JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   27 / 37

78K to 81K   out of 109.4K words

sake ta kuma sake gogewa, tafi hour 1 tana abu d'aya, Zaid ya shigo ya kalleta yace " Seemah albishir?"
Kallansa tai batace komai ba, yace " Jalal yazo yana gunsu Dad gwiwowinsa a kasa."

A zabure ta mik'e ta zauna tare da cewa " Deen?"
Deen?
Deen d'i.....?
Zaid ya d'aga mata kai, fita tai da sauri d'an ko mayafi ta manta bata d'auka ba, sai datakai kusa da falon ta tuna ashe fa sun rabu, hartayi alamar juyawa taji motsin bud'e kofar falon, tsayawa tai cak ta baya gabanta na dukan uku_uku, Jalal shima yana fitowa daga d'an nesa kad'an ya kalleta, gabansa ne ya fad'i a hankali Seemah ta juyo, cikin tsoron wanda zata gani, Jalal ma idanunsa na kanta.

Tana juyowa suka kafe juna da ido, dukansu idanunsu ya ciciko da kwalla, Seemah jitake kamar taje ta rungumeshi, a hankali Jalal ya fara takowa, suna kallan juna, har yazo kusa da ita kad'an, ya fara kokarin maida kwallarsa tare da kakaro murmushi ya rasa me zaice mata, itakam kallansa kawai take.
Can ya dake yace " Long time?"
Ta kalleshi tare da share kwalla tace " ka rame"
Yai murmushi yace " kema."
Ta d'an d'auke idanunta, a hankali yace " bantab'a tunani zan ganki ba."
Ta d'ago ta kalleshi tace " nima bansan ya akai nazo nan ba."
Murmushi mai cike da tausayin juna sukama kansu, ya kalleta yace " an kusa ko?"
Kai ta d'aga mai, yace " Congrats. "
Itama tace " anyi ko?"
Shima kai ya d'aga mata, ta share kwalla tace " I see."
Shiru sukai suna kallan juna can Jalal yace " bakya cin abinci ko?"
Ta kalleshi batace komai ba, yace " do you not resent me?"
D'agowa tai ta kalleshi, ya jinjina kai yace " dole ne ko?"
Kallansa kawai take batace komai ba, yace " bazan nemi yafiyarki yanzu ba, sai na cika alkawarin dana d'auka."
Ta bud'e baki zatai magana, taga Ammar ya fito daga falo, cak ya tsaya daga nesa kawai yana kallansu, itama kallanshi takeyi, hakan yasa Jalal ya juya...........






Ruguntsemi sai ran sallah






? *THE MEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 7?



Jalal ya kalli Ammar sannan ya juyo ya kalli Seemah jikinsa ya kara wani yin sanyi, murmushi yama Seemah sannan a hankali cikin wata murya yace " Nagode Meemah da duk abinda ya faru bai hanaki ganina ba, nagode sosai." Yana kai nan ya fara tafiya ya wuce Seemah, Ammar na tsaye ganin Jalal ya fara tafiya shima jikinsa yai sanyi, har Jalal ya d'an wuceta kad'an Seemah tace "Deen?"
Tsayawa yai cak batare daya juyoba sai idanunsa da suka kara cicikowa, wato haka dama rabuwa take? Seemah ma bata juyaba tace " In ka tafi yanzu shikenan kuma ko?"
Idanu Jalal ya runtse zuciyarshi ta shiga k'una, sai dai ya kasa amsa mata, kuma ya kasa wucewa, Seemah can ta kalli Ammar daya juya baya ta fara takawa ahankali har ta isa inda yake, sannan ta juyo ta kalli Jalal, daidainan shikuma yaji shirun yayi yawa ya juya d'an ya ma ta sallama, gani yai bai ganta ba nan ya shiga dubata, daga nesa ya hangota da Ammar, juyawa yai da sauri d'an zuciyarsa na wani irin zafi, a hankali ya d'inga takawa har ya fita.

