JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   17 / 37

48K to 51K   out of 109.4K words

Ammar ya zauna.

Ammar ya kalleshi tare da cewa "Yaya ka iso?" Habib ya d'aga nasa kai alamar eh yamaida kallansa kan Dad dayai shiru, a zuciyarsa kam addu'arsa d'aya ce Allah ya taimakeshi akan abinda yake shirinyi.

Habib ganin Dad yayi shiru yasa yace " Dad kayi shiru?"

Ya sauke idanunsa akan Habib sannan yamaida kallansa kan Ammar yai gyaran murya tare da cewa " inaso ku bani aran hankalinku nan."

Gaba d'ayansu suka maida kallansu kanshi, Dad ya had'iyi wani abu sannan yace " abinda nake shirin sanar daku shine......."

Duk sun zak'u gashi maganar Dad ta katse bai karasa ba, jin shirun dayai yasa Ammar yace " Dad yaka tsaya?"
Dad yai shiru sannan ya sauko tsakiyansu ya zauna tare da dafa Ammar idanunsa taf da kwalla yace " Ammar kasani inasanka ko?" Murmushi Ammar yai yace " haba Dad harsai ka fad'i haka?"

Dad ya kakaro murmushi sannan ya mik'e tare da takawa gaba dasu kad'an ya hard'e hannayensa ta baya, ya juya musu baya ya cigaba " lokaci yayi daya kamata in sanar daku wani sirri da baku tab'a sani ba, Ammar banaso ka sa wani mugun abu a ranka dalilin dayasa na yanke shawarar sanar daku shine Ammar nakeso ya auri Seemah."


Ba Ammar ba hatta Habib mik'ewa yai a zabure, Dad kam idanu ya runtse, Ammar da Habib a tare suka had'a baki suka ce *What?* Ammar ya cigaba da magana " ban fahimci me kake nufi ba Dad, ni in auri kanwata? Me kakesan fad'ane Dad?"


Habib ya amshe maganar da cewa " Dad me kake nufi da kalamanka? Wani irin zance kakeyi haka? Kana nufin akwai aure a tsakanin Ammar da Seemah ko me?"


Dad ya d'aure tare da share hawayen da suka kwaranyo ta gefen idanunsa, ya juyo tare da cewa " haka ne Habib akwai aure a tsakaninsu domin kuwa Ammar ba d'ana bane."

A tare suka kara cewa *what?* gaban Ammar ya fad'i zubewa yai kasa tare da kallan Dad cikin wani irin rud'ani, Habib ma ya kalli Ammar sannan ya kalli Dad yace " ban fahimceka ba Dad kanasan kacemin Ammar kanina ba kaine mahaifinsa ba?"

Dad ya d'aga kai tare da cewa " nasanar dakune saboda inasan had'shi aure da Seemah shiyasa na aika yazo kasar nan."



Girgiza kai Ammar ya shigayi da sauri ya mik'e yai waje da gudu, Dad ya runtae ido shikad'ai yasan meyakeji, Habib ya matso kusa da Dad, ga mamakin Dad gani yai Habib ya saki murmushi yace " Dad do u expect me to believe that? Mene? Ammar ba d'anka bane? Banda tsananin kama da kukeyi? Da muma mukeyi dashi? Me kakesan cewa dad?"

Dad yai saurin juya baya tare da cewa " kanina da nake tsananin kama dashi shine mahaifin Ammar yana haifarsa sunyi tafiya sukai hatsari shida matarsa wannan dalilin ne yasa na anso Ammar tare da alkawarin kula dashi kamar d'ana."

Habib yai shiru tare da jinjina kai yace " ayya meyasa baka tab'a fad'amin ba Dad?" Ganin Habib ya yarda da kalamansa ne yasa Dad ya juyo yace ba wannan bane da muwar da ya kamata muyi yanzu, Seemah kana tunanin zata rabu da waccen banzan yaron? Habib yai shiru sai can yace " Dad Allah ne kawai ya sani, amma yarinyar nan sai anyi da gaske wajen rabasu, har kud'i na bashi d'azu akan ya bar aikin dayake a company d'ina ya bar garin nan amma yak'i, Dad yaron nan yanada taurin kai."


