YAR GATA CE COMPLETE HAUSA NOVELS BY MIEMIEBEE.txt

Author :  MIEMIEBEE Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   10 / 98

27K to 30K   out of 291.7K words

kallo, sosai Baba ya shiga lalashinta “shikenan toh ya isa Lubabatu koh? Ta tab’a min ke? Sorry toh” Kukan take har yanzu ba makawa, Lubabatu da dad nata suka tsaya kallon ta chan Zeezee tace, “an yima Lubabatu kitson beads ni ba’a min ba” ta kuma fashewa da kuka. Dariya sosai dukansu wajen suka hau yi Alhj. Matafseer ya nisanta yace, “da alama wannan itace auta koh?”
“Itace” Baba ya amsa mai yana murmushi, miqewa yayi da Zeezee a hannunsa suka gaisa da Alhj. Maitafseer tare da yin formal introduction. “Zeezee sauk’a kije ki zauna kinji K’anwata?”
“O’o se ammin ilin kishon Lubabatu.” Baba ya kalli Dad na Lubiee dake murmushi yace, “karka manta fa an mata kitso da beads me kyau tasa mahaifiyarta a gaba sam se an cire mata take wanan fitina yanzu.”
“Ahab! Ko Lubiee nan jiya seda tace a cire mata na hana uwar, ba duk abinda yara suke so zamuna musu ba.”
“Hakane...” cewar Baba kamar dagaske.
“Zeezee mama na sauk’o kinji? Ga k’awa nan na miki kinji sunan ta Lubiee.”
“O’o ni ba maman ka bane niba shohuwa bane.” tasa kuka. Dariya duk suka tsaya yi at her comment, “ya isa, sauk’a toh K’anwata” da k’yar ya samu ya sauk’e ta, ta tsaya tana kallon kitson Lubiee “ni se ammin ilin wannan.”
“Karki damu, muka koma gida za’a miki” Baba yayi assuring nata. “Sunan ki Lubiee?” Zeezee ta tambayi Lubiee.
Kai Lubiee ta d’aga in response “ke kuma Zeezee?” Itama ta gyad’a mata kan.
“Yauwa jeku zauna toh se kuyi karatu fah” hannunta Lubiee taja suka zauna ko ba’a tambaya ba za’a san Lubiee ta girmi Zeezee danko ta fita wayo, shiru Zeezee tayi bata sake cewa komi ba seda taga Baba ya d’au hanyan barin ajin ta sake sa ihu shima se yaji bare iya barinta ba, da k’yar Dad na Lubiee yajasa sukayi waje. Kuka kenan! Kuka Zeezee ke wane ana cire mata rai Lubiee ce ke lalashinta har ta samu tayi shiru ko da aka fita break Aunty da Nanny suka bubbud’ewa kowa lunch pack nasa seda suka sha mamaki ganin yadda aka cika wa Zeezee nata.

Sede wani abin mamaki sekace ba Zeezee me rowan da muka sani ba, ganin nata chocolates d’in sunfi na Lubiee yawa ta d’ibi guda biyu ta bata cikin d’an k’ank’anin lokaci wasa da shak’uwa ya shiga tsakanin Zeezee da Lubiee.

~* ~* ~*
Ko minti d’aya Baba be k’ara kan 12:30PM (lokacin tashin su Zeezee) ba, ana ringing bell ya shiga school yayi class nasu Zeezee alokacin suna ta wasa ita da Lubiee da sauran ‘yan class nasu, tana ganin sa taje tayi hugging nasa, sosai Aunty ta sake yabawa k’ok’ari irin na Zeezee dai-dai Baba yazo fitowa suka had’u da Baban Lubiee gaisuwa kad’an sukayi kowa yabi path nasa.

~* ~* ~*
Dawowan su Baba gida Zeezee tayi ciki da gudu, Mama ta tarar tsaye a tsakar gida da gudu taje tayi mata oyoyo Mama ta d’agata sama “yaya school d’in?”
“Mama nayi k’awa sunanta Lubiee ko Baba?”
“Sannu da zuwa Alhj.”
“Yauwa sannu”
“Zeezee tayi kuka da ka ajiye ta?”
“Sosai ma se a hankali zata saba ai.”
“Toh Auta na me aka koya muku?”
“Littin (written) form of A and sound ‘ahh’, and litten form of B and sound bhh.”
“Ahh gaskiya autan nawa na ja.”