Seemah kam Ammar ta kalla tace " Yaya?"
Juyowa yai a hankali d'an baiyi zatan zai jita a kusa ba, ta kalleshi ta mai murmushi tace " Kayi hakuri na........"
Girgiza mata kai yai yace " Kar kice komai, naji dad'i ma da kika fito daga d'aki, d'an nagaji da ganinki kullum a d'akin nan."

Tai kasa dakai tana neman abin cewa can tace " yaya ni ban ma san......."
Hannu yasa akan leb'enta yace " karkice komai."
Ta kalleshi kawai batace komai ba, a hankali tad'an juya baya ta zata yananan, gani tai ba kowa agun, ga mamakinta jitai Ammar yace " Ya tafi."
Da sauri ta kalleshi jikinta yai sanyi tace " nifa ba wanda nake nema."

Yai murmushi yace " nasani, kin tambayeshi mahaifinki?"
Idanunta ne suka ciciko ta d'ago ta kurama Ammar ido, yace " Seemah?"
Share hawayen daya zubomata tayi tace " Banasan sanin ko waye shi."
Zaiyi magana sukaji ana tafi,juyawa sukai suka kalli Junaid.
Ya karaso yana dariya yace " iyee? Abin ma ba kunya a kofar falon Abba? Da alama kun kosa a d'aura." Yai maganar cikin zolaya.
Ammar ya kalleshi yace " Kai fa meza'ace?"
Junaid yai dariya tareda karasowa yace "ne nai ni kuma?"
Kallan Seemah yai yace " Kanwata kema bakya mamaki? Ace wai Junaid an had'ashi aure da Zahra amma ko meta baiyiba sai ma farin ciki dayake?"

Seemah tai dariya tare da kallan Junaid tace "Gaskiya ne yaya nima ina wannan mamakin, itakanta Zahran da na d'auka kai takeso, amma da akace mata Ya Junaid za'a bata na d'auka zatai kuka sai naga kamas."
Dariya sukai su dukansu, Junaid yace " Wato kukuma 'yan sa ido kenan ko?"
Seemah ta kalli Ammar tao murmushi, ido ya kura mata yana mata wani irin kallo, Junaid ya rik'e hab'a zaiyi magana yaji Ammar yace " Farin cikina bai wuce in ganki kina cikin farin ciki ba."
D'agowa tai ta kalleshi, batare datace komai ba ganin yanda yake mata wani kallo yasa tai saurin d'auke idanta tare da kallan Junaid ta wayance da cewa " Ya Junaid ina Ya Zaid?"

Hakan yasa Ammar ya d'auke idansa, tare da kallan Junaid, tai sa'a yace " bazai wuce wajen gate ba."
Ta juya da sauri ba tare da tace komai ba, kallo kawai Amnar ya bita dashi.



Jalal kam har yakai waje zuciyarsa ba dad'i, yana fita gate ya samu gefen gidan ya zauna, idanunsa ne suke gano mai Ammar da Seemah, da sauri yasa hannayinsa biyu yad'an bubuga fuskarsa yana cewa " Wake up Jalal me ke damunka? Kamanta alkawarinka? Katuna abinda mahaifinka yamata ta dalilin cetanka fa?."
Wata nanauyiyar ajiyar zuciya yai tare da cewa " Gaskiya ne, nasani kuma Ammar ne yafi cancanta da ita."
Ya dad'e a zaune kafin ya mik'e ya tafi, sam ya mantada cikinsa wanda tun d'azu yake kara, gidan Sagir ya wuce.

Bayan sun gaisa Sagir ya kalleshi yace " Mutumin yaushe a gari haka?"
Yai murmushi baice mai komai ba, Sagir ya dafashi tare da cewa " duk ciwon soyayyar ne yasa ka rame haka?"
Murmushi Jalal yai yace " Sagir sorry zan d'an takurama kad'an."
Ya fahimci me yake nufi, ya d'an harareshi yace " Jalal me yasa kake min haka?"
Hannu biyu Jalal ya had'a irin na ban hakurin nan suka shiga d'aki, gado Jalal ya fad'a Sagir ya matso kusa dashi yace "daga ina kake haka?"

Jalal yai shiru, hakan yasa Sagir yace " Jalal ba dai......"
Katseshi yai da cewa " yau fa aka d'auramin aure."
What? Me kake nufi?
Jalal ya juya baice komai ba.