Dad yai tsaki tare da cewa duk taurin kansa ai baifi karfin iyayensa ba, su kuma iyayen nasa nasan basufi karfin kud'i ba,ka bincikomin garinsu zanje har gidansu in basu kud'i su sa d'ansu yabar aiki a company d'inmu.

Habib ya jinjina kai yace " wannan ma is a good idea."

Dad yace " naso in d'auketa mubar kasar amma kuma sai nai wani tunani, inaso kafin mu koma ai baikonsu da Ammar inyaso daga baya sai ai auren."

Habib yai shiru bai amsa ba, shidai tana mamakin wannan al'amarin.

Nan yai sallama akan gobe zai turo address d'in gidansu Jalal.




Jalal kam da kyar ya lallab'a Jalal suka wuce gidansu, sunje shiga gate d'in gidan Yaga k'iran Abba, da sauri ya d'auka tare da saisaita murya ya gaida shi, Abba ya amsa tare da cewa " Ashe ka koma?"
Jalal yace " wlh k'ira na akai na gaggawa."
Abba yace " ba wani abu dama na k'iraka ne na sanar dakai na yanke hukunci ranar Juma'a rana ita jiya kenan, za'a d'aura maka aure da Zainab, ka kuma tabbatar ka iso da sassafe."

Cikim razana Jalal ya bud'e murfin mota ya fita tare da cewa " Abba ban fahimci me kake nufi ba, bangane Aure ba?"

Abba ya had'e rai yace " na yanke hukunci kuma baka isa ka bijirema hukuncina ba kafi kowa sanin hali na, sannan bazan yarda da wani shirmenka ba."


Jalal yace " Amma Abba......."

Cikin fad'a Abba ya katseshi da cewa karka kuskura Jalal kace zaka d'inga musu dani, kai ko kumya bakaji ba? Yarinyarnan tun tana karama take taimakon mahaifiyarka da kanwarka, kai kana tunanin dabadan Allah yasa tana nan ba wani abun ai mahaifiyarka bazata iya jura ba."


Jalal zai kara magana Abba ya kara katseshi da cewa " ka kuma tabbatar ka zo ranar juma'a da wuri d'an intanine gobe ma za'a d'aura auran sa'a kaci mahaifiyarka ta nemi izini zuwa juma'a." ABBA nakainan ya katse layin.


Bin wayar Jalal yai da kallo meke faruwa? Dasauri ya danna number Umma sai dai lokacin tana zaune kusa da Abba hakan yasa tak'i d'aukan wayar d'an umarnin Abba ne kar kowa ya d'auki k'iran Jalal.



Ganin taki d'auka yasa ya k'ira Zainab tana zaune akan sallayar datai salla tana lazimi, ganin k'iran Jalal yasa tai murmushi sai dai data tuna me ya mata da kuma umarnin Abba yasa ta canza fuska ta koma kalar tausayi, sai dai inaaaaa bazata iya ganin wayar Jalal ta katse ba tana zaune, saura kiris ta katse ta d'aga tare da sallama, Jalal ya amsa tare da cewa " Zainab meke faruwa? Ban gane aure wani satin kai tsaye ba?"


Zainab tai kasa da kai a hankali tace " Yaya bansan nima meya faruba gaskiya kawai tun sanda Abba ya fita d'in nan, inaji gidan mu yaje, d'an bai dawoba sai daf da magrib, bansan meya faruba kawai yacemin inyi hakuri lefe da wani sha'anin biki ayi daga baya in inaso amma wani satin za'a d'aura mana aure amma anan zan zana kafin ka samu gida."



Jalal yaja dogon ajiyar zuciya tare da cewa " it can't happen." Yana fadar haka ya katse wayar tare da neman number Seemah, sai dai duk yanda yake k'ira layin a kashe yake matar take sanar dashi.