****
Da yamma bayan tafiyan yaran islamiyya Baba kuma masallaci Zeezee ta samu kanta, k’usa ta samu ta nufa garriage inda Baba ke parking motarsa da yake mugun ji dashi fiye da duk wani abinda ya mallaka. Dai-dai driver’s door ta zana babban letter A sannan da small one a gefensa haka tabi other side d’in ma tayi thesame thing with letter B, jiki ta sata wane batai komai ba taje tasamu Mama dake zaune tsakar gida tana tsifa, “Mama zan tayaki.”
“Inba kaud’i ba ina ke ina tsifa?”
“Ni shena miki.”
“Nace baza kiyi ba kuma ki yasar da k’usan” ihu tasa ta soma kuka, badan Mama na so ba tace ta taso ta tayata. Tsifan da ba’ayi ba ranan kenan, ita ta hana Mama yi ita kuma bawai iyawa tayi ba.
Atare Baba da yaransa suka iso gida kaman ance Baba duba motanka yana kai dubansa yaga letter A na mai sallama “subhanallai me wannan? Waya min wannan d’anyen aikin? ‘yan unguwa ko meh?”
“Laaa Baba gashi ma har a nan!” cewar Yasmeen da hanzari ya zagaya ya duba.
“Aiko ba’a tambaya ba ansan Zeezee ce” cewar Mariam, a rayuwa ba abinda tafiso kan taga Baba da Zeezee suna fad’a. A fusace Baba ya nufa ciki su Mariam ne a sahun baya suna binsa.

“Zeezee! Zeezee! Zo nan!” tana jin muryan Baba ta lab’e bayan Mama dake zaune kan sofa a parlour. “Ba babanki bane yake kiranki? Kije mana!”
“O’o, Mama karki bari ya tab’ani jan baki shweet d’ina.”
“Me kika masa tukuna?”
“Bab-” bata k’are maganan ba sega Baba da gayyansa suna shigowa cikin parlourn, cusa kanta tayi jikin Mama.
“Ya haka Alhj wani abu ne?”
“Zeezee!” Ya kira sunanta a tsawace, kakkarwa ta soma, “mesa kika zana min jikin mota? Dan bana dukanki koh? Wayace ki zana min mota?” Shiru... “Dake fa nake magana!” Ya sake fad’a a tsawace. Kuka Zeezee tasa “toh kayi hak’uri amman kad’an ka gani wallahi ai nasha gaya maka kadena biyewa ‘yar nan bakaji ga irin ta ai.” Ignoring what Mama said yace, “kika sake zana min mota sena zane k’afafuwanki da tsintsiya ce miki akayi mota gun rubutu ne?” Hannu ta d’aga ta zagi Baba, baki kap dukansu including Baban suka sake in shock.
“Zagi! Ni kika zaga Zeezee?” D’ayan hannunta ta d’aga ta sake zaginsa sannan daga bisani ta sauk’e duka ta b’uya bayan Mama “ai kad’an ka gani nasha gaya maka adinga taka mata birki bakaji yau kanka abin ya koma ai.”

“Waya koya miki zagi? Iyyeh! Zan zane kifa! Ni kika zaga? Toh ki sake ki gani da wayan charger zan shod’e kafafunki!” ya tsawata mata sosai, kuka ta shiga yi sosai ko ta kanta beyi ba yabar parlour’n.
Dariya kenan! Ibraheem and others dariya suke tsakanin su da Allah wane dan shi aka turo su duniya, suna dariya suna yimata rawa da wak’ar shoki ita ko se k’ara volume na kukan nata take Mama ce kad’ai ke lalashinta “yi hak’uri amman kema kar ki sake, ba kyau zagin Baba ku kuma haka akeyi ne? K’anwar ku ce fah.”
“Ai Mama ajiye wanga zance a gefe” cewar Mariam in between laughter.
“Ahtoh! Bature beyi k’arya ba, 9 days for the thieve one day for the owner.” Omar ya mara mata baya suka cigaba da yiwa Zeezee dariya ita ko se kuka take.
Da dariyan yayyun nata ya isheta ta fice musu daga parlour’n gabad’ai taje chan bayan BQ ta baje a k’asa se kukanta take sha kan ba gobe.



