JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   15 / 37

42K to 45K   out of 109.4K words

haba Umma meyasa bazaki fahimceni ba?"


Zainab ta d'ago fuskarta duk ta b'aci da kwalla, ta kalli Jalal shikin bakin ciki tace " Yaya yaushe ka zama haka? A da na d'auka kai mutum ne mai tsananin girmama iyayensa, menene dalilin dayasa ka canza? Nice bakasan aure? Saboda ni kake wannan abun?"


Jalal ya had'e rai wani kallo ya buga mata yace "in ima magana da Umma karki kuskura ki kara katseni." ajiyar zuciya tai idanunta suka kara zubar da kwalla tace " Umma d'an Allah kubar shi ya auri wacce yakeso." Tana kainan tai d'aki da gudu ta rufo kofar, kallo Jalal ya bita dashi, Umma tace " Jalal ka bani mamaki." Itama ta juya ciki.


Iska ya furzar daga bakinsa wayarsa ce tai kara ya cirota daga aljihu, ganin Sagir yasa ya d'aga wayar Sagir yace " Jalal kana ina? Kazo Habib na nemanka."

Jalal yace " bangane yana nemana ba? Yau asabar ban fahimci dalilin dazaisa a nemi ni ba bayan ina hutun weekend. "

Sagir yace " to d'an ka'ida amma please kazo yanasan ganinka wajen 5 yace it's urgent."

Harzai musa sai kuma yai tunanin da alama maganar bata aiki bace mayb tsakaninsa ne da Seemah, da sauri yacema Sagir okay zanzo.

Yana katse wayar ya shiga d'akin Umma, a zaune ya ganta ta baza tagumi, ya karasa kusa da ita ya zauna ya kalleta yace " Umma?" Juyo da fuskarta tai ta kalleshi, yacigaba" Umma ko nace dole sai na auri Seemah baza ki amince dani ba?"

Tace kwarai, yai ajiyar zuciya yace " ko nace Seemah ce jigon rayuwata bazan iya rayuwa ba sai da ita bazaki amince ba?"

Kallansa tai da mamaki tace " Jalal!! "

Yace " ko nace in ba da itaba bana tunanin zan iya zama da wata a matsayin matata bazaki amince ba."


Kallansa take cike da kulawa tace " Jalal yaushe ka fara soyayya haka? Ban tab'a tunanin zaka so mace haka ba? JALAL meya sameka? Baka tunanin sun maka asiri?"

Mik'ewa yai ya juya mata baya yace " nikaina bansan ya akai na zama haka ba Umma, bansan yaushe zuciyata tai rauni akan mace haka ba, in tana dariya sai insamu kaina cikin farinciki, in tana bakin ciki sai inji nafita damuwa, in taji ciwo jinshi nake kamar a jikina, in ina tare da ita jinake kamar kar mu rabu, Umma bansan meke damuna ba."



Idanun Umma ne suka cika da kwalla, ta kalleshi cikin tsananin tausayi, lalai ta fahimci halin da d'anta yake ciki amma ya zatai da Zainab? Mik'ewa tai ta dawo ta gabansa tace " nafahimceka kwarai Jalal sai dai Jalal abinda baka sani ba shine, rayuwar aure ba soyayya ake nema ba kawai.

Kai ya girgiza yace " Umma ban damu da wad'an nan ba."


Shiru tai jikinta duk yai sanyi, Jalal ya kalleta yace zan koma Abuja yanzu ana nemana zanzo wani satin, Umma d'an Allah kitaimaken kishawomin kan Abba.

Takalleshi tace daga zuwa? Yace eh oganmu ke nemana, tace to Allah ya kiyaye.


Direct tasha ya nufa ya shiga mota, tunani yakeyi ta ina zai fara shawo kan lamarin.




A company d'insu ya sauka, office d'in Habib ya wuce, ba kowa saboda yau weekend, knocking d'in kofar yai daga ciki akace ya shigo, shiga yai da Sallama, Habib ya bashi izini zama, shikam yana tunanin harda maganar san Jalal da Seemah take yasa Dad cikin wannan halin dukda baisan takamaimai dalili ba sai dai shikanshi bazai yarda da wannan soyayyar ba.