Sagir ya mik'e tare da sa hannunsa a kafad'ar Jalal irin na tausa ya fita.
Jalal ya hard'e hannayensa tare da zarfafa cikin tunani, abinda mahaifin Seemah ya fad'a yafi komai tada mai hankali, dama akwai uban da bazai so ganin 'yarsa ba? Shi ya d'auka inyaji zancen hankalinsa ne zai tashi ya kuma nemi ganin 'yar tasa cikin gaggawa bayan laififukan daya tafka.
Wata iska mai zafi ya furzar tunaninsa d'aya tayaya zai sa mutumin nan ya shiryu?
Sagir ne ya shigo, ya zauna kusa da Jalal yace " tunanin me kake?"
Jalal ya mike da sauri ya fuskanci Sagir yace " Sagir kasan Senate Abdullahi?"
Sagir ya kalleshi da mamaki yace " kai kuma ina kasanshi?"
Jalal yai shiru, Sagir yace " Amaryarsa kanwar Ummana ce."
Jalal ya d'ago yace " What?"
Sagir yad'an tab'e baki yace " hmmm ni sam mutumin nan ba wani burgeni yake ba ita kanta Aunty tun bayan auransu da wata 2 ta fara kawo kara."
Jalal yai tsaki yace " ai da alama, amma ita mai yakaita auransa? Ba'ai bincike bane?"

Kallan mamaki Sagir yama Jalal yace " lalai Jalal, mutum kamarsa wanda yakeda kud'i ga mulki shine kake tunanin za'ai wani bincike? Ita kanta Auntyn ai kud'in ne ya rufe mata ido."

Jalal yai shiru, Sagir ya dafashi, yace " ka ga ka raba kanka da mutumin nan Jalal, a yanda Aunty take zancensa sam..."
Kai ya girgiza kawai, Jalal yai shiru ya shiga tunani, Tayaya zaiyi yasa mutum kamar Senate yaba 'yarsa hakuri kafin auranta?

Dafashi Sagir yai, Jalal ya kalleshi zai yi magana cikinsa yai wani kara, murmushi Sagir yai yace " Bari in kawo ma abinci." Ya fita yana dariya.



Jalal ya dad'e yana tunanin mafita kafin bacci ya d'aukeshi.
Washegari ya shirya ya koma Birnin/gwari.





? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 8?



Sagir na dawowa daga raka Jalal mai gadi ya mikamai wata takarda, kallan sa yai yace " nameye?"
Mai gadin yace "d'azu da zaku fita wanda kuke tare ya bani yace in kun dawo in baka."
Sagir ya amsa yana mamakin takardar miye acikin envelope?
Yana shiga d'aki ya fito da farar takarda, abinda idanunsa suka fara gani nai ya kad'ashi, letter of resignation an yi rubutun da manyan harufa ankuma ja layi, wasik'ar barin aiki?
Hannu yasa a aljihu ya kira Jalal, Jalal kam sun d'au hanya ya d'aga wayar, Sagir yace " Jalal me nake gani haka? Ban gane wasik'ar barin aiki ba?"
Jalal yai shiru, Sagir yace " Jalal menene hakan?"
Numfashi yad'an ja kad'an sannan yace " Please kamin submitting d'in takardar, bazan iya zuwa dakaina bane."
Cikin rashin fahimta Sagir yace " aiki ka samu? Ko me?"
" ba wani aiki akwai babban dalilin dabazai sani na cigaba da aiki a company d'in ba."
Sagir ransa ya b'aci yace "saboda soyayya zaka hallaka rayuwarka ko me? Jalal wai me yasa kek neman barin soyayya ta rufema ido?"
Jalal ya d'anyi murmushi inama ace soyayyarce kawai ba wannan babban al'amarin bane? Ya daure yace " Sagir kenan."
Haushi ya kama Sagir ya kashe wayar tare da jefata kan gado, shikam yana mamaki ace wai mutum yabari soyayya ta nemi hargitsamai rayuwa?