*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 10

_Words can’t ever explain how much I love you *AUNTY SIS*, thank you for everything, thank you for being that one great special person to me. ILY eternally😘😘😘😘 I devote this page in special honour to you! Don’t thank me you deserve more and more!_




_5 minutes later..._
Baba ya dawo parlour da alama ya huce yanzu, Mama kad’ai ya tarar a parlour’n tana tsifa, “Ina Zeezee?” Ya tambaya.
“Oho yayun ta sun sata gaba suna mata dariya ta fice ban san ina ta shiga ba” ba tare da ya amsa taba ya fice tsakar gida ya shiga k’olla wa Zeezee kira tana jinsa tak’i amsawa har a yanzu kukan take. Nemanta ya shiga yi chan bayan BQ ya tsince ta nishinta har wani sama-sama yake sekuma tabasa tausayi yaji dama be mata masifan ba, a nitse ya k’arisa gabanta yace, “Zeezee” kanta ta kawar daga kallon sa.
“K’anwata yi hak’uri kinji? Tashi mu koma ciki” nan ma shiru. “Yi hak’uri kinji K’anwata Baba is sorry amman kema karki sake zana min mota kinji? In rubutu kikeson yi let me know sena baki paper ko book kiyi. Mota ba wajen rubutu bane kinji?” da k’yar ya samu ya shawo kanta dan banzan zuciya irin na Zeezee, bayan ta yarda ya d’auketa yace, “su Ibraheem sun yita miki dariya ko?” Ta gyad’a kai a shagwabance.
“Yi hak’uri toh muje su baki hak’uri” a k’aramar parlour Baba ya tadda yaran, “waya miki dariya cikinsu?” Ya tambayi Zeezee.

“Dukan su” tayi pointing nasu da finger.
“Oya ku bata hak’uri.”
“Hak’uri?” Exclaimed Ibraheem, “meh muka yi mata da zamu bata hak’uri?”
“Uwarka kayi mata, d’an banzan yaro bata hak’uri nace!” Chan k’asa-k’asa alsmost like mumbling Ibraheem yace, “yi hak’uri.”
“Ban jika bafa, ka bata hak’uri kace Zeezee kiyi hak’uri, oya ina jinka.”
“Wallahi Baba raina ni zatayi.” yayi protesting.
“Da kai da rainin duk uwaku, bata hak’uri nace!” Haka Baba ya sasu individually sukayi ma Zeezee apologising.

“Shikenan koh K’anwata yi hak’uri” sauk’eta yayi tare da ficewa. Habaici ‘yan uwan nata suka hau yi suna zaginta kota kansu batayi ba taje ta d’ibo baby dolls nata da teddy bears ta jerasu kan table a waje sannan ta d’au ruwa cikin wani d’an karamin bucket ta ajiye se sponge case nata ta shiga ta d’auko. Wanka ta shiga yima dolls natan tafara da teddy’n kenan Allah ya fito da Mama “kai! Kai! Karki sa ma teddy’n ruwa!” dakatawa Zeezee tayi tana kallon Mama, “‘yar k’auye kawai wayace miki ana wanke teddy bear?”
“Ni shena wanke, tunda Baba ya shiyo min su bashuyi wanka ba.”
“Ce maki akayi mutane nesu? Karki sa musu ruwa nace!”
“Ni shena sa, Baba! Baba!”
“Na’am K’anwata, Hafsah dan Allah kifita daga harkan yarinyan nan, dan Allah nace” Baba yayi maganan daga cikin d’aki.
“Teddy bears fa zata ma wanka.”
“Eh kibarta please.”
“Dama ai ta nan kafi kauri, d’aure wa k’arya gindi, gidan wa aka tab’ayi wa teddy bears wanka?” Dawo da kallonta tayi kan Zeezee “kinji wallahi karki kuskura ki shigo min da su ciki in kin jik’an kinaji ko?”
“Shena shigo dasun” tana kaiwa nan ta kwarawa teddies d’in ruwa tahau musu wanka jak’ab ta jik’asu da ruwa tazo shigowa dasu Mama ta bud’e mata ido sosai koda Baba yayi magana ta nuna mai she’s damn serious baza’a shigo dasu ba.
“Shikenan K’anwata karki kula Mama kinji? In sun bushe seki shigo dasu, jeki cigaba da wasan ki” ciki tayi ta d’auko mai sannan ta bud’e kit na Mama ta zaro scissors ta fice da wuri bayan ta bi baby dolls da teddies d’in ta goggoga musu mai ta d’au d’ayan baby doll me uban gashin tasata gaba ta yayyanke gashin tas, haka tayi da sauran gabad’aya tayi musu aski Yasmeen ce tafito ta kamata in the act.

