YAR GATA CE COMPLETE HAUSA NOVELS BY MIEMIEBEE.txt

Author :  MIEMIEBEE Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   14 / 98

39K to 42K   out of 291.7K words

scolding d’ina su baki ganin laifinsu ai nasani Baba kad’ai ke sona a gidan nan kuma zaki gani” tana kaiwa nan ta shige d’akinta.

Bayan sallan Azahar Baba ya dawo gida har alokacin Omar beje ya siyo wa Zeezee USB’n ba, d’akinsa ya wuce direct alokacin Zeezee ke fitowa daga d’akinta sukayi clashing sekace ‘yar yarinya taje ta rungemeshi ya d’agata sama “Omar ya siyo miki kuwa?” Kai ta kad’a “yak’i shikuma Ya Ibraheem ya nank’washeni a kaina.”
“Haka ya faru? Bari ina zuwa, kinci abinci?”
“A’a”
“Jeki d’iba kici ina zuwa” yana sauk’eta ta wuce kitchen su Mariam da Yasmeen ta tarar se aiki suke da Mama tana tayasu.
“Ina abinci na?” tayi tambayan ma dukansu, ba sannu da aiki ba komai.
“Kinba ma waye ajiya kike wannan tambayar?” Yasmeen ta watsa mata harara. Hararan ta miyar mata itama, “ma ke na baiwa, ni ina abinci na? Tun d’azu ku d’aura lunch kunk’i sekun bari yunwa ya gara mutum.”
“Wai waye sa’anki anan? Zan gaggaura miki mari fah!” Mariam ta bud’e mata ido.
“Mschww!” Zeezee taja tsaki, ganin Mariam ta miqe Mama tayi saurin dakatar da ita “yi hak’uri Mariam barta tana yima kanta ne” nan da nan suka sauk’e girkin Zeezee ta matso da plate nata “asamin.”
“Baza’a san ba kinyi sallah neh?” Mama ta tambayeta, shiruu Zeezee batace komi ba dan kuwa batayi sallan ba, “tambaya nake kinyi sallan Azahar?”
“Ni meh had’in abinci da Sallah kisa min kona fad’awa Baba.”
“Jeki gayan maras kunya kawai” dai-dai nan Baba yashigo kitchen d’in “yauwa Baba kaga Mama tasamin abinci wai o’o.”
“O’o kamar ya? Sa mata abinci mana Hafsah.”
“Kasan kuwa yarinyan nan batayi sallah ba infact bata ma sallah kullum ko an sata se baza tayi ba.”
“Bata sallah?” Baba yayi maganan unbelievably.
“Wallahi k’arya ne” cewar Zeezee.
“Toh kinayi neh?”
“Wallahi batayi Mama” cewar Yasmeen.
“Rufa min baki abinda kika iya kenan” Baba ya tsawata wa Yasmeen. “Zeezee wai baki sallah?”
“Baba inayi wallahi kawai yanzu ne ban yiba saboda ina jin yunwa amman ina gama ci zanyi.”
“Yauwa K’anwata I trust you ai” k’wace serving spoon na hannun Mama yayi ya zuba wa Zeezee potatoe porridge d’in da nama biyar akai.
“Haba Alhj ya da haka? Mukuma sauran me zamu samu?”
“Ke ko kunya bakiji ba me zakiyi da nama tsohuwa dake?”
“Nide ba tsohuwa bace kuma naga wanda suka fini shekaru ma sunaci, kuma Mariam ku d’ibi biyar-biyar d’in, yarinya ko aikin d’aga tsinke batayi sede taci tayi kashi tayi rashin kunya kuma aka tashi ita za’a na bata duka naman miya.”
“Kanki akeji” plate ya ja ya d’iba nasa suka fice da K’anwarsa.

