JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   25 / 37

72K to 75K   out of 109.4K words

kuma shi ke san ganinta ko saboda wani abu, na kalleshi nace " Chairman kayi hakuri yanzun nan zata koma gida......."
Kafin na karasa maganata naji an kifamin mari, da sauri na kalli wanda ya naren d'aya daga cikin abokan Abdul d'in ne nace " Kai meye hakan kuma?"
Wanda ya maren d'in yace " Wai Abdul kai wani irin mutum ne? Ya za'ai kana Matsayin Chairman ace wani banza mai shago har zai kalleka yad'inga ma tambayar banza? Banace ka barni nai handling d'in komai ba? Kobakasan ka d'ana ne?"
Abdul ya kalleshi ga mamakina kamar me tsoransa naga yaja baya, daidai nan cikin rashin sa'a ashe d'ana na kallanmu d'an muna kusa da shagon, ganinsa mukai yazo tare da kallan wanda ya maren d'in yace " Malam me Babana ya maka?"
Wata muguwar dariya ya saki sannan yace " Good haka nake so."

Ban kawo komai a raina ba kawai sai gani nai an cafke min d'ana, an kuma samai wuka a wuya, nan fa ya shiga kuka.
Na rikice sosai, kuka yakeyi sosai nima na shiga rokonsu,dariya suka samin na d'azun da ko sunanshi ban sani ba ya cilla ma wani d'an nawa tare da matsowa kusa dani yace " karkuma kai tunanin wannan ne kad'ai matarka tana hannunmu, ahh abin tausayi ko?"
Sannan ya kalli Abdul d'in yace " kayi tafiyarka ko itama tafi karfin ka?"

Abdul ya girgiza kai yace " ai ko d'aureta ne sai nayi, ina gani ya nufi shagona ina ihu akan karyayi.......

Kallansa nai duk na gana rikicewa nace d'an Allah kuyi hakuri, karku lalata mata rayuwa. Naga tashin hankali a lokacin kuma abin da yaban mamaki ba wanda yazo wucewa, gashi kamar sun tambaya, ba wutar nefa gashi dama a lokacin ba gen ake kunnawa ba.
Dariya suka samin dashi sannan aka kwad'ama d'ana k'otar wuka a goshi wani ihu yasa kawai sai ga jini kankace mai......

Kuka nake sosak, suka cemin matarka da alama bata ma da lafiya ko? Na d'ago da mamaki d'an ko ni ban sani ba, suka kwashe min da dariya sukace dataji azaba cemana tai wai muyi hakuri karmu bari abin cikinta ya zube.


Nan na matso tare da rik'e kafafunsu, tashin hankali ne ya karune a sanda suka fito da bindiga, suka nunani sannan suka nuna d'ana sannan sukace " kaje ka k'ira ma Fatima wanda take jira kayi sauri kafin Abdul ya mata ila."
Na d'auka tausaya mata sukai hakan yasa da sauri na wuce na tadda ana fitowa daga masallaci nan na gyara fuskata na shiga cikin masu fitowar, Isma'il na gani na d'aure na sanar dashi Fatima na nemansa na gaggawa.

Mun taho gabana sai faduwa yake, muna zuwa zan shiga sai naga sun min alamar inzo, hakan yasa Isma'il ya shiga shi kad'ai ni kuma na je gunsu, sukamin tafi sukace yauwa ka kyauta.
Na kallesu nace d'ana fa? Mugun ya tab'e min baki sannan ya kalli Abdul da nima sai a lokacin na kalleshi yanasa wando, zaro ido nai nace " meke faruwa?"

Hoton D'ana aka nunomin an saitashi da wuka sannan matata ansaita ta da bindinga, sukace abu d'aya zakai ka cecesu.
Kuka nake sosai ina rok'onsu, ban farga ba kawak naji karar mutanen gari, sukace cewa kawai zakai Abokinka Isma'il shiya mata fyad'e.

Girgiza kai na shigayi ina kuka, mugun yace " to shikenan ka taimaki abokimka in yaso matarka da d'anka, da wanda ba'a haifa ba kwa had'u a lahira.