“Laaaha’ila! Bade aski kika yiwa dolls nakin ba?” Dariya tasa ta kira Mariam, “Adda Mariam! Zokiga wani abu” atare Mariam da sauran suka fito, dariya suka hau yi ganin yadda Zeezee ta tand’e gashin kan baby dolls natan wane aikin wanzami. Dariya suka tsaya yi har seda Mama dake kitchen ta fito “wai haka kuka ta dariya lafiya dai ko?”
“Dubi fa Mama” Yasmeen tayi maganan tana k’ok’orin d’ago d’aya daga cikin dolls d’in cizo Zeezee takai mata “kal ki tab’a min Baby na.”
“Zeezee yanzu aski kika ma baby dolls nakin? Meye amfanin hakan?”
“Gashin je fito ai, ba Mulan (cartoon) ma ta ashke gashinta ba kuma ya shake fitowa, nashu shuma je fito.”
Habbaa!! Dariya dukansu suka sa gun, saura harda hawaye da k’yar Mama ta iya tayi shiru tace, “sekuma aka cemaki wannan cartoon ne? Ai tunda kika aske musu bai sake fitowa.”
“Sheya fito”****


Kasancewar yaran basu je islamiyya ba yasa bayan Sallan La’asr kowannensu ya kwanta yin bacci, Mama ma can ad’akinta ta mik’e tana bacci Baba da Zeezee ne kad’ai idonsu biyu shima don yana buga lisafi ne yana gamawa ya mik’e kan gadon d’akinsa “K’anwata zo mu kwanta kinji? Ajiye Ipad d’in kinga kinje school yau kamata yayi ki huta kema, bakiga sauran yayyun naki duk sunyi bacci ba?”
“Ni o’o banajin basshi.”
“Toh Allah baki hak’uri ni zan kwanta” nan da nan Zeezee tabar d’akinsa tayi nasu Mariam kulle ta tarar da k’ofan nasu, ba kalan knocking da batayi na suna ji suka k’i bud’ewa dan kanta ta nufi nasu Ibraheem suma haka suna jinta tana knocking suka k’i bud’e mata. D’an shirme tayi a tsakar gida, data gaji don kanta taje ta samu Baba a d’aki ta mik’e gefensa itama tana wasa da d’an gemun dayake ajiewa. Ahaka har bacci yayi gaba da ita ba ita ta tashi ba se 7:35PM alokacin gari yayi duhu shaarrr. Bayan ta fito daga parlour ta nufi parlour inda ta tarar da ‘yan uwan nata suna kallo “ni ahad’a min tea shafe yayi.”

“Ke waya gaya miki safe yayi? 7pm nefa yanzu.” Cewar Yasmeen.
“Meh 7pm? Ni a had’a min tea shafe yayi.”
“Shareta Yasmeen fitina ne da ita ai Baba ya hanata shan tea da daddare ba abinda za’a had’a miki.” Mariam tayi stating. Kuka Zeezee tasa awajen tana kiran sunan Baba seda yafito tayi shiru, “K’anwata kin tashi neh?”
“Baba kace Adda Mayyam ta had’a min tea.”
“Babu shan tea da daddare yana saki fitsarin kwance, in kina jin yunwa a dafa miki indomie da egg naki koh?”
“Yanzu ai shafe ne ba dale ba ni a had’a min tea.”
“Dan fa bata saba baccin yamma bane shiyasa take gani kaman safe ne yanzun” Ibraheem yayi explaining.
“Ba shakka kam, K’anwata ba safe bane fa yanzu dare ne.” Mik’ewa tayi k’asa agun tana birgima tana ihu ita a had’a mata tea, ba yadda Baba beyi da ita ba ta gane fa ba safiya bane dare ne yanzun amman inaaa sam takasa ganewa ita tunda tayi bacci ta tashi toh safe yayi don haka kuma a had’a mata tea. Haka Mariam ta had’a mata tean itade Mama tausayin katifanta take gudun kar Zeezee ta tsula mata fitsarin kwance.