*** _2:45PM_
Baba ya tara iyalan sa a parlour dan raba musu kayan babban sallan su wanda will take place in 3 weeks time. “Ina Omar?”
“Yaje siyo wa Zeezee USB.” Ibraheem ya amsa.
“Okay” yayi maganan yana zaro had’ad’d’un zannuwan dake cikin wani babban leda, guda goman duka ya baza a kan carpet “ina K’anwata?”
“Na’am Baba” ta matso kusa dashi ta zauna.
“Zab’i guda hud’un da suka miki anan-”
“Haba! Haba! Alhj kayi adalci mana, Mariam Babban su ai ita ya kamata ta fara zab’a” Mama ta fad’a.
“Zani ba zani bane kam? D’auka Zeezee da Allah kar kiji ta.” Gwalo Zeezee tayi ma Mama sannan ta kwasa hud’u mafi had’uwa cikin goman. “Oya kema Hafsah d’au naki guda biyu.”
“Biyu? Ita hud’u ni biyu kuma seda ta d’auka zan d’au wallahi banaso kabata nawan, na hak’ura.”
“Kanki akeji” ya d’au guda biyu ya wulla mata sauran hud’un kuma ya bawa Mariam ta zab’a biyu ta bawa Yasmeen biyu ana cikin haka Omar ya dawo nan Baba ya basu shaddojinsu shida Ibraheem guda uku-uku had’d’d’u masu kyau, bayan nan ya sake jawo wani leda ya zazzage laces biyar ciki nanma yace Zeezee ta zab’a biyu bayan ta zab’a ya raba wa Mama da su Yasmeen ragowar haka kaman suyi kuka sukayi godiya suka watse. D’aki Zeezee ta nufa da kayakin sallanta se tsalle take nata guda six (6) na sauran 3-3 ganin ta wargaza wardrobe natan d’azu agarin neman USB kuma gashi tana son sa sabin kayanta ciki yanzu gashi she is not in the mood of preparing her wardrobe taje tasamu Baba tayi ta mai shagwab’a ita akira Yasmeen ta gyara mata wardrobe nata, bayan taje ta kira Yasmeen Baba ya isar mata da abinda yakeson tayi ai atapir tace ita baza tayi ba ai da gan-gan Zeezeen ta wargaza kayakin, ido sosai Baba ya bud’e mata sannan ta amince se kumbure-kumbere take.
Nan da nan ta shiga gyara wa Zeezee wardrobe nata ana cikin haka Lubiee tazo, parlour’n Baba Zeezee ta kaita suka yita hira kaman ba gobe suna game, bayan Yasmeen tagama gyara mata wardrobe d’in suka koma d’akinta taciro wa Lubiee kayakin sallanta seh 5:30PM Lubiee tace zata tafi bayan sallamarta da Baba yayi yasa Ibraheem yayi dropping nata nan Zeezee tace se ta bisu itama. A bayan mota suka zauna su biyu se k’us-k’us suke har suka yi dropping nata.

“Toh bazaki dawo gaba bane sena mauje ki?”
“Ayyi Ya-”
“K’aniyanki nan waye driver’nki? dawo gaba nace!” Harara me rai da lafiya ta watsa mai batasan ko ya ganta ta mirror ba, bayan ta dawo gidan gaba ya seta kanta ya sake mata rank’washi me zafi, “Allah ya is-”
“Meh kikace?”
“Babu” hannunta yakama da niyar murd’awa aiko tasaki ihu “dan Allah Ya kayi hak’uri wallahi bazan k’ara ba.”
“‘Yar banza kawai ai ko kiyi behaving kanki ko na b’ab’b’ala ki kamin mu isa gida wallahi” daga nan Zeezee bata sake ce mai komi ba dan lafiyarta tayi shiru on their way back home budurwan Ibraheem Fateema ta mai waya kan tana buk’atan ganinsa nan ya sha U-turn Zeezee na ganin haka tace, “ni wallahi ka kaini gida kafin nan kaje gun Fateeman.”
“Magana kike?” Ya mata sending wani dirty look dan kanta tayi tsit ahaka suka isa Ibraheem yasata tabar motan Fateema ta shiga. Se hira sukeyi tun Zeezee na hak’ura taga bazata iya ba ta mik’e taje ta samesu “ni wallahi kashi nakeji hiran ya isa haka.” Kallonta Ibraheem ya tsaya yi totally out of words.
“Zeezee toh muje in kaiki ciki kiyi?” cwar Fateema.
“Ni bana sharing toilet, na gidanmu nakeso” baki wangalau Fateema ta bud’e tana kallon Zeezee dake murgud’a mata baki sama-sama “toh Baby se next time baby sis is in need kuyi ku tafi.” Har a yanzu Ibraheem ya kasa cewa komai haka yana gani har Fateema ta shige gidansu Zeezee ta bud’e motan ta shiga “toh kayi sauri mana Ya, yafa matseni” bece da ita komi ba ya kunna motar suna cikin tafiya sunzo ta old GRA ya yi parking gefen hanya “meh kuma zamuyi anan Ya?” Nanma bece komi ba ficewa yayi kawai ganinsa tayi ya karyo itche d’anye yana nufan motan kafin tace zata bud’e k’ofar ta har ya isketa, fincikota yayi ya hau zabga mata itchen a k’afafunta daman ‘yar guntuwar ‘yar kanti ne a jikin ta tana ihu tana basa hak’uri amman ina se k’ara mata yake kasancewar hanyan shiru ba hayaniya, seda ya nad’a mata na jaki sannan ya barta lokacin har wani sama-sama nishinta ke. “Kad’an kika gani bake fitsara da rashin kunya ba? Muna tare dake ai gyara miki zama zanyi maza miqe ki bud’e motan ki shiga.”toh kayi sauri mana Ya, yafa matseni” bece da ita komi ba ya kunna motar suna cikin tafiya sunzo ta old GRA ya yi parking gefen hanya “meh kuma zamuyi anan Ya?” Nanma bece komi ba ficewa yayi kawai ganinsa tayi ya karyo itche d’anye yana nufan motan kafin tace zata bud’e k’ofar ta har ya isketa, fincikota yayi ya hau zabga mata itchen a k’afafunta daman ‘yar guntuwar ‘yar kanti ne a jikin ta tana ihu tana basa hak’uri amman ina se k’ara mata yake kasancewar hanyan shiru ba hayaniya, seda ya nad’a mata na jaki sannan ya barta lokacin har wani sama-sama nishinta ke. “Kad’an kika gani bake fitsara da rashin kunya ba? Muna tare dake ai gyara miki zama zanyi maza miqe ki bud’e motan ki shiga.”

