JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   26 / 37

75K to 78K   out of 109.4K words

to sai dai ku fita da gawata."

Mutumin ya kalli Jalal yai murmushi yace " I wish kayi karatun Soja da anyi jarumi."
Jalal ya juya kai, mutumin ya cigaba sai dai inhar baka tafi ba zakuwa a fita da gawarka.

Jalal ya kara dakewa tare da jingina da katangar gun, ran mutumin ya b'aci ya d'aga kasan bindiga zai bugama Jalal, sai sukaji karar horn, da sauri suka jeru aka bud'e gate, motoci uku ne suka shigo Jalal ya kalli motocin har sukai parking sannan wata yarinya ta fito daga motar sanye da riga da wando sun matseta, tana tafe tana jijiga kai alamar rawa, Jalal yaja karamin tsaki yace "Allah ya shirya."
Juyowa tai d'an taji alamun kamar ana kallanta caraf suka had'a ido da sauri Jalal ya d'auke idanunsa, d'an takaici aransa yace "yanzu wannan kanwar Seemah ce fa ko?"

Baisan tazo kusa dashi ba sai jiya tace " waye wannan?"
Securitin ya kalli Jalal yace " Sorry madam."
Yanda take magana ma ya tabbatar ma Jalal ba'a hayyacinta take ba, ta nuna Jalal tace " Kai."
Jalal ya kalleta tare da girgiza kai yarinya karama dabata wuce shekara 18 ba amma.......
Zata sake magana taji daga saman beni ance "Me kikeyi anan?"
Da sauri Jalal ya d'aga kai, baban mutum ne da dukda baikai su Abba ba amma kasan baba ne, Jalal ya kara cusa ido ya kalleshi tabas mutumin da yake nema ne.
Dabara ce ta fad'o mai,
Yarinyar zatai magana Jalal da karfi yace " Sannu Dad dama cewa tai inzo gunka akan maganar soyayyarmu."

Securities suka kalleshi da mamaki itama ta juyo duk da a bige take ta nuna shi sannan ta nuna kanta, murmushin rainin hankali ya mata yace " Ko Sweety?"
Kai ta d'aga sannan ta kalli Mahaifinta wanda ransa yai mugun b'aci yace ku shigo ciki.
Jalal yai wani murmushin rainin hankali sannam ya kalli Securities d'in yace " Sorry bansanar daku da wuri ba."








Fatan Alkairi gareku " _*MUM HAMRA, MOM FARHAN, FRESH, AGRA, RAHANCY DA MOM FAROUK*_ "
Hope anyi weekend lafiya.......=?
?=?
?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


*This page is for you Ramalurv......*=?
?=?
?=?
?=?
?


No. 5? 5?

_I am really sorry jiya da shekaranjiya kun jini shiru, wani uzuri ne ya hanani typing. ......luv u ol_



Jalal ya kalli yarinyar ya mata wani murmushi yace " muje ko? Ta kalleshi sai dai idanunta nuna mata wani guy datakeso yake, hakan yasa ta d'aga kai da sauri tare da natsowa tana k'okarin kamamai hannu, Jalal yad'anyi baya tare da cewa "kiyi gaba ina binki."

Tad'an tab'e baki kafin tai gaba, wani tafkeken falo ta bud'emai ya shiga da sunan falon baki sai dai duk dakiya irin ta Jalal sai da jikinsa ya amsa d'an kyan falon ya wuce inda mai karatu zaiyi tsamani, ta nuna mai kujera, Jalal ya zauna tare da karabin falon da kallo, sam ya shagala baiyi tsamani ba yaji mace ta zauna kusa dashi tare da sakalo hannunta, zabura yai ya mik'e cikin mamaki yace "me kike yi hakan?"
Ta tab'e fuska kamar zatai kuka, jitai ance tashi ki shiga ciki, atare suka kalli mai maganar, ta mik'e tana layi tai ciki shikuma Jalal ya sake kuramai ido.

