwar abin nan muke cikin rashi mai karfi, Jalal shi yai wahalar karatunsa haka kuma ya taimakemu, sai yanzu da Allah yataimakeshi ya zama wani abun, ka yafemin ko d'ana zai fara aiki cikin sa'a sannan yarinyata ta samu lafiya."

Sunyi shiru kowa ya kasa magana sai dai tausayin Abba ya ratsa kowa, agoggo Abba ya kalla, ganin karfe 2 daidai yasa ya kalli Abban Zaid yace " D'an Allah a kunna tashar Karamci Jalal yace yanada sako mai amfani dazai isar, sannan Seemah ta taimaka itama ta kalla."

Kallan mamaki sukai mai, Habib ya mik'e da kanshi ya kunna sannan ya kalli Ammar yace " ka kira Seemah muga sakon."

Ammar ya juya ya fita.






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 6? 4?


Seemah ta shigo falon itada Ammar da Zaid, kowq ya tattara hankalinsa akan Tv d'an ganin me Jalal ke kokarin isarwa.


A b'angaren Jalal kuwa bayan sun gama shirya komai, Senate Abdul ya shigo cikin isa directors da producers d'in kowa ya fito yana gaidashi, Jalal kam na zaune akan kujerar da zai gabatar da shirin, bayan sun gama gaisawa ne Senate ya kallesu yace " da wa zamu gabatar da shirin ne? Ban samu na ganshi ba."

Abbas ya juya yana neman Jalal can ya hangoshi gaba d'aya ma hankalinsa baya kansu, da karfi yace " Jalal?"
Juyowa yai ya kalleshi, Senate ma ya kalli inda director d'in yake kallo, Jalal ya musu murmushi sannan ya d'aga musu hannu, Senate ya kara kallan Jalal yace " waye shi dabazai zo gaidani ba?"

Abbas yai gyaran murya yace " hmm dashi zaku gabatar da shirin takardun da zakuyi amfani yake dubawa, ai shi haka yake bashi da magana." Abbas kam yai kokari gurin kare Jalal.

Abdul yai murmushin jin dad'i a ransa yace indai bashida magana ai hakan sai yafi dad'in yin shirin.

Kara kallan gun da Jalal yake yai kamar yasan fuskar amma a ina? Watsar da tunanin yai nan ya karasa ya zauna a kujerar dake kallan ta Jalal.
Jalal ya sakar mai murmushi tare da gaidashi, Abdul ya aksa tare da cewa lokaci yayi mu fara? Ina d'an sauri ne.


Jalal ya d'aga kai sannan ya mik'e ya duba komai, sai daya tabbatar komai yayi sannan karfe 2 dot da buga, suka fara gabatar da shirin kamar haka.

Jalal ya gaida mutane sannan ya sanar musu da sabon shirin su na yau da kuma babban bakon da suka gayyata wato *Senate Abdullahi* wanda yake tunanin neman kujerar shigaban kasa.

Bayan Senate ya gaishesu ne shima Jalal ya kalleshi yace " Honourable Senate kayi mukamai da dama tun daga kan Chairman har zuwa matakin da kake yanzu, shin ka tab"a fuskantar wani matsala a harkar siyasarka?"

Senate yai murmushi yace " hmm gaskiya ban tab'a samun matsala ba sai ma kaunar da talakawa ke nunamin inajin dad'i kwarai da yanda suke bani had'in kai."

Jalal yai murmushi yace " Gaskiya ne mutane na sanka, Allah ya kara d'aukaka."
Senate ya amsa da Ameen.

Jalal yace " Yanda mutane kesanka baka tunanin ka tab'a bata ma wani rai ko musgunawa talakawa da saninka ko cikin rashin sani?"
Senate ya had'a hannayensa biyu tare da kara sakin fuska yace " a iya sanina ina kokari gurin kyautatawa talakawa da mutane ina kuma kaunar talakawa kamar yanda nakesan nawa 'yan uwan to menene zaisa ni na wulakantasu? Bayan sun zama jinin jikina."

Jalal ya saki wani mugun murmushi ba shakka wannan mutumin ya iya siyasa Jalal ya cigaba " Gaskiya ne kam kana kokari gurin kyautatawa mutane, sai dai ina fatan Allah yasa yanda kakesan talakawa 'ya'yanka ma su so ka haka."