Zama Jalal yai sannan Habib ya mik'amai hannu, sun gaisa Jalal yace " akace kana nemana?"

Habib ya kalleshi tare da ajiye takardun hannunsa, yace " kasan kanwata?" Kai Jalal ya d'aga, Habib yace " akwai wani abu a tsakaninku ne?"

Cikin rashin fahimta Jalal yace " kamar me fa?" Habib yace " kamar abinda ke tsakanin mace budurwa da namiji."

Jalal yai murmushi sannan yace " eh, we like each other. "

Habib ya tattara hankalinsa kan Jalal sannan ya zaro envelope ya tura masa abansa, Jalal ya kalleshi da rashin fahimta yace na meye? Habib yace ka bud'e, Jalal ya zaro abinda ke ciki check ne na million 3, cikin tsananin mamaki da tambaya ya kalli Habib yace na meye? Yai maganar tare da ajiye envelope d'in.

Habib yace " wannan kud'in ina tunanin ya isheka ka fara business d'an haka inaso kabar garin nan kaje wani gun ka fara kasuwancinka."


Jalal ya kalleshi yace "bangane in fara kasuwanci ba? Kuma kai a matsayin me kake a guna da zaka bani kud'i ka kuma umarceni akan wasu sharad'u dabata shafi aiki ba?"


Habib yaji zafin kalamansa amma ya daure yace " ina nufin ka rabu da Seemah, kai kanka kasan tafi karfinka, ko kana tunanin kanada abinda zaka kula da ita ne?"


Jalal ya saki wani murmushi yace "Ahhhh dalilin kenan? Sai dai yaza'ayi yaya Habib bana tunanin zanyi accepting wannan offer taka."

Yana kai nan ya mik'e cikin tsananin b'acin rai, zai iya jurar komai amma ya tsani amaidace gara wanda za'a iya siya da kud'i.


Habib shima ya mik'e zaiyi magana kawai sukaga an turo kofar, Seemah ce da Ammar suna dariya, dariyar ta tatsaya ne sanda taga Jalal, da mamaki ta kalleshi tace " My Deen me kake a nan? Ba kace kana birnin gwari ba?"

Idanunsa ta kalla ba shakka ransa a b'ace yake matuka, Jalal ya kalleta sannan ya kalli Ammar ya juya ya kalli Habib yace na wuce, ta kusa da su yazo ya wuce bai kula Seemah ba, Ammar ya bishi da kallo haka kawai yaji bayasan guy d'in.

Seemah kam kallan Habib tai tace " yaya lafiya?" Bai amsa mata ba kawai ta juya tai waje da gudu, Ammar na k'iranta amma inaaa, da kyar ta tadda Jalal yana jiran elevator da sauri tasha gabansa tana hakki, tace " Deen menene? Yanaganka haka? Kana ganina baka min magana ba."

Kallanta yai sannan yace " haka kuke dama masu kud'i? Komai bakwa iya solving d'insa sai da kud'i? What do u people think of me? Kije ki sanar dasu halaye na."

Gaba d'aya Seemah takasa fahimtarsa, bai jira amsarta ba yana ganin Elevator ya tsaya ya danna ya shiga ya barta a tsaya tana maimaita kalamansa.






? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

_To you all my fans, wish you happy new year

No. 3? 1?



Juyawa tai da sauri ta koma office d'in Habib.

Ammar ne ya tsaya kallan Habib cike da mamaki yace " yaya waye waccan d'in?"

Habib ya juya baya yace " bakaji abinda Seemah tacemai ba? Shine wanda takeso, bakuma soyayya ta wasa ba harda maganar aure take nufi."

Dariya Ammar yai yace " haba yaya kamar bakasan kanwata ba? Na sani guy d'in daya fita yana da cikar zati da kirar jikin da maza ke so, amma kanwata bata damu da wannan ba, wanda takeso shine wanda zai kula da ita, wannan kuwa kana ganin yanda yaganta ya wani d'auke kai?"