Har mutumin yazo ya zauna tare da kunna tv Jalal na tsaye sai da yace " zauna mana."
Sannan Jalal ya farga tare da zama a kasa, yace "Ina wuni?"
Mutumin bai amsa ba yabi Jalal da wani kalan wulakanci sannan yace "kaine kesan Huda?"
Jalal a ransa yace Huda sunanta?
A fili ya d'ago ya kalleshi, zaiyi magana taji yace " Naji dad'i dana ganka haka, dama nafisan talaka wanda yake nema, yanda duk abinda na gindaya mai dole ne yabi, d'an haka ka sanar da iyayenka d'an nima na gaji da wannan iskancin nata da jamin magana datakeyi, a d'aura muku aure sai in turaku Australia kuje can kuzauna har karshen rayuwarku."


Jalal ya d'ago ya kalleshi da tsananin mamakin kalaman fayake furtawa a matsayinsa na mahaifinta.

Daurewa yai tare da cewa " niba saurayinta bane sannan ni maganar danazo ma da ita......."
Jiyai an katseshi da cewa " what? Kaikasan ko ni waye zaka rainamin hankali? Da kace gunta kazo yanzu kuma me? Ko dama ba da aure kake santa ba?"
Ya mik'e yana kare ma Jalal kallo, Jalal ya dake tare da d'agowa ya kalleshi yace" akan maganar d'aya babbar 'yar taka nazo."
Kallan mamaki yamai yace " Da alama bakasan ma mai kazo yi ba, bayan huda ragowar kannanta maza ne guda uku sai karama yanzu wacce ko shekara 4 bata kai ba." Cikin takaici ya fara kokarin juyawa.

Jalal gani haka yasa yai saurin cewa " Ka manta Fatima ne? Ta garin birnin/gwari?"

Da sauri ya juyo ya kalleshi idanunsa suka kad'a da sauri ya dawo kusa da Jalal ya d'agoshi tare da rik'emai kwalar riga cikin fad'a yace " Who are you? D'an jarida ne kai?"
Har zuciya Jalal yaji tsoro sai dai da ya tuno Seemah sai ya dake yace " Ni ba d'an jarida bane, Sunana *JALAL* D'an gidan Amadu mai shago dake garin birnin/gwari."

Sakeshi yai sannan yace " What?"
Jalal ya gyara tsayuwarsa, yace " 'yarka tananan lafiya agun mutumin da kuka ma sharri ya rik'eta, sai dai ko bata fad'a ba nasan itama tanasan ganin mahaifinta."

Wata mahaukaciyar dariya Jalal yaji an fara mai kallan Abdul yai cikin tsoro, Ya dad'e yanayi kafin ya tsagaita yace " What?'ya ta?" HA HA HA HA
Ya cigaba " ko a da ba 'yata bace banga dalilin dazaisa yanzu ta zama 'yata ba."

Jalal yai ajiyar zuciya tare da komawa ya zauna a kasa, yace " ka manta Fatima fa wacce kuka ketama......."
Tsawa ya dakamai yace " na keta mata ko Isma'il ya keta mata?"
Jalal ya d'ago cikin mamaki yace " me yasa kana babba kakesan take gaskiya? Me yasa bakajin kunyar karyata abinda kasan tabbas shine gaskiya?'
Ya kalli Jalal yace "in ma turo ka akai ko d'an kanka kazo sai ka kama hanya ka fita, duk duniyar nan banga wanda zaizo ya wargazamin harkar siyasa ta dana shiryata da gumi na ba, dan rainin hankali sai da nakai wani matake sosai ina shirin kara hawa sama shine zakazomin da zancen banza d'an kasamin bak'in jini gun mutane? Da can bakuzo ba sai yanzu?"
Ya nuna Jalal da yatsa yace " Wallahi kaji ma fad'ama ba 'yataba? Ba kuma matata ba ko mahaifiyata bata isa ta kawomin cikas a harkar siyasa taba in kyaleta bare kai da wata yarinya daban ma santa ba, in kud'i takeso kaje kace ta fad'i ko nawa ne, Ni Abdullahi nad'au alkawarin ba ta."