Har a yanzu kuka take wane dan shi aka turota k’afafunta har sun soma kumbura sunyi jaa dan azaba, yi tayi kamar bata jisa ba, bulalan ya d’aga as if ze sake zaneta “dan Allah kayi hak’uri zan shiga.”
“Oya!” Yayi commanding nata, motar ta bud’e ta shiga shima haka sede har a yanzu bata bar kukan ba. “Kuma kimin shiru wallahi in bakiyi ba sena k’ara miki wanda yafi wannan” kukan tacigaba dayi “aww! Baza kiyi shirun ba kenan?”
“Zanyi dan Allah kayi hak’uri.”
“Oya yi shirun kuma wallahi kikaje kika fad’awa Baba na dakeki ya kirani yamin suratan banza zakiga abinda zan miki, kinfi kowa sani na” a da tanada niyyar sanar da Baba abinda yayi mata amman jin ya kashe mata warning ta fasa saboda tasan halin Ibraheem sarai mugu ne first class ma kuwa. Haka tana ta sobbing har suka samu suka isa gida aranta tana meh tunanin wani abin zata yimasa ta rama.


Tana fitowa daga motan ta buga murfin wane zata b’alla ko uffan bece mata shide da murfin motansa ya b’alle da seta raina ma kanta wayo. Karo taci da Baaba A’ee gbam! “meh haka mutum na tafiya bai ganin gabansa” tayi maganan ba tare da tasan da wa ma sukaci karon ba.
“Toh Zeezee lafiya dai koh?”
“Aww Baaba kece sannu nasha ma ‘yan iskan almajiran nan ne.”
“Sannu Zeezee ba gaisuwa?”
“Nikam da Allah kullum gaisuwa baki gajiya da amsawa ne?” Bata jira jin meh A’ee zata ce ba ta wuce ciki, baki A’ee ta tab’e tace, “Allah shiryeki Zeezee.”

**** _8:17PM_
Tailor’n su ya iso nan kowa ya fito da zannuwansa bayan ya gama a’aunasu suka zab’i styles nasu Baba ya bada advance har tailor yazo tafiya Baba ya tsayar dashi, “yauwa Shaheed d’inkin nace ka tabbata seka gama dana Zeezee kafin ka fara na sauran saboda kaga ita yarinya ce, su ko ba kayan sallah zasu iya yin sallan ka gane ai?”
“Eh Alhj zan fara da nata in nasamu nayi koda biyu ne a natan sena tab’a na ‘yan uwan nata.”
“O’o ni seka gama min duka six d’in” Zeezee tayi chipping in.
“Bakida hankali? Mu kuma fa? Shaheed please kar ka saurareta” cewar Mariam.
“Lallai sannu toh se an gama da natan za’a tab’a naku maras kunya kawai” Baba ya sanar da ita.
“Allah sarki Baba-” inji Yasmeen.
“Allah sarkin K’aniya, sam ku baku san meh kara wa k’anwarku ba? Se an gama nata a fara da naku ka jini ai Shaheed? Se mun jika nan da 2 weeks d’in.”