Gaban Senate ya fad'i me mutumin nan yake nufi? Bai amsa mai ba Jalal yai saurin cewa " yanzu 'ya'yanka nawa?"
Abdul ya kalleshi me ya kawo zancen 'ya'ya nan?
Amma ya daure yace " 'ya'yana uku mata 2 sai namiji yanzu yake primary 6."
Jalal ya jinjina kai yace " Allah sarki, Allah yaraya manasu."

Abdul ya amsa da Ameen.
Jalal ya kalli Camera yace " Kada ku manta kuna tare da babban d'an siyasan nan wanda talakawa ke kaunarsa wato Senate Abdul. "
Nan aka sake nuno Senate yana murmushi.
Jalal ya kalleshi yace " Sanda ka fara siyasa kayi aure ne?"
Abdul ya girgiza kai yace " A'a lokacin dai an kusa yin auren."
Jalal ya jinjina kai yace " munji labarin matar da zaka fara aura Allah baiyi auren tsakaninku da ita ba ko?"
Abdul ya bugama Jalal wani kallo tunawa dayai live ake d'aukansu yasa ya saki murmushi yace " gaskiya ne, matsala aka samu aka fasa auren."


Jalal ya d'an gyad'a kai alamar tausayi yace "Ayya!!! Na tabbata matsalar badaga kai bane."
Abdul ya d'anyi kasa dakai kamar me shirin kuka yace " amanata taci."

A ran Jalal yace " thank God."
Jalal ya kalleshi da mamaki yace " Amana kamar tame fa? Na tabbata masu kallo suna san ji."

Abdul ya had'iyi yawo yace " Amanata taci da wani banasan tuna asiri irin wannan a bainar jama'a."

Jalal yace " gaskiya ne ai tona asiri ma bashi da dad'i sai dai muce Allah ya rufa asiri."

Abdul yace " Ameen."

Jalal ya kalleshi yai murmuaji yace " Yanzu amma nasan ka yafe mata ko?"

Abdul ya kalli Jalal yace " na yafe mata d'an ni mutum ne mai saukin kai banasan kulatar mutum."

Jalal yace " I see, amma shi wanda yaci Amanar taka fa? Kana da wani sako zuwa gareshi ne ko kuwa shima ka yafemai?"

Abdul ransa ya fara b'aci ya kalli Jalal sannan ya daure yace " ba wani sako danake dashi, Amanata ya riga yaci nikuma na yafemai ."

Jalal ya d'an rangwab'ar dakai sanar ya murza ido, yana bud'e idanunsa Abdul yaga idanunsa sun kad'a sunyi Jaa kana ganinsa kasan b'acin rai ne karara a bayyane a idanunsa tsoro ya fara kama Abdul.
Jalal ya kalleshi da jajjayen idanunsa yace " Amma a binciken da mukai sai mukaji kamar fyad'e akama matar da zaka aura?"

Ba Abdul ba hatta ragowar masu recording sai da suka kalli Jalal cikin tsananin mamaki, a falo kuwa gaba d'aya sun kame kallan tv kawai sukeyi.

Abbas ya rasa yanda zaiyi yama Jalal magana tunda dai abin live ne.

Abdul ya kasa magana, Jalal ya d'an murmusa ta gefe yace " Ina mamakin namijin dazai iya yafema wada yama matarsa fyad'e ana saura kwana biyu auransu."

Abdul idanunsa shima suka fara canza kala, tsoro ya fara kamashi, Jalal ya kara wani murmushin yace " gaskiya na jinjina maka ba kowani namiji bane zai iya yafemasa."

Abdul hannunsa ya fara rawa cikin rawar murya yace " haka ne ni amma daga baya nai tunanin rashin d'aukan abin da zafi hakan ne yasa na yafemai."

Jalal ya d'aga kai tare da had'e fuska yace " amma sai naji kamar wanda akace yayi fyad'en shi kuma yace sharri aka mai"

Abdul ya zazzaro idanuwa cikin tsananin tsoro yace " me kake nufi da kalamanka?"
Jalal yai murmushi yace " ni d'an jarida ne ba lawyer ba bincike ba nawa bane sai dai a labarin da mukaji Kamar fyad'an ba shine yai ba sharri akamai, zai iya yiwuwa wanda ya mata sharrin ko bayasan auranka da ita yarinyar ne ko kuma santa yake, ko kuma......"