Jalal wani irin kallo yake binsa dashi na tsananin ban mamaki da kuma tsoron furucinsa, wani irin mutum ne wannan? Siyasa ce ta maidashi haka ko kud'i ne? Ko kuma dama can haka yake?"
Kafin Jalal ya k'okarta yai magana haryakai bakin kofa, Securities ne suka shigo suka kalli Jalal sukace " fito ko mu fitar dakai."
Jalal ya kalli mutumin cikin takaici ya dake ya matso kusa dashi kad'an yace " Wallahi kaji na rantse maka in dai ina raye sai ka tsuguna a gaban Seemah ka nemi yafiyarta da abinda kama mahaifiyarta, idan kafi karfi na ai bakafi karfin hukuma ba, Allah kuma na tare dani kajira ka gani."

Dariya Abdul yai tare da zaro 'yan bandir d'in dubu d'aya ya mik'amai yace " Daga kai har yarinyar har hukumar bakufi karfin wannan ba."

Jalal cikin takaici yake kallansa ya kakaro murmushi yai sannan yace " in kafi karfin hukuma ai baka fi ta Allah ba."
Yana kainan yai waje.

Ko securities d'in bai kula ba ya fita, kafa kawai yake sawa, yana tafe yana mamakin abinda idanunsa suka ganemai, kuma kunnensa suka jiyemai, a hankali wasu kwalla suka zubo mai, a fili yace " Seemah ya zamuyi?"




Seemah kam tana zaune a kan gado rik'e da waya, tarasa abinda ke mata dad'i, d'azu Zaid yazo yace mata wai za'a sanya musu rana da Ammar, itakam ta rasa mema zatayi, motsin bud'e kofa ne yasa ta kalli kofar, Dad ne ya shigo tare da sallama, ta amsa tana neman kakaro murmushi, ya karaso kusa da ita ya zauna tare da kamo hannunta yace " me kikeyi anan bayan kowa na falo?"
Tai kasa dakai batare da tace komai ba, yai murmushi yace " Kinji labari?"
Da sauri ta d'ago ta kalleshi tace " name fa Dad?" A ranta kuwa addu'a take Allah yasa ba zancen Zaid yake nufi ba.
Dad ya sake murmushi tare da shafa mata kai yace " burina ya kusa cika Seemah, babban burina bai wuce inga kin auri d'aya daga cikin 'ya'yana ba, na sani kuma kowa ya sani Ammar ne yafi dacewa dake, shiyasa nakesan ki daure kicire san Jalal a ranki."

Seemah jitai kafarta na rawa da sauri ta hawuda ita kan gado kar Dad ya gane, ta kakaro murmushin yake sannan tace " Dad nasani ya Ammar zai kula dani sosai. "

Dad yasa dariyar farin ciki yace " ko? Ashe kema kinsani, shiyasa muka yanke za'a samuku rana sai mukoma ki karasa karatunki sai ai auren."
Tai murmushi tare da cewa hakan yayi Dad, burina bai wuce inga nasanyaka farinciki ba."
Takarasa maganar cikin rawar murya.

Dad ya jawota jikinsa yana lalashi, yace "kicire komai a ranki ki koma yanda kike da nakuma gode sosai da amincewar da kikai."

Ta d'ago tare da girgiza kai tace " nice da godiya Dad koda ace zan bauta maka har karshen rayuwata banaji zan biya kwatan abinda kamana nida mahaifiyata."

Dad cikin wasa yace "oh ni Seemah yaushe zaki daina maimaita abin nan?"

Tai kasa da kai tana murmushi ya mike ya fita ta bi bayanshi da kallo tare da cewa "Deen yazanyi?"



Jalal tsaye a kofar gidan Abba yanaso ya musu gaisuwa sai dai inaaa kunyar ma shiga yake in ya tuna abinda ya faru, gani yai an dalleshi da fitila, hannu yasa yad'an kare fuskarsa, a hankali mai fitilar yazo kusa dashi ya nuna shi da yatsa tare da kwashe wa da dariya yace " I am right kaine." Yafad'a tare da nuna kansa alamar naushi.
Jalal ya kalleshi sannan yai 'yar dariya yace" ashe baka manta ba."
Zaid yace " ya za'ai in manta bayan an nemi a gurd'eni?"
Jalal yace " Kayi hakuri time d'in....."
" baka hayyacinka ne saboda kishi ko?"Zaid ya karasa mai.
Jalal yai murmushi baice komai ba, Zaid ya rik'e hannunsa yace " muje ciki kuyi sallama da Seemah an kusa sa mata rana."

