JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   36 / 37

105K to 108K   out of 109.4K words

gangaroma Ammar yasa hannu ya cire yace " Dad ya zanyi? It's all my fault. "

Dad yai shiru yace " Ammar!"
" Dad."
Yai maganar cikin wata murya, Dad yasan halin Ammar da tausayi dafashi kawai yai yace " kaje gida nizan tsaya anan."

Kai Ammar ya girgiza yace " bazan iya tafiya ba Dad sai naga Jalal ya ware."
Kai Dad ya jinjina yace " to Ammar amma kaga dare yayi ga gobe karfe 10 za'a daura auren nan baka tunanin ya kamata kaje gida?"

Ammar yai shiru, can yqce " Dad in Seemah tasan Jalal bashi da lafiya ya zatai? Balle intasan ciwon a dalilinta ne?"

Dad ya kalleshi batare da yace komai ba, Ammar ya cigaba " Dad ya zatai?"
Kai?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? dad ya juya yace " Ai ba fada mata za'ai ba."

Ammar ya runtse ido sannan ya bud'esu idanunsa sun cika taf yace " Dad baka gani muna shiga hakkin ta?"
Da mamaki Dad yace " Ammar me kake nufi haka?"

Ammar ya had'iyi wannan abun yace " Dad babban bakin cikina aduniyar nan bai wuce inga Seemah cikin damuwar da harzai kaita gayin kuka, amma Dad kasan kukan da nasa Seemah ta dalilin yaron nan? Sau nawa ina ganinta tana kuka akan abinda baifi karfina ba ko ince akan abinda nine xan iya daidaitashi, amma haka nake ganinta tana kukanta bana iya tab'uka komai saboda wani buri na zuciyata."

Hawaye ne suka gangaro kumatunsa, ya kalli Dad yace " Dad nan!!!!"
Dukan inda zuciyarsa yake yai, da karfi yace " nan gun Dad ni kadai nasan ya nakeji inaga Seemah na hawaye, sannan ina tuna Sadaukar da rayuwarsa da Jalal yai saboda Seemah, kanwarsa batada lafiya amma baije gunta ba......"

Dad ya dafashi yace " Amma ai ita Seemah itama ta zab'eka."

Ammar ya girgiza kai yace " tadai zabi farin cikin ka ne Dad, yarinyar nan bataso ko kadan taji tama abinda bazai faranta maka rai ba ciki kuwa harda sadaukarwa da farincikin rayuwarta, na sani zan kula da ita, ina santa kamar raina sai dai nasan inda zuciyarta take , Seemah na bala'in sona amma son 'yan uwantaka takemin."

Dad yai shiru sai dai jikinsa yayi mugun sanyi yakasa furta komai.
Ammar yacigaba tare da share hawayensa yace " Dad duk farincikin da Seemah takeso nima inasan shi sai dai ina bakin cikin zuciyata tana neman canza min tunani na."

Dad ya kalleshi, Ammar ya tsaida hawayensa yace " Dad na tsaida solution gobe auren nan da Jalal za'a daura bazan iya ganin abokina da kanwata danafiso a duniya cikin damuwa ba nikuma ina farin ciki ba."

Kallan tsananin mamaki dad yamai yace " Ammar kasan me kake fada kuwa?"
Murmushi Ammar yai wanda kana ganinsa kasan na bakin ciki ne yace " Dad ka taimaketa ne saboda son da kake ma mahaifiyarta da kaunar da kake ma yarinyar ko?"
Dad ya daga kai tare da cewa " hakane amma...."
Ammar yace " ka taimakesu ne saboda Allah na sani Dad."

Dad yai shiru, Ammar ya cigaba " in har munaso ladanmu ya karfafa agun Allah mu bawa Jalal Seemah sai kaga Allah yakara daukaka mu ya kuma biya mana da mafificin gidan Aljanna."