Jalal yai d'an karamin hucci yace " nayi mamaii a binciken ku da bakuyi bincike ba cikin wannan al'amarin."

Abdul ya mik'e a zuciye yace " me kake nufi? Wani nakusa dani ne dan bayasan na aureta ya mata fyad'e ko kuwa so kake ma kace ni na mata gaba d'aya , gayyatata kukai d'an ku wulakantani ko me? a iya sanina Fatima ta rasu, to waye zai ce nine na......."

Murmushin da Jalal ya sakar masa ne yasa yai saurin rufe bakinsa sam yamanga abin live ne, Jalal ya rike baki irin abin mamakin nan yace " badai kaine ka.....ahhh nasan haka bazai faru ba da kaije da tuni ka nemi 'yarka tunda ance har haihuwa tayi sannan da ka sanar damu 'ya'yanka 4 nasan ba kaibane to amma ban fah........"

Abdul ya fusata a zuciye ya d'aga hannu zai wankama Jalal mari, murmushi Jalal ya masa sannan yace " karka bari mutane su fahimci b'oyayen halinka da kake kokarin b'oyewa."

Cikin tsananin takaici da bakin ciki Abdul ya fita.


Jalal ya kalli Camera yace " muna sa ran kuto zatai kokari wajen gano mana gaskiyar wannan al'amarin kar muzu mu zab'i shugaban da ake kokwanto a kansa Bissalam."

Abdul ya fita a zuciye sai dai me? Yana fita zai shiga mota yaga mutane dayawa da ragowar 'yan gidan wasu tv d'in da gidan radio suna juranshi.

Jikinsa ne ya shiga rawa ya kasa tunanin komai...

Seemah kam da gudu ta mik'e tabar falon.






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 6? 5?


Abdul ya kara kallan mutanen a zuciye ya koma ciki, Jalal kam yana ma mutane sallama da kuma sai sun jisu a sabon shiri na gaba kawai yaji an shakumo mai riga, kallan Abdul yai cikin mamaki sam idanun Abdul ya rufe ya manta shiri akeyi kuma live, cikin masifa da bakin ciki yace " kai waye kai? Me na maka ko ince menene tsakanina dakai da zaka aikama ragowar 'yan jaridu dasuzo? Dama can ka shirya ci min mutunci ne bawai shirin mutunci kaso yi ba ko?"

Jalal ya kalleshi yace " Senate me kake yi haka bakaga shiri akeyi ba? Mutane fa suna kallanka."

Cikin masifa yace " da a kalleni da kar a kalleni ai ka riga ka gama cimin mutunci ya fad'a tare da nunamai Jaridar da P.A d'insa ya kawo masa yanzu."

Jalal ya kalli head line d'in inda ya bud'e " *SHIN DA GASKENE SENATE ABDULLAHI BASHI DA HANNU AKAN FYAD'EN DA AKAI?*

Jalal yai murmushi tare da ba masu aikin umarnin su daina d'aukan rahotannin, bayan sun daina Jalal ya kalleshi ya sakar mai wani mugun murmushi yace " Bana tsoronka, ba kuma na tsoron abunda zakamin, ka manta kalamaina lokacin dana je gidanka?"

Abdul ya kalleshi da mamaki "kai ne kaje gidana?"

Jalal ya d'aga mai gira yace " Kayi tunani dakyau, sanda nazoma da zancan 'yarka wani cin mutunci kamin ko ince kama yarinyar da ba ruwanta?"


Nan fa Abdul ya tuno jikinshi ne ya shiga rawa ya sake Jalal yana girgiza kai, kamar zararre.
Jalal yad'an zumburo baki yace " ayya I pity you, gashi yanzu na kai kararka kuto kana zuwa gida zakaga sammaci."


Kai Abdul ya cigaba da girgiza wa yace " karya kake d'an talakawa, ko Amadu bai isa yaja dani ba bare kai, inada arziki da karfin da ba wanda ya isa ya ja dani."