Habib ya matso kusa dashi ya rik'e hannayensa yace " Ammar, Dad fa nacikin tsananin damuwa bansani ba ko shine dalilin ko kuma da wani abun."

Ammar yace " Dad kuma? Nifa na kasa fahimtar abinda kake nufi? Kanasan kacemin yaran nan shi Seemah keso.................."

Da karfi sukaji an bud'e kofar, suka juya atare Seemah ce tsaye fuskarta a had'e, ta karaso kusa da Habib ta kalleshi ido cikin ido tace " Yaya mai kawa Deen?"

Habib ya had'e rai shima yace waye wani Deen?


Ta kara had'e fuska, tace " Jalal, mekamai?"

Ammar da mamakin abinda yake gani yace " Seemah waye waccan d'in dahar zai sa ki zo ki tsare yayanki da kike girmamawa?"

Idanta ne ya ciko da kwalla ta kalli Ammar ta??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ce " Ya Ammar na rasa dalilin dayasa akemin haka, na d'auka kowa yana da right d'in dazaiso abinda zuciyarsa take so?"


Ammar kam yama kasa furta wata kalma, haka kawai yaji ransa na b'aci, me yarinyar nan take nufi? Bai ankara ba kawai yaga ta tsugunna tare da rufe kanta da hannu tana kuka, cikin kukan take cewa" Ya Habib please karku rabani da Deen, yanzu gashi ya tafi bansan ya zanyi ba."

Habib haushi ya kamashi kawai yai waje da sauri duk da yanajin kukan kanwartasa har cikin ransa.

Yana fita Ammar ya tsaya kawai yana kallanta, Jin idanunsa suna neman kawo ruwa saboda kukan datakeyi yasa ya matso ya zauna shima kusa da ita a hankali ya jawo kanta ya kwantar akan kafad'ar sa.

Kwanciya tai lamu, ta fara share hawayenta, Ammar cikin sanyin murya yace " Seemah do u love him that much?"
Kai ta d'aga sannan tace " yaya bansan ya zanyiba yayi fishi dani?"

Ran Ammar yakara b'aci sai dai ya d'aure yace " Seemah kinsan me? Ta girgiza kai, yace" Falling in love is so easy but keeping that love is very difficult., bansan yaushe harkika fara soyayya haka ba, but karki bari soyayya da kikeyi tajawo fad'a tsakaninki da iyayenki da kuma 'yan uwanki."

D'agowa tai ta kalleshi ta kara share kwallarta, sannan ta kalli idanunsa da kwalla ta taro murmushi ta saki, tace " yaya please please kar ka k'i abinda nakeso, in har kaima kak'i Deen it will make it difficult for me. "

Murmushi ya kakaro wanda kana ganinshi kasan a iya leb'ensa suke, ta mik'e tace "yaya kataimaken please kaji?"
Yace name fa?

Tace ka k'ira Jalal a wayarka kacemai yai hakuri duk dabansan me ya Habib ya mai ba.


Ammar ya kalleta cikin mamakin gaske yace what? Me? Kai ta d'aga cikin halin ko in kula tace " kaine best bro d'in na kaikad'ai nake tunanin zakamin abinda nake so kuma, kaji yaya please? "

Kallanta yake da mamaki, sai dai haka ya sabar mata bai iya ce mata a'a ba akan duk abinda tace, wayar ya mik'amata tai tsalle tare da ansa tasa number tai dialling.


Jalal kam yana fita waje yai kawai tafiya yakeyi, zuciyarsa taf take da tunani kala kala, yarasa meya kamaceshi, sai dai abinda yafi bashi takaici kud'in da Habib ya bashi, me ya d'aukeshi? Jin karar waya yasa ya zarota daga aljihu ganin number ne yasa sai data kusan katsewa ya d'aga tare da Sallama, Seemah naji sallamarsa tai saurin mekama Ammar waya, Ammar ya mik'e tare da ansa duk da ransa bayaso, ya amsa tare da cewa "Yayan Seemah ne da muka had'u a office d'in Habib yanzu."