Dad ya kalli Ammar cikin tsananin kulawa yace " Ammar kaifa? Ni gani nake kamar sai kafi Jalal shiga wani hali in aka rabaku da Seemah."
Kai ua girgiza yace " a'a dacan a matsayin kanwata take yanzu ma a haka zata zauna, na sani sanda nake mata ya wuce duk yanda kowa ke tunani amma tunda ni kadai nake santa haka banaji wani abun zai sameni."

Dad kam kalaman Ammar sun ratsa jinin jikinsa, yace " shikenan Ammar."


Murmushi Ammar yai yace " Dad dan Allah karmu fadawa kowa sai Abba kowa yaji a gidan bayan an daura in ba haka ba wani sai ya nemi canzama ra'ayinka."


Dad ya dafa Ammar yace " Ammar ka tabbata ba komai?"
Kai Ammar yadaga yace " marainiyar Allah itace first ni daga baya, sannan sai kamin addu'a Allah yabani wata."

Rungumeshi Dad yai yace " Ina Alfahari dakai d'ana ka fahimtar dani abinda ban yi tunani ba, Jalal yaron kirki ne tun yana karami, naji dadi sosai da kaunar da kukema juna kuna yara ta dawo muku yanzu."


Sun dade agun suna hira kafin su koma ciki, dad da Zaid suka koma gida.



Washegari kowa ya tashi anata hidima, Seemah ta rasa dalilin dayasa gabanta keta faduwa, Ammar ta kira sai dai taji Junaid ya d'aga, tace " yaya Ammar fa?".

Junaid ya kalli Zaid wanda yace Ammar yace kar afad'a mata inda yake, yace " yad'an fitane."

Ta kashe wayar tare da d'an had'e rai.

Zaune suke a massallaci an fara add'uoi za'a daura aure.
Abba zaune yayi shiru yana tunanin kalaman Dad, na jiya daddare, ajiyar zuciya yai alokacin da akace waliyin Jalal yaji dad yace " ganinan."


Dad ya riga ya sanarda mahaifin Jalal wato Amadu nan yai farin cikin da hakan har kuka sai dayai.



An dauren auren Junaid da Zahra, Jalal da Seemah akan sadaki dubu d'ari wanda da kudin da za'a bada na Ammar ne.

Mamakine ya kama 'yan uwan mahaifin Dad dana mahaifiyarsa, Habib ya kalli Dad cikin mamaki sai dai aikin gama ya gama.



Zaid ne ya kira Ammar dake asibiti gun Jalal yace " Ammar an d'aura."

Runtse idanunsa yai jiyake kamar yasa ihu, dakyar ya daure yace " ka fad'awa Seemah mijinta na asibiti ba lafiya."




Zaid yace " Ammar inzo in daukeka?"
Ammar ya d'aga kai, Zaid ya daga kai tare da cewa " Jalal din ya farka?"

Ammar ya girgiza kai yace " a'a ko ido ya bud'e sai dai inga ya maidasu, sai dai likita yace abarshi ya huta stress sunmai yawa ga damuwa."

Zaid ya d'aga kai.





? *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


*Luv u oll my fans.......*

No.7? 7?




Seemah na zaune tayi wanka tana jira agama ma Zahra kwalliya sannan a mata, rigace doguwa ta atamfa a jikinta aiki ne a jikin rigar har wajen ciki d'inkin yayi masifar kyau, a zaune kawai take amma gaba daya batajin jikinta daidai, jitai an fara kud'a hakan yasa gabanta ya sake fad'uwa, suka shigo d'akin sukace an d'aura, Seemah kasa tai da kanta ganin wayarta tai kara yasa ta daga, Zaid ne da sauri tace " Ya Zaid ina ya Ammar? Jinake kamar wani abu ya sameshi."
Zaid yace " Seemah ki fito ina waje mijinki ba lafiya."
" Naam? Me kake nufi?"
Kashe wayar yai dan jiyai baisan me zai ce mata ba, A zabure Seemah ta mik'e ko hijab bata dauka ba d'ankwalin data yafa akanta kawai ta sura tai waje ko takalmi batasaba.