Abba na zuwa nan yai share hawayensa, Umma ma haka, Jalal kam kukan ya kafe kaf kawai Abba yake kallo wani irin kallo daban fahimceshi ba ni kaina.
Jinai cikin wata irin murya Jalal yace" Saboda tsoron kar ama matarka da d'anka ila yasa ka ce Amininka ne ya mata fyad'e?"
Abba ya kalli Jalal sannan ya kara goge kwalla yace " Akan d'ana ba abinda bazan iyayi ba, ina ganin ansama d'ana wuka za'a yankashi mezai sa inkasa fad'ar kalma d'aya?"

Jalal ya mik'e ya shiga jijiga kai sannan ya kalli Abba sai a lokacin wasu zafaffen hawaye suka fara zubo mai, Abba ya matsu tare da kokarin rik'e hannunsa Jalal yayi baya.








? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM.*


*Gaisuwa ga duk Masoyan littafin nan ....I Luv u Ol*d'=?
?=?
?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com



_*This Page is Dedicated to you ? wish u ol the best in ur Exams..... Thanks once again*_

No. 5? 3?




Jalal jikin bango ya jingina a sulale ya tsugunna hawaye ke malala a kuncinsa, Umma dake zaune itama tana kuka ta taso ta matso kusa dashi tace Jalal! Wani irin kara yayi da duk sai da suka tsorata kuka ya wuce da shi kamar wani karamin yaro, Umma tsoro ya fara kamata ta kalli Abba tace " Meyasa ka fad'amai? Yanzu in wani abu ya sameshi fa?"

Abba ya kalleta cikin wani yanayi, yace " daga sanda Isma'il yazo gidan nan nasan ban isa in b'oye sirrin nan ba, da wani a waje ya fad'amai mahaifinsa yaci amanar Amininsa gwara ni dakaina insanar dashi. "

_Nikaina Ayusher yanda naga Jalal na kuka sai da naji hawaye ya zubomin a hankali nayi waje d'an bazan iya zama ba._


A b'angaren Seemah kuwa bayan mutane sun ragune Ammar ya shigo d'akin, ya kalleta a rak'ub'e a gefen gado, tausayinta ya kara kamashi ya matso inda take tare da d'agata, kallanshi tai kamar wacce hankalinta baya jikinta tace " Ya Ammar am d'aura ko?"

Kallanta yai idanunsa suka ciciko, hannu yasa a kafad'arta yashiga jijigata yana cewa " Get hold of your Self Seemah, please. "

Ya d'ad'e yana jijigata kafin ta kalleshi tace " Yaya ya zanyi?"
Yace " Seemah England zamu koma ranar bakwai inajin shi kad'ai ne zai sa ki manta komai."
Ta d'aga kai tace " na yarda Yaya ni kaina haushin kaina nakeji."

Nan ya mike yai waje, bai dad'e ba sai gashi ya dawo rik'e da plate na abinci, Zama yai kusa da ita tare da d'ebo abinci a cokali da niyyar ba ta, ta kalleshi sannan ta amshi cokalin tace " Zanci da kaina Oppa."

Murmushi ya mata sannan ya mik'a mata spoon d'in, ta fara ci, yace " Matar Dad tazo ta dubaki?"
Ta d'an tab'e baki har zatai maganar rashin kunya ta tuna ashefa ta fita matsayi yanzu, tai kasa dakai tare da cewa " Ta l'eko d'azu."
Ammar yai d'an karamin tsaki yace " bansan ya akai Dad ya aureta ba, sam batada kara."
Seemah tai shiru can tace " Ka manta Yaya? It is all my fault, bakaji Dad nacewa saboda ni ya aureta ba? Na sani saboda yanaso akula da......."
Kasa karasawa tai saboda hawaye, Ammar ya kallera yai murmushi yace " Oh yazanyi da wannan kanwar tawa mai saurin kuka?"

Ta kalleshi tare da share hawayenta tace " Yaya?"