Hannu yasa ya shafi kansa sannan ya furzar da wata isa tare da naushin jikin bango da hannunsa, yaji zafi kwarai sai dai baikai zafin da yakeji a zuciyarsa ba.





Sagir ne ya matso ya dafashi, baice mai komai ba.




Seemah kam taci kuka harta gaji, Aisha sai dariya takeyi, d'an karma tai lallashi yasa taki shiga d'akin, gani take gwara a saita mara kunya da sakalci.

Farida kam shigarta uku tana bata hakuri amma inaaaaa seemah taki hakura sai kuka takeyi itadai a bata wayarta.







? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*




@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 3? 6?




*Washegari*..........


Seemah na kwance tana bacci Dad ya karaso gidan, bayan sun gaisa da Habib da matarsa da 'ya'yansa kasancewar yau lahadi kowa na gida, Farida ta kwashe su Ra'isa suka barmusu falon, Dad ya kalli Habib yace " yaya ka nemo gidan?"

Kai Habib ya d'aga tare da cewa na nemo Dad dama na tab'a tambayar abokinsa Sagir a wani gari Jalal yake shine yacemin Birnin/gwari, to shine nasa akamin bincike a garin, ya fada tare da mik'amai takarda.

Habib ya kara kallan Dad yace " Amma Dad kana ganin hakan ne ya dace?"

Dad yai murmushi yace " Habib kenan, ban tab'a ganin yaran ba amma tunda kar baiji kunyar kallan Seemata ba yace yana so hakan ya nunamin he is stubborn sannan iyayensa ne kad'ai zasuma tufkar hanci."

Habib ya gyad'a kai alamar gamsuwa, Dad ya amshi takardar tare da cewa yauwa Habib nagode, sannan ina so anjima ka shirya kaje Suleja ance jikin Hajiya ya tashi.

Habib ya amsa ta to, tare da cigaba da cewa " Amma Dad ya maganar Ammar?"

Dad yai murmushi tare da cewa "karka damu yana Nordic Villa, sai wajen 1 na dare dana dameshi da waya shine yamin text."


Habib yai kasa dakai yana tausayin kanin nasa, Dad ya mik'e tare da cewa ina baby na?

" Tana d'akinsu mayb bata tashi ba."


Dad yai hanyar d'akin kai tsaye a raina nace lalai rayuwar turai ta zauna muku amma mu anan yaza'ai uba ya wuce cikin gidan d'ansa kai tsaye? ?????



Yana ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?isa kofar d'akin daidainan Aisha ta fito daga d'akin,, ganin Dad yasa tai saurin risinawa ta gaida shi, Dad ya amsa fuska a sake yace " Seemah fa?"

Ta kalli d'akin tace " tana bacci."

Bai amsa mata ba ya tura d'akin tare da sallama, a kwance take tama baccinta zama yai gefenta yana kallanta, ba shakka tana tsananin kama da mahaifiyarta, sai dai ko d'an shi kansa bai san uban bane???? Hannu yasa ya shafi gefen kanta a hankali Seemah ta bud'e ido ta saukeshi akan Dad, murmushi ta saki cikin abin bacci tace " My Dad yaushe ka iso?"

Yanzun nan ya fad'a yana kallanta.

Ta mik'e zaune tare da rik'e hannayensa, tace " Dad please kad'aukeni mukoma gidanmu kaji?"

"Bakyasan gida Habib d'in ne ko me?"


Sake hannun Dad tai ta turo baki tace " banaso Dad ni Yanzu nama daina san Ya Habib, Dad please mukoma kaji? Gani gaka ga ya Ammar hakan yafi dad'i."


Dariya Dad yai yace " Seemah kinsan ba mace a gidan dazata d'inga girki da sauransu."

Ajiyar zuciya tai tace " Nidai to banasan gidan nan"

Dad ya mik'e tare da kallanta yace " Amma yanaga idanunki haka?"


" banacr maka banasan gidan nan ba? Dad dan dai bakasan me ya Habib yamin bane, yanzu ko waya ma bandashi, narasa meyasa bayasan Deen bayan ni zan........."