Ran Jalal ya kara b'aci yace " Wani kud'in kaima zaka kara bani akan in rabu da Seemah ko me?"

Sai a lokacin Ammar ya gane abinda ya faru, amma saboda bayaso Seemah tagane yace" Hmm da Alama wannan saurayin na kanwata yanada zafin rai."

Jalal ya kara had'e rai kamar Ammar na ganinshi yace " Ya akai to?"

Ammar yai ajiyar zuciya tare da kallan Seemah data rik'e hannunsa tana rokonsa, ajiyar zuciya ya sakeyi yace " Kanwatace tace in k'ira in baka hakuri."


Jalal yace " me kace?"

Ammar ya kara kufula yace " Kanwata ce ta damu da yanda taganka shine takeso naji ko komai lafiya."


Jalal yace " kana nufin saka tai ka k'irani ko me?"

Ammar ya had'e rai sai dai yazaiyi? Yace " gata tana san magana dakai." Yana kainan ya mik'ama Seemah wayar yai waje da sauri.




Seemah na amsa tace " My Deen ka sauko?"

Jalal yace " wannan yayankine?"
Tace " eh special brother na ne." Ya d'an tab'e baki kad'an yace" shine kikasa ya k'irani? Yama za'ai ya biye miki? Kuma ce miki akai in kika k'irani bazan d'auka ba?"


Turo baki tai tace " menene d'an nasashi yamin abu? Ni duk abinda nace masa inaso yimin yakeyi, sannan yanda naga kayi shine yasa nai tunanin bazaka d'aga ba."

Murmushi Jalal yai a ransa yace lalai an sangartata dayawa, a fili yace naji, zan k'iraki a wayarki anjima.

Tace zan jiraka fa? Yace eh zan kira.

Sunyi sallama ta kashe wayar tare da sakin murmushi.


Jalal ma yabi wayar da kallo ya saki murmushi.


Ammar kam yana fita toilet ya shiga yai ta watsama fuskarsa ruwa, kalaman Jalal ke dawomai, mirror d'in toilet d'in ya kalla sannan ya goge fuskarsa ya fito.



Habib na fita daga office ya nufi gidan Abba, ba yan sun gaisa da Zahra ne ya tambayeta mahaifiyarta, tace " taje Suleja d'azu da safe."
Habib yace wani abun ya faru ne? Zara ta girgiza kai tace " wlh bansani ba Yaya naga dai da safe Abba ya k'irata tana dawowa tace suleja zata."

Habib ya d'aga kai sannan yace" Abba fa?"

Tace yana falonsa kaje, Habib ya tura kai b'angaren Abba.


Yai sallama Abba ya amsa tare da bashi izini, Habib ya shiga, a zaune yaganshi kamar yanda ya saba da jarida a hannunsa, bayan Habib ya shigo ya ninke jaridar tare da kallansa, Habib ya karasa ya zauna a kasa tare da gaidashi.

Abba ya amsa yace " Habibu daga ina haka?"

Habib ya d'ago yace " Abba wani abu ke damuna." Abba ya kalleshi da mamaki.

Habb yace " d'azu naje gun Dad na ganshi a wani yanayin da bazan iya fad'a ba, Abba abin nan ya dameni ya hanani sukuni, da farko nai tunanin ko Saurayin da Seemah takeso ne bayaso, amma yanzu kaina ya kulle, bansan menene ba."


Abba ya gyara zama yace, saurayin da Seemah takeso? Kamar ya? Akwai wanda takeso ne?"

Habib ya d'aga kai yace " eh tasanar mana ni da Dad jiya."

Abba yai shiru, wato wannan ne dalilin dayasa Dad yake tunanin abubuwa kala kala? Yanzu gashi ganin seemah da Hajiya tai dakuma zuwan Dad dayai yasa ta takwanta d'an ciwonta ya tashi.

