YAR GATA CE COMPLETE HAUSA NOVELS BY MIEMIEBEE.txt

Author :  MIEMIEBEE Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   5 / 98

12K to 15K   out of 291.7K words

guda biyu akai kafin nan Yasmeen kije ki had’a mata tea sauran ki d’ibar mata madara kisha kuma.”
Kamar wacce zatayi kuka Mariam tace, “wallahi Baba ko an dafa mata Indomie’n ba ci take ba haka jiya ma k’arshenta zubar wa akayi kawai dan tasa nutum aiki ne.”
“Toh ina ruwanki ai bake kike siya ba, shegen rashin son aiki maza tashi yaso kuka gama seku koma baccin, ku tashi mana!” A sanyaye suka miqe suka nufa bayi dan washing up se gunguni suke.

~* ~* Tea’n ta me kauri Yasmeen ta kawo mata tana zaune kan dining table nata da chair ta shanye tas, a rayuwa Zeezee akwai son tea bayan 25 minutes Mariam dake ta kumbure kumbure har yanzu ta kawo wa Zeezee abincin. As expected Zeezee ta jagualgwala taci kad’an ta k’ara mai abinta.

_09:34AM_
Su Mama na a kitchen suna had’a breakfast, bayan Yasmeen tayi wa Zeezee wanka ta saci jiki tayi d’akinsu Mariam daidai gaban dressing mirror ta tsaya ta fara bi ta kan cosmetics d’in tana applying ita a dole tana kwalya, kaca-kaca tayi da kayakin kwalyan, data kama sharpening eye pencil seda taga k’arshen shi, data waina jan baki seda ya karye, liquid eyeliner ta bud’e ta zana a saman girarta saura ta zagar a k’asa. Komi seda ta b’ata sannan ta masu wanka da turare, daidai tazo fitowa kenan tayi kacib’us da Mariam dake shigowa. Hannu bibbiyu Mariam ta aza kan bakinta da taga fuskan Zeezee.
“Ki masha min in wuce” cewar Zeezee tana k’ok’arin kare fuskanta.
“Da kayan kwalyan wa kika-” bata k’are maganan ba idanunta suka sauqa kan ta’addancin da Zeezee ta masu da kayan kwalya. Fincikota tayi da hannu takai ta gaban mirron.

“Meh amfanin haka? Ban hanaki tab’a min kayan kwalya ba?” Ganin haka Zeezee tasa ihu wane ana cire mata rai, Baba da Mama ne suka shigo a tare a cewansu ma ko Zeezee ta fad’i ne. Zeezee na ganin Baba ta ruga aguje wajensa ya d’agata sama “Baba kaga Adda Mariam koh?”
“Me haka a fuskan ki Zeezee?” Mama ta tambaya.
“Mama dubi fa, kalli abinda ta min da kayan kwalya komai seda ta b’ata kuma da gangan take.”
“Taya zaki ce da gangan?” Cewar Baba, “bakiga yarinya ce ba? A jinki in tasan whats right and wrong zata yi abinda tayin neh?”
“Amman fa Baba this is not her first time kwanaki da tayi seda na mata magana” tayi maganan idanunta na cikowa da hawaye.
“Toh Mariam kema seda na fad’a miki ki riga sa kayan kwalyan naki cikin wardrobe kina rufewa achan Zeezee barata iya tab’awa ba.”

“Shikenan Zeezee?” Kai ta gyad’a a shagwab’ance sannan tace, “zan sha tea.”
“Tea? Ko a dafa miki Indomie kina jin yunwa ne?” Ya matse cikinta yana mata cakul-kuli, nan ta hau dariya.
“Eh” ta basa amsa.
“Oya Mariam miqe ki je ki dafa mata Indomie da k’wanta guda biyu akai kafin nan Yasmeen kije ki had’a mata tea sauran ki d’ibar mata madara kisha kuma.”
Kamar wacce zatayi kuka Mariam tace, “wallahi Baba ko an dafa mata Indomie’n ba ci take ba haka jiya ma k’arshenta zubar wa akayi kawai dan tasa nutum aiki ne.”
“Toh ina ruwanki ai bake kike siya ba, shegen rashin son aiki maza tashi yaso kuka gama seku koma baccin, ku tashi mana!” A sanyaye suka miqe suka nufa bayi dan washing up se gunguni suke.