Bawai baiyi tsammanin ranar zatazo bane, bawai kuma tsoron hakan yake bane, bawai kuma baisan hakan a faru bane a'a shi aganinsa hakan ne daidai sai dai jin kalmar ya sa ya ja burki ya tsaya, gabansa ne yashiga fad'uwa, idanunsa suka canza kala, Jalal ya daure yace " dare yayi mubari sai gobe nazo."

Zaid ya haska agoggon hannunsa yace "karfe 8 da rabi shine dare? Tab lalai inbaka gantaba yau banaji zaka kara samun wani lokacin."

Jalal ya kalli Zaid sannan cikin sanyin murya yace " muje."

Yana tafe yana " *_INALILAHI WA INA ILAHIHI RAJI'UN_*" har yai sa'a gaban nasa ya daina fad'uwar.









? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 6?



Jikin Jalal yai sanyi haka suka shiga gidan, Zaid yace " ka ga ka nausheni ashe kaima gaba kai za'a nausa?"
Jalal yai murmushi yace " hakane dama, to amma karfa mu shiga cikin gidan ka d'inga cewa na nausheka."
Dariya Zaid yai yai alamar zip a bakinsa, Jalal yai murmushi, sun shiga falon mami, mata me 'yan uwa a zaune, nan Jalal ya tsugunna kansa a kasa ya gaishesu, suka amsa suna kallansa, ya musu ya hakuri, Zaid ne ya kalli mami yace " mami kin ganeshi? Jalal d'in........"
Kafarsa Jalal ya mintsina da karfi, Zaid yai 'yar kara tare da kallan Jalal, da sauri ya mik'e yace " Sai da safenku."
Ya fad'a yana kallan Zaid, muryar mami suka ji tace " Ka kaishi ya gaida su Abbanka."
Jalal ya kalleta jiki a sanyaye, da alama ta ganeshi tunda sun had'u a asibiti, Zaid ya kalli Jalal yace muje ko?
Nan suka wuce falon Abba, a hanya Jalal ya kalli Zaid yace " d'azu mai kake san fad'a?"
"AUUUU wannan? Hmm dama cewa zanyi Jalal d'in Seemah in na fad'a za'afi ganewa."
Jalal ya kalleshi cike da mamaki yace " mene? Jalal d'in Seemah?"
Dagewa yai ya takamai kafarsa da karfi Zaid sai da yai 'yar kara yace " Wai ni menai?"
Girgiza kai Jalal yai yace " lalai Zaid mema kai kake tambaya? Da alama........."
Ammar ne ya karaso gun yana cewa " Zaid meye hakan?"
Ya fad'a yana kallan wanda ke tsaye, kalan kallo suka shiga yi, Jalal ya daure tare da mik'a mai hannu, Ammar ya mik'amai shima suka gaisa.
Jalal ya kalli Zaid sannan ya kalli Ammar yace " Gaisuwa nazo."
Gyad'a kai yai alamar gamsuwa sannan ya nuna mai kofar falon yace " muje?"
Nan suka shiga su uku tare da sallama, Abba, Dad, da kawu suna zaune a falo ga Junaid a kasa da alama nasiha ko fad'a ake mai, jin sallama yasa suka amsa, Junaid ya kalli Kawu yace " Zan rik'eta amana insha Allah."
Yana kainan ya maida kallansa kansu Ammar, Zaid ne ya fara shigowa, sai Ammar sai Jalal a baya, dukansu suka canza fuska shikam Junaid kallan Jalal yai nan suka karasa suka zauna a kasa.
A hankali Jalal ya gaidasu, suka amsa kamar basa so, ya musu ya hukuri, nan ma suka amsa kamar d'azu, sunyi shiru a falon kafin Junaid yace " daga ina?"
Jalal ya kalleshi suna kamada ya Habib hakan yasa ya gane shine d'ayan yayan Seema, mik'ewa yai a hankali ya dawo sautinsu Dad a hankali yakai gwiwowinsa kasa, kallan mamaki suka mai, idanun Jalal suka cicoko ya d'ago a hankali ya kalli Dad yace " Nasani banida bakin magana, bankuma san da wacce kalma zan fara ba, da ace abin bai faru bane shine zan sami karfin gwiwar yin magana." Yai ajiyar zuciya sannan ya cigaba" na sani dani da mahaifina bamu da bakin da zamu nemi yafiya daga gareku, sai dai.......sai dai....."
Hawaye ne yafara zubomai hakan yasa ya kasa karasa maganar, kansa ya durkusar a kasa yana hawaye sosai, dukansu tausayinsa ya kamasu, Junaid ma ya gano shine Jalal d'in, Dad yanasan Jalal tunsanda aka haifeshi, ganinsa cikin wannan yanayi yasa shikansa yaji idanunsa sun ciciko.
Ammar mik'ewa yai yaje kusa da Jalal a hankali yace " Tashi mu tafi."
Jalal ya runtse ido, ba tare da ya motsa ba, Ammar ya kalleshi cikin tausayawa, Zaid ne ya mik'e shima ya kalli Jalal yace " Katashi ka tafi Jalal."
Nan ma bai motsa ba, Zaid ya kalli su Dad cikin b'acin rai d'an shi baisan meya faru ba, yace " Abba shiya muku laifi? Me yai? Meyai muku da zai tsugunna yana neman yafiya amma dukanku ku shareshi? Bayan yarinyar dayakeso take sanshi kun......"
Da karfi kuma cikin tsawa Jalal yace *ZAID* kowa sai da ya kalli Jalal, Zaid a zuciye yai waje, a zahiri shikam ya kasa gane menene dalilin dazai sa a hana yarinya yaron da takeso.