A waje taga mutane sun taro anacewa " waye kuma Jalal?"
Tsayawa tai turus, can kuma sai tai tunanin ko ba Jalal d'in ta suke nufi ba, waje tai da sauri ta fada mota Zaid ya kalleta sannan ya ja motar, duk ta rikice tace " Ya Ammar meya samu Ya Ammar d'in?"
Kallanta yai jiki a sanyaye yace " Kunyi magana da dad?"
Ta girgiza kai tace " a'a yadai kirani da safe yacemin, ko mai na rayuwa mukaddarine, haka kawai yacemin."

Suna isa asibitin suka fito, duk Seemah ta rikice, harsunje shiga d'akin wayar Zaid tai kara, ya kalleta yace " nan ne ki shiga."

Ko kula shi batai ba ta fada dakin, daga nesa tafara ganin kamar ba Ammar ba, jiki a sanyaye ta karasa kusa da gadon, turus tai ganin Jalal a kwance duk ya rame sai bacci kawai yake.

Hawayene suka fara zubo mata a hankali takai hannu gefen fuskarsa hawayenta ne suka shiga d'iga kan kuncinsa, sai zubowa sukeyi ta kasa magana sai hawaye kawai take.


A hankali Jalal yad'an bud'e ido jin ruwa na d'igarmai, kallan Seemah yadauka mafarkine yasa ya kara lumshe ido, hawaye kawai takeyi, can ya sake bud'e ido daidainan ta kalleshi, idanu suka had'a yad'an motsa bakinshi kad'an yace " Meemah?"

Hawayene ya cigaba da zubo mata tace " Deen? Me ya sameka haka?"

Sai a lokacin ya tabbatar ba mafarki yake ba kallanta yai tare da cewa " me kike anan?"
" Naam?"
Tafad'a tare da kallan d'akin sai a lokacin ta tuna kamarfa Ammar ne yakamata ta gani ba shi ba, ta d'an juya tace " Ni cemin akai inzo in duba mijina na d'auka ya Ammar ne bashida lafiya."

Jalal ya d'an juya ido yace " meya sami Ammar d'in?"

Ta d'aga wayarta ta kira Zaid ga mamakinta Ammar ne ya d'aga.
Cikin tsanin damuwa tace " Ya Ammar kana ina?"
Yace " Seemah?"
Yanda ya kira sunanta yasa jikinta yai sanyi ta kasa amsawa.

Cikin wata murya yace " ki kula da mijinki, ke yake bukata a wannan lokacin."
Da mamaki tace " ban gane ba? Kana ina?"
Yai shiru can ya daure yace " An daura muku aure da Jalal karki damu dani ko kiyi tunanin wani abun, kawai ki kulada lafiyar mijinki."

Jitai kalaman sun shigar mata kunne banbarakwai sai dai kafin ta sake magana Ammar ya kashe wayar.

Kallan Jalal tai sai dai ganin yanasan tashi ya kasa saboda cikin dake bayansa, yasa ta daure matsowa tai zata taimaka mai, kallanta Jalal yai yace " bashi kawai, ki nemomin likita."

Bata kulashi ba kawai ta shiga taimaka mai, tana gamawa ta duba ga kayan shayinan da abinci hakan yasa ta hadamai shayi ta mikamai tace " ina zuwa."
Kallanta yai yace " kina zuwa ina? Me zaki dawo yi anan? So kike ran Ammar ya sake b'aci?"
Kallan yanda ya rame tai ta kauda kai tare da cewa ni kaina ban fahimci abinda ya Ammar d'in yake nufu da an d'aura mana aure dakai bane shiyasa nakesan ganinsa.

Bata jira mai zaice ba tai waje, Jalal ya kara maimaita kalamanta.


Seemah na fita taga Dad yana tahowa shida Abba, da sauri takarasa gunsa yace " Seemah muje ciki."

Kallan mamaki tamai sai dai ba zata iya musu ba.
D'akin Jalal suka koma bayan sun zauna shiru, nan Dad ya warware musu duk abinda ya faru jiya zuwa yau.