~* ~* Tea’n ta me kauri Yasmeen ta kawo mata tana zaune kan dining table nata da chair ta shanye tas, a rayuwa Zeezee akwai son tea bayan 25 minutes Mariam dake ta kumbure kumbure har yanzu ta kawo wa Zeezee abincin. As expected Zeezee ta jagualgwala taci kad’an ta k’ara mai abinta.

_09:34AM_
Su Mama na a kitchen suna had’a breakfast, bayan Yasmeen tayi wa Zeezee wanka ta saci jiki tayi d’akinsu Mariam daidai gaban dressing mirror ta tsaya ta fara bi ta kan cosmetics d’in tana applying ita a dole tana kwalya, kaca-kaca tayi da kayakin kwalyan, data kama sharpening eye pencil seda taga k’arshen shi, data waina jan baki seda ya karye, liquid eyeliner ta bud’e ta zana a saman girarta saura ta zagar a k’asa. Komi seda ta b’ata sannan ta masu wanka da turare, daidai tazo fitowa kenan tayi kacib’us da Mariam dake shigowa. Hannu bibbiyu Mariam ta aza kan bakinta da taga fuskan Zeezee.
“Ki masha min in wuce” cewar Zeezee tana k’ok’arin kare fuskanta.
“Da kayan kwalyan wa kika-” bata k’are maganan ba idanunta suka sauqa kan ta’addancin da Zeezee ta masu da kayan kwalya. Fincikota tayi da hannu takai ta gaban mirron.

“Meh amfanin haka? Ban hanaki tab’a min kayan kwalya ba?” Ganin haka Zeezee tasa ihu wane ana cire mata rai, Baba da Mama ne suka shigo a tare a cewansu ma ko Zeezee ta fad’i ne. Zeezee na ganin Baba ta ruga aguje wajensa ya d’agata sama “Baba kaga Adda Mariam koh?”
“Me haka a fuskan ki Zeezee?” Mama ta tambaya.
“Mama dubi fa, kalli abinda ta min da kayan kwalya komai seda ta b’ata kuma da gangan take.”
“Taya zaki ce da gangan?” Cewar Baba, “bakiga yarinya ce ba? A jinki in tasan whats right and wrong zata yi abinda tayin neh?”
“Amman fa Baba this is not her first time kwanaki da tayi seda na mata magana” tayi maganan idanunta na cikowa da hawaye.
“Toh Mariam kema seda na fad’a miki ki riga sa kayan kwalyan naki cikin wardrobe kina rufewa achan Zeezee barata iya tab’awa ba.”

“Ahtoh! In har dagaske kike, kuma me kika ma Zeezee take ihu?”
“Duka na tayi a zuciya na.”
“A zuciyanki koh? Yi hak’uri, wallahi Mariam ki kiyaye ni sau biyu nake miki magana kenan yau na uku duka ne.”
“Alhj amman Zeezee’n ma kai mata magana ta rage b’arna ko jiya a islamiyya seda ta yage wa Mrs. Bee littafi.”
“Lokacin ta ne ba maganan da zan mata ke Allah kad’ai yasan kalan b’arnan da kikayi kema” yana kaiwa nan ya fice k’arisawa Mama tayi kusa da Mariam da har ta fara kuka tana bata hak’uri haka seda Mama ta bata dubu biyu tayi shiru.