Yad'an rangwab'ar dakai yace " Seemah rufe idonki."
Ta kalleshi tad'an turo baki kad'an, sannan ta rufe, hannu yasa a aljihunsa, sannan yace "bud'e."
Da sauri ta bud'e tanasan ganin menene, kwalin waya ya mika mata, ta kalli wayar Iphone 6 ce, tace " yaya inafa da waya?"

Yace " Dad ne yace kar abaki waccan."

Tai murmushi sannan ta amsa tace " Thanks Bro."
Yai murmushi shima yace " Ahhh naji dad'i kinyi murmushi, sannan kinci abinci."

Ta kalleshi tace " saboda Deen ne ba'asan abani d'ayar wayar?"
Ammar ya kalleta bai amsa ba, ta kara murmushu tace " karkadamu yaya, yama za'ai in sake ganinshi? Sannan bazan bari effort d'inka ya tafi ba yanda kasa naji zuciyata tayi sanyi ba."

Ammar kallanta kawai yake, ta kara sakar mai murmushi sannan ta hure mai ido tace " Yaya kallan fa?"

Mik'ewa yai da sauri tare dasa hannu a aljihu duk ya rikice yace " Ehem dama dama fita zan d'anyi, nan zafi ko bakya ji?"

Batasan sanda tasa dariya ba, tace " Zafi kuma yaya? Nan d'in?"

Kallanta yai yace " Seemah just now dariya kikai ko? Badai hallucination na gani bako?"

Tai kasa dakai tana murmushi tace "kai yaya kai d'in ne wai zafi."

Kallan yanda take murmushi yasa ya farajin zafin na karuwa, da sauri yai waje, yana fita daga d'akin ya fara furzar da wata iska yanacewa " Cool down Ammar."

Can kuma yace " meke damuna?"

Junaid ne ya dafashi yace " Ammar agidan gaisuwar ba kunya kake soyayya?"

Kallan Junaid yai a tsorace, Junaid yai murmushi yace " Ya Habib ya fad'amin komai karka damu."

Ammar yai ajiyar zuciya sannan ya kuma kalleshi da mamaki yace " ban gane soyayya ba kuma?"
Junaid yace " in ba soyayya ba me kake a d'akin?"
Ammar ya kalleshi da mamaki yace " What? Seemah ce fa a d'akin."

Junaid ya d'an jinjina kai yace "ai sanin Seeman ce yasa na fad'a, Ammar ka nutsu ka tambayi zuciyarka, wacce irin soyayya kake mata?" Junaid na kainan ya juya yai gaba yabar Ammar da binsa da kallo.






Jalal kam bayan su Abba sun fita yana nan dai a gun da yake, ya dad'e agun kafin ya daina kukan, yafara cewa " ya zanyi Seemah?"

Jin ba amsa yasa yai shiru can yace " Abdul?"
Cikin zafin nama ya mik'e yai waje, a waje yaga Abba, Abba na ganinsa wani dad'i ya kamashi da alama harya sauko kenan, Jalal ya kalleshi cikin d'aure fuska yace " Abdul d'in yana ina yanzu?"


Abba ya girgiza kai yace " Jalal ka rufamin asiri d'an Allah wannan mutumin yafi karfin mu bani ba har Isma'il d'in dayake da kud'i."

Jalal ya kalli Abba yace " Abba ina Abdul d'in yake yanzu? Dole ne ya nemi yafiya agun Seemah da iyayenta, kaima kuma Abba dani dolene mu nemi yafiya, duk da ba lalai a yafemana ba, wayasan wace irin rayuwa suka shiga akan kalaman nan guda d'aya?"




Abba ya kalleshi a tsorace yace " Jalal ninaji zan bada hakuri ko mai za'amin bazan damu ba amma Jalal ba ruwanka da harkarnan, dama tun farko baka san komai ba, d'an haka yanzun ma ka nuna bakasan komai ba."

Jalal idanunsa suka ciciko yace " Me kace Abba? In nuna bansan komai ba? Taya zan iya?"
Hawaye suka zubo mai yacigaba " akan Mahaifiyar Seemah ne fa da kuma Wanda ya rik'eta kamar 'yarsa Amininka kuma."