Zahra ce ke ta shiga d'akuna tana kaima mutane abincin safe, ta taho da flask d'in abincinsu Junaid tai d'akin, takalman dake bakim kofa ta kalla, takalmin Zaid ne kawai hakan yasa tai sallama tare da tsayawa a kofar d'akin, Junaid dake kwance ya amsa a kasalance, zuciya d'aya ta shiga tana cewa " kai dai ya Zaid kaji jiki ace kowa ya tashi amma kanannan akwance kamar ba namiji ba."
Junaid jin maganarta yasa ya fara murmushi tare da kara shiga bargo, ta matso cikin tsokana tafara jan bargon daya rufu dashi, Junaid ya zaro ido tare da kallan kayan jikinsa, vest ce sai gajeran wando, da sauri shima ya ja bargon nan suka fara jaye_jaye, tana ja tana cewa " Allah yau sai ka tashi kai ko kunya bakaji Yaya?"
Junaid ya kara jan bargo, hannu ta hard'e tare da sa kafarta a kan gado ta kamo bargon da karfinta, ai kam ta fizgo bargon, Kallan mamaki tama Junaid tare da bud'e baki cikin mamaki, Junaid ya fizgo bargon da karfi, itakuma gaba d'aya nauyinta nakan bargon, ai kuwa tabi bargon ta fad'a jikinsa, Ta d'ago ta kalleshi cikin mamaki murmushi ya mata na karfin hali dan shima kunya yaji, yace " Zahra kece?"

Mik'ewa tai da sauri tare da juyawa tai waje da gudu, Junaid ya bita da kallo fuskarsa na wani irin murmushi, Zahra d'aki ta fad'a da gudu tare da sama d'akin makulli ta matso kusa da Seemah dake zaune rik'e da agoggon Jalal, Zahra ta fado kusa da Seemah kamar mai shirin kuka tace " Seemah an kashe ni?"
Seemah ta kalleta tace " an kashe ki kamar ya?"
Zahra ta mik'e ta fad'a gado tai rufda ciki tare da rufe fuska tace " Seemah naga Ya Junaid da vest."
Tana fad'a tare da tura kanta jikin katifa, dariya Seemah ta kyalkyale dashi wanda rabon datai dariya haka harta manta, dariya sosai tai sai data tsagaita tace " Haba? Kuramai ido kikai?"
Zahra ta bubuga kanta tace " Eh mana?"tafad'a kamar mai kuka.
Seemah ta kara sa dariya tace " lalai Zahra wato ba kunya? Kika kuramai ido?"


Zahra ta mik'e zaune tace " wayyo wlh ba da sanina bane nifa bansan shi bane."
Seemah ta guntse dariyarta tace " kyama fad'i gaskiya da alama ma dama haka kika so, yanzu Zahra ko kunya? Hmmm"

Zahra ta mik'e da sauri ta matso gun Seemah ta rik'e hannayenta tace " Seemah yazanyi? Shima zaiga kamar banda kunya ko? Nashina da wani idon zan kalleshi?"
Seemah ta kara guntse dariya tace " gaskiya kam wannan kam fitsira ce."
Zahra kula datai Seemah cinnata takeyi yasa ta kalli Seemah tace " tsaya! Shi yayan naki waya ce yaki fad'amin shine? Ai ni banida laifi."
Seemah tai dariya tace " ahhhh gaskiya ba laifin yaya na bane a dai duba."
Haka tai ta tsokanar Zahra.


Jalal kam har ya isa zuciyarsa ta rasa bashi mafitar alkawarin daya d'auka, yana isa gida yaga mutane a cike, shiga yai duk da ransa ba so yake ba, nan suka shiga gaisawa da jama'a wasu 'yan uwan Zainab ne wasu nashi, yana gama gaisawa ya wuce d'akinsa ya kwanta, Abba ne ya shigo d'akin ya tsaya a bakin kofa yace " Jalal?"
Jalal bai juyaba yace " Naam"
Abba yai shiru cikin sanyin jiki yace " kaga Abdullahin?"
Jalal yace " eh amma...."
Sai kuma yai shiru, Abba ya kalleshi yace " Jalal mutumin nan ba mutunci gareshi ba ka karfi na dukiya da mulki dayake das??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????hi bana tunanin kanada hanyar dazaka sashi abinda baiyi niyya ba."
Jalal yai shiru, tabbas yasan haka abin yake, Abba ya cigaba " Kai ba Lawyer ba, ba kuma D'an jarida ba mai zaka iyayi? Bayan ko shari'a yafi karfinta?"