**** 8:23PM
Baba da kansa ya taya Zeezee suka yi mata homework, bayan sun gama yasa mata book nata cikin jaka “sauran bacci ko K’anwata? Akwai school gobe.”
“Nishe an sha min beads ilin na Lubiee” nan Mama dake karatun Qur’ani ta juyo ta watsa mata harara “waye boyi-boyin ki agidan nan? Jiya kice se an cire yau kice a miyar? Kinyi k’arya.”
“Ni nace ke jaki shamin ne” tayi maganan tare da murgud’a wa Mama baki.
“Ai ko kince nima ba sa miki zan ba.”
“Toh ya isa haka da Allah, kisa ‘yar yarinya a gaba kina exchanging words da ita, Zeezee asa miki beads?”
“Eh” ta gyad’a kai.
“Oya Hafsah ibo beads d’in maza ki sa mata.”
“Wallahi-”
“Ni banashon Mama Ya Omal nakeso” Zeezee tayi sauri katse Mama.
“Omar kuma?” asked Baba.
“Eh shi.”
“Toh Hafsah mik’a mata beads d’in taje ta same shi ya samata.” Bayan Mama ta mik’a mata ta fice a k’aramin parlour ta tsinci yayyun nata suna kallon King Of Hearts gaban Omar tasha yayi saurin fad’in “ya haka? Matsa min nikam” beads natan ta nuna mishi “gashi ka samin.” Wani kallon rainin hankali ya sakar mata sannan yasa dariya ba shi kad’ai ba har sauran ‘yan uwan nasa.
“D’an daudu ne ni da zakice in sa miki beads?”
“Ni kasha min.”
“Bazan san ba maras kunya kawai, matsa min ko na gaggaura miki mari inba iskanci ba ki dubi Adda Mariam da Yasmeen ki wani ce wai ni zan sa miki beads bakida kai.” Kuka tasa wajen har seda Baba ya fito tayi shiru, “ya haka? Meke faruwa?”
“Omal ne yashamin beads wai o’o.”
“Laha ila! Ni? Yaushe nace barin sa miki ba?” Cewar Omar.
“Munafiki na sanka sarai maza zaunar da ita ka fara sa mata” ba tare da ya sake musu ba ya soma aiwatar da abinda aka sashi.
“Ni banashon wannan film asa min dijney junior.” Banza da ita sukayi kaman basu jita ba.
“Ashamin dijney” ta k’are maganar a shagwabance.
“Shin baku jita bane?” Asked Baba.
“Ayyah Baba yanzu fa ze k’are” cewar Mariam calmly.
“Wayyayi kayya ne ni asamin disney.”
Dogor tsuka Ibraheem yaja ya sa mata disney’n “kalli fa Baba shirme ake.”
“Eh bar mata shi takeso” yana kaiwa nan ya fice, habaici yaran sukayi tayi tsakaninsu suna zagin Zeezee a yayinda Omar keta samata beads na mugunta yana d’ad’d’angale gashin bayan ya gama mata ta wuce d’aki ta kwanta tsakiyan su Baba ma yau.

***Washegari...
_6:05AM_
Bayan Mariam ta shigo ta gaishe da Baba kaman jiya ta gaya mai dalilin zuwanta da ‘toh’ ya juya ya shiga tada Zeezee dake ta sharb’an bacci.
“Zeezee tashi kinji? Akwai school yau ko bakison kije kiga Lubiee?” Shiru... “Tashi kinji K’anwata.”
“Ni o’o bayin jeba.”
“School d’in?”
“Eh bayin jeba.”
“Yi hak’uri.”
“Ni o’o” ba yadda Baba beyi da ita ta tashi ba tak’i. Bayan sunci fiye da minti goma Zeezee tak’i tashi Baba yace da Mama “to ke bazaki sa baki bane?”
“Ni asuwa? Wai daddawa acikin kunu, bayan kai Zeezee tana jin maganan wani a gidan nan ne? Tsakaninku” tana kaiwa nan ta juya mai baya tare da jan comforter.
“Zeezee tashi kinji?”
“Baba ni bayin jeba” tasa kuka, kuka take tsakaninta da Allah ita bazata jeba, at long last Baba ya amince mata “jeki Mariam, Zeezee bazata je school ba yau se gobe.” Kai kawai ta gyad’a cike da

10 / 98