Yai ajiyar zuciya sannan yai d'an murmushin yake yace " Tunda naji labarinnan nasan ban cancanci auran Seemah ba, ko da kuwa iyayenta zasu amince dani, Ammar shine ya dace da ita koda har karshen rayuwata zan kasance cikin tsananin begenta bazan kuskura inkara gangancin cewa ina santa ba."

Kalaman Jalal sun ratsa zuciyar Abba shima ya share kwallarsa yana kallan Jalal, cigaba da magana yai da cewa " Shiyasa nakeso ko ban aureta ba insamu in mata wani abinda zaisa ta rage tsanar datamin hakan ne zaisa ta manta dani."
Ya kara share kwalla sannan ya kalli Abba yace " Abba kataimakeni inma Seemah abu guda d'aya a rayuwar duniyar nan."

Abba bai san sanda ya rungume Jalal ba, yace " Jalal a koda yaushe ina alfahari dakai, kafi wannan mahaifin naka tunani mai tsawo."

Jalal idanu kawai ya runtse, shikad'ai yasan rad'ad'in dayakeji a ransa.












? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


No. 5? 4?


Jalal ya d'ago ya kalli Abba yace " Shugaban kasa ne shi ko me?"

Abba ya kalleshi yace "Jalal Sanate ne yanzu wanda kuma ake ji dashi haka kuma mutane na sanshi, ina tsorace maka abinda zai biyo baya."

Wata muguwar dariya Jalal yai wacce sai da abin ya tsorata Abba, sannan ya tsagaita yace " mene? Sanate? Wasu mahaukatan ne suka zab'eshi? Kuma shi ko kunya mutumin dabai san darajar d'an Adam ba harya iya cigaba da siyasa?"

Abba yai ajiyar zuciya yace " nidai yanzu kabar komai kaga gobe za'a kawo Zainab."
Jalal ya kalli Abba shi harya manta da wani auren Zainab, ya juya kai batare dayace komai ba.

Ganin haka yasa hankalin Abba yad'an kwanta, mutane mak'ota ne suka fara zuwa halan yasa Jalal ya koma ciki, shiru yai yana tunani can ya d'auko wayarsa yafara duba senate na kasa, kan wani yazo *ABDULLAHI UMAR*
Ya kalli hoton mutumin dakyau gabansa ne ya fad'i ba shakka wannan shine mahaifin Seemah bawai kama sukai sosai ba sai dai in har ka kalleshi ka kalli Seemah zakasan akwai alak'a ta jini sannan ga tarihinsa daya karanta, ransa yakai k'oluluwar b'aci sanda yaga yanda ake ji dashi da kuma yanda mutane ke masifar sanshi wasu har so suke ya tsaya a matsayin shugaban kasa na zab'e ma gaba.
Haushi ya ishi Jalal ya cilar da wayarsa kan gado sannan ya mik'e cikin zafin rai kawai wayarsa ya d'auka ya fita.

Tasha ya nufa kawai ya shiga motar abuja, sam idanunsa sun rufe.



Dad da Abba da kuma kawo ne zaune a d'aki, Abba ya kalli kawu yace "Wani hukunci ka yanke?"
Dad yai saurin cewa " Kawu nidai dan Allah kadawo nan da zama me zakayi a suleja yanzu? Dama can ba garin mu bane."

Kawu yai shiru cam yace " naji amma dai kai Isma'il kaima ina fatan kadawo nan da zama kenan?"
???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? Dad ya d'ago ya kalli Kawo sannam ya kalli Abba jikinsa yai sanyi, Abba yace " gaskiya kam ya kamata kaima ka dawo kazauna anan."

Dad a hankali ya furta "karatun Seemah fa? Ina tunanin yimusu baiko itada Ammar sai in koma can inyaso in ta gama karatun sai mu dawo gaba d'aya."

Abba yai shiru can kawu yace " naji bayananka sai dai nima na yanke nawa hukunci na."
Ya kallesu sannan yace " In akai bakwai d'in marigayiya nakeso wahsegari ai baikon Junaid da Ammar, in yaso sai ka d'auki matarka ku koma England har zuwa sanda zata gama karatu, da zarar ta dawo za'a had'a ayi auren."