Da sauri Jalal ya mik'e ya yace "d'an jarida? Lawyer?"
Kallansa nai nima cikin mamaki mai yake nufi?







*HUSSYLURV, BILLY, AENART, AMAL, HADIJA, ZEE BALA, UMMU NAFISA, RAMBI. DAFATAN KUNYI WEEKEND LAFIYA.*



? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

_Ina kara ba masoyan littafin nan hakuri na jina shiru da kukai kwana biyu, a min afuwa ina cikin taro ne.......Nagode kwarai da kulawarku da kuma kaunar da kukema littafin nan_


No. 5? 9?

Abba ya kalleshi shi kanshi bai fahimci mai Jalal ke sakawa a ransa ba amma mamaki ne bayane a fuskarsa ganin Jalal na murmushi.
Daurewa yai yace " Jalal kazo ka fita gun abokanka anjima kad'an za'a kawo amarya."
Ya kalli Abba yace " yanzu Abba inza'a kawo Zainab gidan nan har sai na fita? A gidan nan take da fa, sannan ni gun wa zani kasan ba abokai garan ba."
Abba yace " Al'ada ce hakan yaza'ayi akawo Amarya kuma Ango na cikin gidan? Ai sai daga baya zakuzo siyan baki da abokanka."

"Siyan baki? Bakin wa kuma zan siya?" Yai maganar cikin mamaki.
Abba yai murmushi yace " Jalal ya akai bakasan komai na aure ba? Ai in aka kawota sai kunzo kun ba kawayenta kud'i sannan su tafi."

" Ah wannan ba siyan baki bane, neman kud'i dai kawai."
Abba yace " Haka dai akeyi d'an haka kazo ka fita sannan ga wannan." Ya mik'a mai bakar leda an d'an nad'eta, Jalal ya amsa yana kallan Abba.

Abba ya cigaba " 'Yan uwanka ne suka tara maka, sai ka ciri wani abun kaba 'yan siyan baki sannan a ciki ka siyo kaza da madara ko yogurt ko lemo, na fad'ama su Kafilu suzo su rakako anjima."

Jalal ya irga kud'i dubu 20 ne cif, ya kalli Abba yace " Yanzu Abba meyasa akasa su tara kud'i haka?"
Abba ya sake Murmushi yace " ba wanda ya sasu, dama haka akeyi, had'awa akeyi kowa ya kawo nawa yai niyyar bayarwa."
Jalal yai shiru yana kallan kud'in, Abba ya juya tare da cewa, kai wanka kasa sabon kayanka kazo ka fita.
Jalal yace to, sannan yace " Amma Abba baka tambayeni......."
Abba ya juyo ya kalleshi yace " nasani Jalal, amma daga baya mayi maganar."
Yana fad'a yai waje.
Kallo yabishi dashi sannan ya zauna a bakin gado, shifa sam baiyadda wai shine akama wani aure ba, shi da yad'auka in mutum aka mai aure wani farin ciki ne ke mamayeshi, to shi ya yake jinsa ba wani farin ciki? Sai ma wani bakim ciki na mahaifin Seemah dake nukurkusar sa? Ga zafin rabuwa da abinda zuciya da gangar jiki ke bege."

Ya zaiyi?
Haka dai ya mik'e yai wanka ya zura shaddarsa sabowa da Umma ta d'inkamai ya fita, cikin gida ya kara shiga ya musu godiya sannan ya fita.

Waya ya d'auko ya kira Sagir, shikam Sagir haushin Jalal duk ya isheshi, da kyar ya d'aga wayar, Jalal yace " Sagir d'an Allah tambaya, a tsakanin Lawyer da d'an Jarida wanne yafi d'aukan lokaci wajen gama karatunshi?"

Haushi ya kara kama Sagir

27 / 37