Habib ne ya katseshi yace " Abba ya za'ayi?"

Abba yace " zamuyi magana da Isma'el d'in sai dai inaso kaima inkaje gida ka kwace wayar Seemah ka kuma hanata fita harsai mun gama yanke hukunci da Mahaifinka."


Habib yace " to Abba amma Seemah zata yarda kuwa? Tanasan yaron....."

Katseshi Abba yai ya mik'e yace " Seemah gwal ce? Kai meyasa kaida mahaifinka halinku yake d'aya ne? In kasan abinda mahaifiyarta taja mana bazaka tab'a bin bayanta ba."

Habib ya kalleshi da mamaki yace " bangane mahaifiyarta ba? Ba Maman mu bace ta haifeta kake cewa ko me?"

Sai a lokacin Abba ya tuna, Habib da Jalal da babban d'an Abba Jafar tare suka kaisu karatu tun suna yara yan 15yrs da Habib da Jafar, junaid kuma 12yrs aka kaisu England gun Kanwar mahaifiyar Jafar dake zaune acan, Abba shiya had'asu ya biya musu karatunsu, a lokacin da abin ya faru suna can, Ammar ne kawai a gaban mahaifiyarsa lokacin yana d'an shekara 5.


Habib ya sake cewa" Abba bakace komai ba?"

Juya baya Abba yai yace " wani abune a raina, sam hankali na yana gun, kaje ka aiwatar da abin da nasaka kawai."

Yana kai nan ya juya yai d'aki, Habib ya bishi da kallon mamaki, me Abba yake nufi? Daga yanda Abba yai maganar yama za'ai ya yarda wai badashi yake ba? Shidai a iya saninsa Seemah mahaifiyarsu tana haifarta tabar duniyar, wannan shine abinda suka sani kuma dashi suka taso, to amma me Abba yake nufi da kalamansa..........?





S'T'S'T'S'T'S'T'da alamar tambaya......injini=??



? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*





@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 3? 2?


Ammar ne ya fito daga toilet, a bakin kofar toilet d'in ta ganshi yana fitowa ta d'aneshi, tace "yaya godiya sosai, thanks to you munshirya da Deen."


Ammar ya had'iye wani bakin cikin sai dai ya kakaro murmushi yace " are you that happy?" Kai ta d'aga sannan ta d'ago ta kalli Ammar tace " yaya inasan Deen sosai, kasan me?"

Kallanta yai zuciyarshi kamae ta fashe duk yanda yaso ya b'oye bakin cikin dake ransa ya kasa, Seemah tai murmushi tace " amma kasan wani secret yaya? Na kasa tantance wayafi matsayi tsakaninka da shi a guna."

Ammar ya kalleta jiyai zuciyarsa bazata juri ganin ta ba, shi zata had'a da wani bare da ko wata da had'uwa basuyi ba? Juyawa yai ya fara tafiya batare da ya tankamata ba, da sauri tasha gabansa ta rangwad'ar da kai tace " Ohhhh my bro ba dai haushi kaji ba?" Idanunsa ya runtse saboda bazai iya fad'a mata magana mara dad'i ba, gashi bai san ya mata magana, cewa yai" Seemah matsa mu wuce, Dad nake san gani."

Ya matsa kad'an daga kusa da ita, hannunsa ta kamo tace " wasa nake yaya." Juyowa yai ya kalleta tai murmushi tace " yaya inasan Deen sosai amma yama za'ai in had'ashi da kai? Ko kamanta ne? In na kwanta zazzab'i saboda shakuwarmu kaima sai ka kwanta?"

Tai murmushi sannan ta cigaba" tsokanarka kawai nakeyi, Deen soyayyar macen dake bala'in san saurayinta nake mai kai kuma soyayya ce ta jini yama za'ai ka had'a?"


Murmushi ya saki sosai ta had'a yanayenta biyu ta tafamai tace " yauwa my dear bros yanzu kafimin kama da yayana."

Ajiyar zuciya yai, yace " Seemah nima

15 / 37