Dad ya jinjina kai alamar gamsuwa sannan can ya kalli Abba sannan ya kalli Kawu yace " Amma junaid yanada budurwa ne?"
Nan Abba ma ya kalli kawu da mamaki, Kawu yai murmushi yace " ba wani taro za'ai ba saboda rasuwar da akai mana kawai dai za'asa rana ne a kuma bada kud'in gaisuwa."
Abba ya kalli Kawu yace " amma kawu......"
Kawu yai murmushi yace "Mahaifiyarku babban burinta bai wuce tayi had'in aure a tsakanin 'ya'yan ku ba, tunda shi Ammar yanada Seemah shiyasa nake tunanin had'a auren Junaid da Zahra."

Kallan juna Dad da Abba sukai, Kawu yace " na amince da auran Ammar da Seemah sai dai kamar yanda mahaifiyarku tace dole ne kafin ranar auren asan mahaifinta."

Dad yai murmushi tare da cewa gaskiya ne naji dad'in had'in nan, Abba ma yai murmushi.





Jalal sai bayan magrib ya iso Abuja, wayar Umma ce ta shigo sai alokacin ma yai tunanin ashe bai fad'a musu ba, da sauri ya d'aga wayar yace " Umma?" Tace " Jalal kana inane? Tun d'azu ana nemanka."
Jalal ya kalli cikin garin Abuja yace " Umma kiyi hakuri d'an Allah wani uzuri ne ya tasomin ina Abuja yanzu."

Tace " Abuja kuma?gobe fa za'a kawo Amarya."
Jalal ya runtse ido jin an anbaci Amarya yace " kiyi hakuri Umma."
Tace " naji amma ka tabbatar gobe ka dawo da wuri banasan mutane su fara zargin wani abun."
Yace "insha Allah." Nan suka kasje wayar.


Yana sauka yai sallah sannan ya nemi d'an machine yace " kasan gidan Sanate Abdullahi?"
D'an machine d'in ya kalli Jalal daga sama har kasa sannan yai dariya yace " kasan me kake cewa kuwa?"
Jalal ya had'e rai yace " mahaukaci ne ni dabazan san me nake cewa ba ko me?"
D'an machine yace " A'a muje inkaika." Aransa yace ko mai aiki ne a gidan?
Sun isa wata had'ad'iyar unguwa manyan gidajen dake gun da kuma tsarinsu zai tabbatar maka da guri ne manyan mutane.
A kofar wani had'ad'an dank'araren gida yai parking, Unguwar shiru kamar ba mutane, d'an machine ya juya yatafi bayan ya cemai nan ne gidan.

Jalal yabi gidan da harara yace " Dama irinkune masu hana kasar mu cigaba, kun tara zunubai a kanku kuma kunzo d'an yaudarar mutane."

Kofar Gate d'in ya karasa tare da tunanin ta inda zai fara, wani security ne ya fito tare da kallansa yace " me kake anan?"
Jalal ya kalleshi yace " Gidan Sanate Abdullahi ne?"
Mutumin ya kara had'e rai yace " eh amma kai waye?"
Jalal ya d'an daure tare da sa hannu a aljihu yace " nemansa nakeyi."
Security d'in ya jara kallansa yace "baka da hankali ne? "
Jalal yace " what?"
Nunashi da bindiga yai irin doguwar nan yace " waye kai?"
Nan fa idanun Jalal sukai tsuru tsuru, husur security d'in ya hura nan da nan wasu securities d'in suka fito, ya kalli Jalal yace " a dubashi da kyau ban yarda da shiba."

Jalal haka suka ririk'eshi suka shiga lalubamai jiki kamar yai ihu d'an bakin ciki, suna gamawa suka sakeshi tare da cewa " nothing suspicious Sir."
Ya kalli Jalal yace " tashi ka kara mai karkuma insake ganinka anan."
Jalal ya dake zuciyarsa yace " ganina kuwa dolene d'an bazan tafi ba harsai naga mutumin gidan nan inkuwa kuka hanani

25 / 37