Wani kallo da Dad ya maka mata yasa tai shiru tare da cewa " ni duk kun daina sona ma ina Ya Ammar d'ina?"

Dad ya saki fuska yace " yauwa dama abinda nazo fad'a miki kenan, Ammar bayajin dad'i shiyasa nakeso kije gunsa."

Dirowa tai daga kan gado tace " me ya sameshi? Jiya fa lafiyarsa kalau."

Ganin yanda ta rud'e yasa Dad yai dariya yace " Yana Nordic villa kishirya kije."

Da sauri ta zari towel d'in wanka tace " Dad nayi nan."


Dariyar farinciki Dad yai yanasan yanda sukesan junan.


Fitowa yai sukai sallama da Habib da kuma Farida ya fad'a motarsa driver ya jashi sai binin gwari.




Jalal kam sam jiya kasa barci tai saboda bayasan takurama Sagir yasa ya kwanta kamar mai bacci harsai da yaga Sagir yafara bacci sosai sannan ya mik'e ya d'auro alwala ya fara sallah a neman mafita agun Allah sai wajen karfe 3 bacci ya d'aukeshi akan sallar.

Da safe bayan sunyi wanka Sagir yabashi d'aya daga cikin kayansa yasa, nan ma dakyar Jalal ya yarda, Sagir ya nunashi da yatsa yace " gaskiya Jalal bansan irinka ba? Meyasa ne sam bakasan kai amfani da abin wani?"


" Sagir tun ina karami haka na taso, Hali nane, banasan amfani da abinda ba nawa ba ko neman alfarmar wani ko kuma bari kud'i su nemi cin galabata."


Kai Sagir ya jinjina yace " shiyasa kowa yake respecting d'inka, wlh ko ni ina bala'in ganin girman ka."

Murmushin dabai wuce iya leb'e ba Jalal yao sannan ya d'aga waya ya kara k'iran umma sai dai yanzun ma bata d'aga ba, ajiyar zuciya yai tare da kallan Sagir yace " tunanin zuwa birnin gwari nakeyi."

"Yanzo? Ba jiya ka dawo ba?"


Ido Jalal ya kankance ya kurawa wani gun ido baice komai ba.

Sagir ya daga kafad'ar sa yace " Calm down Jalal."

Kallansa Jalal yai yace " how can I? In this situation? Ga nakasa samun Seemah?" Sagir zaiyi magana yaga Jalal ya mik'e tare da cewa " Inaji gidansu Seemah zani."


Zaro ido Sagir yai yace " Jalal meke damunka wai? Yaushe kazama haka wai? Taya za'ai kaje gidan da inagani a ido ba sanka ake ba in fact ni tsorona ma karka rasa aikinka."


Jalal yasaki wata dariya yace " I wish zasuyi tsautsayin korata daga aiki, dana nuna musu shayi ma ruwa ne."


Sagir ya kalleshi da alamar tambaya yace " kamar ya?"

Jalal ya had'e hannayensa ya fara takawa yace kai kana tunanin in suka koran daga aiki ban musu laifin komai ba zan barsu haka? Takarda zan tura harsai sun sanar dani menai dana cancanci kura, in ba haka ba su amsa k'iran hukuma."

Sagir yasa dariya tare da tafi yace " Jalal kenan u are really smart suma nasan bazasuyi wannan gangancin ba, amma dai duk da haka ka kula."


Jalal ya juyo yace " nagode Sagir amma please in ba inda zaka aramin motarka yanzu zan dawo.
Sagir ya mik'amai batare da yace komai ba, Jalal ya amsa tare da godiya ya fita.





Seemah ta isa inda Ammar yake, sunje shiga daidainan wani babban mutum ko ince d'an siyasa babba, ya fito tare da mutanensa da 'yan goya kai baya, Seemah ta kalleshi baifi sa'an dad ba amma ko ba'a fad'a ba kasan d'am siyasa ne, idanta ta d'auke daga kansa sai dai maganar dataji ne yasa ta maida hankalinta da kallanta gun.