*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 14



~* ~* ~*
Da Asubaah Mama da kanta tazo tada Zeezee daga bacci don yin Sallah ‘cause anytime ta tura sauran bata tashi. Gbam! Gbam! Gbam! “Zeezee bazaki tashi ki bud’e k’ofar bane?” Murya cike da gyangyad’i tace, “waikam ba naji ba? Ai zan tashi.”
“Shine nace ki bud’en k’ofan.”
“Toh wai ki shigo kiyi meh Mama? Ai zan tashi.”
“In baki tashi ba ma keda Allan ki” daga nan ta wuce d’akinta. Jin shiru hakan ya tabbatarwa Zeezee Mama ta tafi, “ai wallahi bazan tashin ba” daga fad’an haka taja comforter ta cigaba da baccinta se 7:00AM ta tashi tayi sallan ta sake komawa bacci, kasancewar yau Sunday ba school. Se 10:30AM ta tashi tayi wanka tasa wani A-shaped gown nata ta fito, a parlour ta tarar da Baba ta gaishesa sannan ta wuce kitchen dan neman abin karin kumallo chan taci karo da duka sauran ‘yan gidan nasu Mama kad’ai ta gaisar, dama on normal basis tana gaishe da Ibraheem ma amman data tuna da dukan daya mata jiya se ta fasa.
“Ina breakfast d’ina?” Banza da ita duka sukayi Mama ce ta mik’a mata flask natan tace, “in bazaki gaisar da sauran ba Ya Ibraheem fah?” Baki ta turo sannan ta watsa mai harara dan ko kallonta baiyi “ina kwana?” Tace chan k’asa-k’asa almost like whispering, ganin yak’i amsawa yayi banza da ita tace, “tafi nono fari karka amsan” dai-dai zata karb’i flask nata Mama ta rik’e “amman fa yau akwai aiki kinga Baaba bata ji dad’in jikinta ba so bata samu daman zuwa ba yau adalilin haka na rabawa kowa aikin da zeyi, naki aikin share site nasu Ya Ibraheem da musu mopping neh” seda tabari flask na abincin nata ya shiga hannunta tace, “chabd’i! Ni ce zan share musu d’aki meh sauran kuma zasuyi? D’akina kawai zan share kowa ya share nasa.”
“Haka kika ce?” Mama ta tambayeta.

“Eh mana ni ba abinda zan share musu, Allah yayi wa kowa hannu” ta kama hanyan fita daga fad’an haka.
“Tsaya ke! Kika gama breakfast d’in kizo zan aike ki shago” Ibraheem yayi maganar in a serious tone. Shiru tayi kamar bata jisa ba, “ko baki jini bane?”
“Naji” ta watsa mai harara ganin bai kallonta nan ta juya ta hau gun-guni “shikenan shi baida aiki se aikan mutum shago wallahi bazan jeba.”

_Back in the kitchen..._
“Wai Mama kinajin yarinyan nan bazaki buge bakinta ba?” Cewar Yasmeen.
“Barta tanayi wa kanta ne ai ba inda rashin kunya ze kai mutum se halaka Omar Baba na kayi hak’uri ka share muku kaji? Yi hak’uri.”
“Mama wallahi haushi kike ban in kince tana yi wa kantan nan duka ne be isheta ba.”
“Barta de ba muna nan tare da ita a gidan nan ba? Zan gyara mata zama” Ibraheem yayi maganan tare da miqewa haka ranan kowa na aiki banda Zeezee dake kallon disney channel, ita gabad’aya ma tama manta Ibraheem yace ze aike ta shiko yana sane time ya bata inhar takai 12noon bata zo ba ita da shi ne!