Jalal ya jinjina kai tace " hmm gaskiya ne wannan ni kaina na shaida, sai dai wannan karan dukiyarka da matsayinka bazasuma amfani ba, d'an kuwa al'uma sunga halin da ake ciki kana tunanin wani zai taimaka maka bayan shima yana tsoron kar mutane su tsaneshi irinka?"


Abdul cikin tsananin takaici ya d'aga hannu zai mari Jalal, hannu Jalal yasa ya rik'e hannunsa sannan yamai murmushin rainin hankali yace " wlh wlh kaci darajar jininka ne ke ya wo a jikin Seemah da wlh sai na maka abinda yafi wannan, sai naci ma zarafin da har karshen rayuwarka bazaka manta da abinda kama Fatima, Dad wato Malam Isma'il, Mahaifiyarsu Ammar da kuma Mahaifina Amadu ba da sai na sa ka fisu wulakanta a doron kasar nan."

Abdul ya kalli idanun Jalal yanda sukai jaa, tsoron kalaman Jalal ne ya fara kamashi ya kalli Jalal a tsorace sannan ya fizge hannunsa, Jalal ya had'iye wani abu sannan yace " ka b'atama mutane dayawa rayuwarsu tayaya ma zakayi rayuwa cikin farin ciki? 'Yar ka da batama sanka ba baka tab'a tunanin nemanta ba saboda giyar mulki na d'ibanka."

Harya bud'e baki zai sake magana sai kuma ya fasa ya juya ya fara tafiya, har yad'anyi nisa ya tsaya tare da cewa " sai na ganka a kuto."
Jalal ya wuce su Abbas da duk sukai tsuru tsuru suna kallansu cikin tsoro.


Jalal fita yai direct yahau sabuwar motar daya sa Sagir ya siyomai, kirar Mercedes benz fara tas, gidan su Abba ya wuce.


Sukuwa a b'angarensu Abba jikin kowa yagama yin sanyi, Dad ya share hawayen daya rasa na dadi ne ko name, ya kalli Amadu yace " Amadu a wani dalilin zaka bar Jalal yai wannan abu mai hatsarin gaske? Me kakeyi da bazaka hanashi ba?"

Amadu ya share kwallarsa yace " Isma'il wlh sam bansan me yaron nan yake shirya wa ba nidai kawai cemin yai ince a kunna tv a kuma kira Seemah."


Abban Zaid ya kalli Amadu yace " Abdul bazai bar jalal haka ba, amma dama Abdul shine yama Fatima fyad'e?"

Nan Amadu ya warware musu komai na abinda ya faru.

Sunyi shiru kowa na tunanin mafita, samari 'yan gari kuwa sun fito da sanduna suna zanga zanga a kofar gidan Abdul akan dolene ayi bincike dan suma basu yarda ba.




Jalal kam bayan ya isa gidan yai parking motarsa ya fito, a harabar gidan yaga Zahra da Zaid a tsaye, jiyai Zahra tana cewa " Yaya Zaid kazo ka duba Seemah inajinfa ba lafiya take ba wani abu takeyi kamar ba'a hayacinta take ba."

JALAL ya matso da sauri yace " ina Seeman?"
Zahra ta kalleshi da mamaki, Zaid yace " Jalal zo muje."
Nan sukai d'akin da Seemah ta rufe kanta a ciki, Ammar suka gani a tsaye a kofar yana kwankwasawa tare da kiran sunanta.
Jalal yasha jinin jikinsa, tsayawa yai cak batare da ya karasa ba.
Ammar ya kara buga kofar yace " Seemah meyasa kike min haka? So kike kiga hankalina yayi matukar b'aci ko kuwa?"


A hankali Seemah ta mik'e tazo ta bud'e mai kofa tana bud'ewa ta fad'a jikinsa ta rungumeshi tana wani irin kuka, Ammar ma kwalla ce ta taro mai a ido, yace " Seemah menene? Mahaifin naki ne bakyaso ko kuma nakiso akacimai mutunci ba?"

Kai ta girgiza tace" ni ba mahaifina bane, Dad ne kawai mahaifina, sai dai Ya Ammar nasan mutumin nan, na tab'a ganinshi a hotel d'in daka zauna, yaya bashida mutunci na tsorata da gani mutum irin haka. "

Jalal ya share

30 / 37