D'an siyasan nan taji yana fad'a kamar zai yanka mutanen dake gun, mamaki abin ya bata ta kara dubawa dawa yake fad'an? Wani dattijo tagani a tsugunne yana rokarsa jitai mutumin yace " wai ku mutane wasu irin dakikai ne? Sau nawa ina sanar dakai za'a baka kud'in gidan ka? Nifa banasan hauka kuma wlh karka kuskura ka kara zuwa inda nake, in banda darajar kai tsoho ne da tuni nasa an d'aureka."


Tsohon sai hannu yake had'awa alamar ban hakuri, sam Seemah batajin ke yake cewa da alama ma baya iya magana da karfi saboda tsufa, tsaki tai tace " na tsani mutane irin wannan dabasu san darajar tsofaffi ba aikin banza kawai......

Ta juya wasu 'yan jarida ne suka shigo cikin harabar hotel d'in securities na cemusu su tafi amma ina....sai da suka karasa gun wannan mutumin, Seemah ta juya ta kallesu, da mamaki ta kara kallan gun me zata gani? Wannan mutumin daya cima tsohon nan mutunci tagani ya kama hannun tsohon yama bashi hakuri, ga 'yan jarida nata d'auka, da mamaki ta kara kallansu, mutumin taji yace " Baba kayi hakuri munanan muna kok'arin yanda zamuyi kud'inku su fito amma ga wannan, batasan nawa ya mik'a ba amma tasan kud'ine masu kauri, mutumin taga ya kara kankame hannun babban harda kwallarsa wai Baba ka yafe mana, mukanmu mumajin tausayin halin da kuke ciki, ko bacci bana iyayi saboda tausayi.


Seemah dariya tasa tace " what? Me nake gani? Wannan wani irin mutum ne? 2 face? Ahhhhh yau naga abinda ban tab'a gani ba, harara ta maka mai duk da baimasan tanayi ba ta karasa ciki, tana tafe itakad'ai tama masifa.



D'akin da Ammar yake ta jarasa tare da danna kararawa, bata dad'e ba Ammar yazoya bud'e d'an ya d'auka masu aikin hotel d'in ne, ganin Seemah yasa ya tsaya kawai yana mata kallan mamaki, itama kallam mamaki take mai ta sa hannu akan fuskarsa yace "yaya menene haka? Meya sameka?"


Ammar bai amsa mata ba ya koma ciki tare da komawa karshen bango ya zauna, kamar yanda yake d'azu, Seemah da sauri ta karasa kusa dashi tace " yaya menene hakan?"


Bai ko kalleta ba bai kuma amsa mata ba, Seemah mamaki ya kara kamata ganin yanda duk ya canza a daren jiya yasa ta matso gabanshi tasa hannayenta akan fuskarsa idanunta suka ciciko tace " Yayana menene?"


Kallanta Ammar yai sai dai duk yanda yaso ya mata magana ya kasa, hawaye ne suka sauka a idanunsa, itama hawaye suka zubo mata tace " yaya wani abun ne? Please ka fad'amin."


Tafad'a tare da kallan d'akin, da alama ko kan gadon bai hau ba gashi kuma kamar abincin ma da aka kawomai d'azu ma bai ciba.



Kallansa tai da mamaki, bata tab' a ganin Ammar haka ba, mutum mai barkwanci? Mik'ewa Amnar yai kawai ya shiga toilet ta bi bayansa da kallo tare da share kwalla, wayarsa tagani akan gado da sauri ta k'ira Dad sai dai bai d'auka ba, ta kira junaid yace mata zai kirata yana aiki ne, haushi ya isheta gashi ita bazata k'ira Habib ba, da sauri tasa number Jalal.



Jalal kam har ya iso gidan yana shirin fita daga mota wayarsa tai kara ya d'aga jin muryar Seemah yasa ya koma ya zauna tare da cewa "Meemah ina kika shiga nakasa samun layinki? Do u know how worried am I?"


Ajiyar zuciya tai sannan taxe " My deen ina nan Nordic sai dai narasa meke faruwa da Ya Ammar yak'imin magana gashi duk ya canza."

17 / 37