Seemah kuka take sosai, yana gama maganar yace " dan haka ki zauna anan ki kula da mijinki ki bar sha'anin biki su Zahra sayi."
Ta kasa magana haka ma Jalal wanda yakejin maganar kamar ta tsuniya, ganin halin da suka shiga yasa Dad ya mik'e shida Abba sukai waje.

Seemah ganin sun fita yasa ta mike da gudu ta bi bayan Dad ta baya ta rungumeshi tana wani irin kuka, Dad ya daure ya juyo da ita setinsa yace " Seemah?"

Cikin tsananin kuka tace " Dad meyasa ka bar Ya Ammar yai haka? Kamanta nace na hakura? Sannan babban burinka ne fa?"

Dad yad'an shafa kanta sannan ya kalli kafarta da ko takalmi babu yace " a haka kika fito ba ko takalmi?"

Hawayenta ne ya karo tace " Dad ina Ya Ammar d'in? I have to meet him. "

Dad yai murmushi yace " karki damu yayanki yace ki kulada Jalal."

Yad'an zareta daga jikinsa yace " karkiyi tunanin komai sai mijinki."
Yana kainan ya juya ya fara tafiya.


Tsugunnawa tai a gun ta shiga kuka, ta dade agun sosai mutane sai wucewa suke suna kallanta dakyar ta daure ta mike tai cikin d'akin ga mamakinta Jalal ta gani ya mik'e yana sa rigarsa, da sauri ta karasa inda yake? Idanunta duk sun canza tace " Ina kuma zaka?"

Kallanta yai yace " me Ammar yake tunani? Ni zanje in mai magana."

Cikin kuka tace " ni ina zansan me yake tunani, amma kaidai bazan barka ka fitaba bayan ba lafiya gareka ba."

Kallanta yai cikin wani yanayi yace " Meemah tunanin halin da Ammar yake ciki nake."

Ta goge hawayenta tace " naji wannan amma ka koma ka kwanta sai inkira Ya Ammar d'in."

Jiki a sanyaye Jalal ya zauna, ta mikamaj wayarta tareda dialling d'in number Zaid.


Ammar ya d'auka, Jalal yace " Ammar meke faruwa?"

Ammar yad'anyi murmushi kad'an yace " meke faruwa dame? D'an na bar maka Seemah ko dan kana tare da ita?"

A zuciye Jalal yace " Ammar meke damunka ne? How can u joke now."

Ammar yai ajiyar zuciya yace " kai dai dakake lovesick yanzu sai ka ware."

Jalal yace " Ammar ban aminta da...."
Katseshi yai da cewa " ka saketa to."
Yanakai nan ya kashe wayar, shiru Jalal yai yana maimaita kalmar saki.

Seemah ta zauna kusa dashi kadan tace " me Ya Ammar d'in yace? Wasa yake ko?"

Jalal ya kalleta cikin mamaki yace " da alama dagaske yake tunda haryake cemin wai in sakeki ."

Ta kalleshi da mamaki, mik'ewa tai da sauri tace " Me Ya Ammar yake tunani?" Tafad'a tare da hura iska.

Jalal ya daure yace " taimaka min in kwanta please. "
Harararsa tad'anyi tace " akan me?"
Kallanta yai sannan ya daure yace " hmm kiramin ko nurse ne."
Ta d'an tab'e baki tace " nurse d'in ai kala biyu ne, maza da mata wacce kakeso a kira ma?"

Jalal ya kalleta tunowa yai da masifarta ta da yace " auu kiramin koma waye ai ni patient ne."
Ta makamai harara tare da turashi gado da d'an karfi, zafi yasa sai daya saki kara yace " me kuma nai kinsan dai ba lafiya ce dani ba, irin wannan tureni?"
Ta harareshi tare da komawa gefe ta zauna, Jalal ya juya kai kamar mai bacci dan jin abin yake banbarakwai.