11:56AM aiken da Ibraheem ze mata yayi ringing a kanta firgit ta mik’e duk kalan rashin kunyan Zeezee tana d’an shakkan Ibraheem sanin halinsa.
“Gani” tace alokacin da ta shiga d’akin nasu bata damu da miyar wa Omar shara bayan da tayi ba, gindin tsintsiyan ya seta k’afafunta ya rabga mata “bakiga shara nake bane da zaki shigo kina miyar min da aiki baya?”
“Wayyo Allah! Allah ya isa na ni nasan kana sharan ne” kunnenta ya kama “meh kika ce?”
“Babu dan Allah kayi hak’uri” murd’a kunnen nata ya shiga yi tana ihu Ibraheem dake zaune yana kallonsu ko k’ala bece ba “ni kike jawa Allah ya isa?” Tana hawaye tace, “a’a na tuba dan Allah kayi hak’uri.” Se anan ya saketa ta shiga share hawayenta N2000 Ibraheem ya mik’a mata “siya min Glo na 2k.”
“Ya nima ka bani N500.”
“Da uban rashin kunyan kin zan baki N500? In kinason kici arziki na ki dena yimin rashin kunya now b’ace min daga gani” bata ce dashi komi ba ta zarce d’akin Baba takai k’ara nan ya turata ta kira Ibraheem d’in.
“Uhm Ibraheem Baba na kanada N1,000 kabani?” Baba yayi maganar cike da dabara.
“Eh Baba” nan ya zaro wallet nasa ya mik’a mai “shikenan?”
“Eh shikenan nagode koh?”
“Ba komai Baba kekuma kije ki siyomin ina jiranki.”
“Wai toh ba na jiba haa’a!” Bayan ficewan Ibraheem Baba ya mik’a mata dubu d’ayan, “saura kuma kije kice dubun daya banin na baki ba ruwa na.”
“Barin fad’a ba Baba nagode” nan da nan taje ta sai masa katin itama ta sai nata.****


Da Azahar friends na Ibraheem suka zo bayan sun dawo daga sallan Azahar ya tura Yasmeen ta kira Zeezee, seda ta gama b’ata mai lokaci tazo tana tura baki, “meh?”
Kallo ya galla mata da kanta ta gyara zancen nata, “na’am Ya ka kirani.”
“Se kuma dana kiraki baki iya gaisuwa bako?” Kallo tabi friends nasan dashi Allah yaso ba mumuna cikinku da kunga buro-uba tayi maganan a zuci.
“Ina wuninku” tayi murmuring, k’asa-k’asa suka amsa.
“Kije ki kawo musu drinks sannan Yasmeen tayi guiding naki ki dafa mana indomie tunda ba ayi abinci ba tukuna.”
“Ni? In dafa muku indomie? Gaskia a’a Ya, ni ban ma iya dafawa ba kuma koda na iya ma sekace wata boyi-boyi.”
“Magana kike? nace kice Yasmeen tayi guiding naki.”
“Ni wallahi Ya...” ta hau bubbuga k’afa tana tura baki “ni bazan dafa ba ina kallon shake it up kawai kuyi hak’uri zan kawo muku snacks d’ina na school kusha da drinks d’in.” Dariya sosai ta sa friends nasan d’aya daga cikinsu yace, “Mazaa kabar baby sis nakan nan kawai dama ba yunwa muke ji ba, kawo mana ruwan kawai kinji?”
“Yauwa Ya Suleiman” shide Ibraheem bece komi ba tunanin kalan dukan da ze mata kawai yake, haka taje ta d’ibo musu drinks da snacks nata ta jera musu kan tray dai-dai tazo ajiwa kenan Ibraheem ya cafke hannunta tare da sa mata nank’washi meh uban zafi aka, k’ara ta saki tare da jan Alah ya isa nan ya k’ara mata “meh kikace?” Tana kuka tace,
“Nace kayi hak’uri wallahi sabon kitso ne a kaina.”

“Mazaa let her be please” cewar d’aya daga cikin friends nasan.
“No kubar ni da ita me kika gama cewa d’azu?”
“Babu, Ya dan Allah kayi hak’uri wallahi bazan k’ara ba wayyo kaina.” Kunnenta ya kama ya murgud’a da k’arfi.
“Argghh!” Ta saki k’ara “wayyo Baba na dan Allah kayi hak’hri.”
“In sake saki aiki kice min baza kiyi ba kiga abinda zan miki marasa kunya kawai” ya saketa “get out!” Da

14 / 98