Jalal yai ajiyar zuciya tare da kara share hawayensa ya kakaro murmushin da kana gani kasan na bakin ciki ne ya kalli Dad yace "Dad an d'auramin aure."
Kallan sa sukai su dukansu, ya sake murmushi sannan ya kalli Ammar yace " Ammar ina tayaka farinciki, naji an kusa sa rana."
Ya sake wanni murmushin tare da goge kwalla ya maida kallansa kansu dad yace " Dad Allah yasanya alkairi, naji dad'i."
Hawaye suka kara zubomai, yace " Bakomai in har zuciyarka bazata iya yafemin ba, na sani wannan wani gyambo ne da ke zuciyarka, tunda Amininka ne ya cuce ka."
Yai murmushi har hakoransa suka fito, ya share hawayensa sannan yace " Amma nikam a kasan zuciyata nayi tunanin wani abu guda d'aya, naji dad'i daya kasance kaine ka raini Seemah har kawo wannan lokacin, da Allah ne kad'ai yasan wace rayuwa zatayi a gidan wannan mutumin da zuciyarsa ba imani."

Ya share kwalla sannan yace " in na duba abin ta fuskar daya kamata sai inga Allah ne ya taimaki Seemah......."

Dukansu tausayin Jalal ya ratsasu sosai, dan Dad sai daya kauda kai ya share kwalla a fakaice, Junaid ma idanunsa sun ciciko, Ammar kam shima hawayen yakeyi, a hankali Abba yace " Kasan mahaifinta ne?"
Jalal ya kalli Abba yana hawaye yace " nasanshi, sai dai ba amfani a sanin nashi."
Dad ya mik'e yazo kusa da Jalal yace " Me kake nufi?"
Jalal yai murmushin takaici yace " Dad karka damu, bazan iya fad'a muku ko waye a wannan lokacin ba, sai dai nama Ammar alkawari, kafin a d'aura masa aure da Seemah sai mutumin nan yazo da kansa yaba Seemah hakuri koda kuwa hakan shine zai zamo abu na karshe dazanyi a rayuwa ta."


Dad ya kalleshi cikin tsananin tausayawa, Ammar ya share kwalla ya kalli Jalal yace " kar ka kuskura kayi abinda zai jama matsala a rayuwa da sunan alkawari."
Jalal yai murmushi, ya mik'e yazo kusa da Ammar ya dafashi, baice komai ba yai hanyar kofa.


Zaid kam yana fita gun Seemah yaje, tana zaune da waya tana rubuta sunan Jalal sai ta goge, ta

26 / 37