Text tama Ammar kamar haka.
_Ya Ammar na sani sarai kayi haka ne dan farin ciki na sai dai Ya Ammar aikin gama ya gama bani da abincewa a wannan lokacin, kalma daya zan iya fadama shine Allah ya sakama da mafificin gidan aljanna ya kuma baka matar data fini._

Tana turawa ta
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

*LAST PAGE*

No. 7? 8?



Can gida kuwa wasu abin nan ya basu haushin gani suke Dad bai kyauta ba, wasu kuwa harda habaici na dama yarinyar da batada mahaifi me zaisa ya had'ata da d'ansa?"

Zahra kam taji ba dadi dasu Junaid sai dai ya za'ai tunda dai an riga da angama, Ammar ko gidan baije ba, sun riga sun shirya yin dinner sai dai Zahra ce da Junaid kawai zasu.


Jalal kam suna kwance, sai can Seemah ta farka, tana ganin Jalal idanunsa biyu da sauri ta mik'e tsaye tare da wayancewa da hmm ina toilet din ne? Tafad'a tana dubawa da gudu tai nufi kofa ta bud'e ta shige.
Jalal ya bita da dariya ganin yanda ta rikice.

Tunanin wayarsa ce tazomai yasa ya jawo wayar Seemah ya kira Abbansa.
Abba ya daga, Jalal ya gaidashi.
Cikin zumud'i Abba yace " Jalal kaji abin alheri ko? Bansan mezancema Ammar da Isma'il ba."
Jalal yadanyi murmushi yace " Zainab fa?"
Abba yai shiru, Jalal ya danyi murmushi kad'an nasan bazatai farinciki ba.
Abba yace " Jalal kayi tunanin inda Seemah zata zauna?"
" hmm ina tunanin tambayarta ko nan kaduna ko kuma nan, ni abin ne banbarakwai nake jinsa."

Abba yai dariya yace " ba wani banbarakwai Allah ya riga ya tsara Seemah matarka ce."
Jalal ya kalli kofa inda yaji motsin Seemah, yace " Abba sai anjima wayar Seemah ce."
Nan sukai sallama tare da kashewa, Seemah ta harareshi kad'an tare da cewa " wa yace a d'aumin waya?"

Jalal ya dan yi murmushi yace " yayarki na kira."

A zabure ta karaso kusa dashi tace " wacce yayata?"
Kallanta yai yace " haka ake jinyar baza'a bani abinci ba? Yunwa nakeji."
Ranta a b'ace ta bud'e kular da ta gani a d'akin fatan dankali ne yaji kifi sosai, ta zubamai a plate sannan ta mikamai, tace " wacce yayata?"
Jalal yadan rik'e ciki kadan yace " haka ake kula da miji ko abincin baza'abarshi yaci ba?"
Juya kai tai aranta tace " su miji manya."

Yana gama ci ta kalleshi tace " wacce yayata? "
Hannu yasa ya riko ta tare da zaunar da ita kusa dashi yace " Meemah bamuyi tunanin inda zaki zauna ba?"
Ta turo baki tace " inafa zan zauna?"
Ya kalleta yace " inda zamu zauna nida ke a kaduna ko anan."

Ta mik'e tare da cewa " ni yazanyi iyi sallah ko mayafi ban fito dashi ba, kallanta yai yace " ai kuwa sai dai kiyi waya a kawo miki dan bazaki fita a haka ba......"


Kusa dashi ta matso tace" to ya kakeso inyi?"

Yace " bana fadamiki ki sa a kawo miki ba nidai matata bazata fita a haka ba mutane su kalleta."

Ta sa dariya sai data tsagaita ta kalleshi tace " lalai mai mata."
Lumshe ido yai yace " sosai ma, Ammar ne ya bani matar da nakeso wacce ji nake duk numfashina tana tattare dani."
Dariya ta sakeyi tace " Kai Deen yaushe ka zama haka?"
Jawota yai jikinsa yace " ke kika maidani haka, mu zauna a abuja

36 / 37