Su Baba suna zaune a tsakar gida da Zeezee’nsa se hayewa jikinsa take tana wasa wane d’an biri, Ibraheem ne ya dawo daga yawonsa, da wayansa riqe hannunsa ya bashi full attention nasa a haka har ya k’arasa d’aki Zeezee na ganin shigewan sa ta taso daga jikin Baba tabi bayansa. Zaune ta tarar dashi kan couch dake d’akinsu a hankali taje ta zauna gefensa ko uffan bece mata ba se chatting nasa yake yana murmusawa time-to-time, da Zeezee ta d’anyi observing nasa seta gane chatting yake a whatsapp. “Ya Ibyaheem da whashapp.” tace da shi.
“Ya akayi Zeezee?”
“Ya Ibyaheem zanyi game.”
“A’a Zeezee ni gaskiya bara ki kashe min battery ba duk games d’in ma gogewa zanyi” ba tare da tace mai komai ba ta miqe ta kama tafiya “k’ara na zaki kai gun Baba koh? Zo in sa miki toh.” Ko ta kansa batayi ba taje ta samu Baba ta fara kuka “wa ya tab’a min k’anwa?”
“Ya Ibyaheem ne.”
“Meh ya miki shi kuma?”
“Yak’i bani wayanshi nayi game.”
“Ibraheem! Ibraheem!”
“Na’am Baba!” ya amsa tare da goge dukka games na wayan nasa sannan ya fito. “Gani Baba” ya durqusa gefe guda.
“Ina wayan naka? Bata tayi game d’in.”
“Baba nifa ba game a waya na.”
“Ka goge kenan?” Kafin Ibraheem ya amsa Zeezee tace, “eh Baba yace min zeyi deleting.”
“Ni? Yaushe nace miki haka Zeezee?”
“A’a barshi Zeezee jeki amso wayan nasa.”
“Baba me zaka min da waya?”
“Downloading mata zanyi ba ka iya gogewa ba? In na sake installing seka sake gogewa kaine da asaran data dan ba shi ze hanani next in ka goge na kuma downloading ba, amso min wayan Zeezee.”

“Baba in na fita anjima zan tura a wayan friend d’ina wallahi ba nida data nima managing nakeyi.”
“Wannan kuma damuwan ka amso min Zeezee” haka Ibraheem naji yana gani Baba ya shiga playstore “wani game kikeso K’anwa ta?”
“Shubway churfers da plincess salon.”
“Zeezee har biyu Baba wallahi data na ze k’are.” Banza dashi Baba yayi yama Zeezee downloading duka sannan ta fara playing. “Kaje in ta gama zata kawo maka wayar.” Kamar wanda zeyi kuka Ibraheem ya kalli Baba sannan Zeezeen dake ta game nata ya miqe ya bar gidan ma gabad’aya.



*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
beeenovels.blogspot.co.ke

PAGE 05

*December, 2016*


_This page is in honour of *Fathooma Ali* a great fan I never knew I had. I have recieved your message, thank you so much for the love stay blessed Habibti #OneLove💕_


Game Zeezee tai tayi kamar ba gobe, dan kanta ta gaji da bugawa ta shiga photos tata kallon pictures saura kuma ta rik’a gogesu a takaice seda tayi mai battery low wayar ta mutu gabad’ai sannan ta kai mai wayan alokacin yana zaune a parlour a side nasu yana assignment nasa na Technical Drawing “Ya Ibyaheem ga wayan ka” ta fad’i tare da ajiye mai a gefensa ko kallonta beyi ba ya cigaba da abinda yake chan tace, “Ya Ibyaheem zane kake yi?” Nanma ko uffan be ce mata ba feeding bottle nata da ke rataye a wuyanta wanda tea ne had’e ciki ta d’aga zata bud’e dan sha. A garin haka tean da yake ciki ya zube kan zanen Ibraheem, “shikenan ai kin huta yanzu! Tashi ki ficemin daga kallo!” ya daka mata tsawa.
Lamo tayi tana kallonsa a yayinda hawaye ke ciko mata a ido, “baraki fita bane?! Ace mutum kullum se bad luck fice min! Yaso in Baban naki ya dawo ki fad’a mai, get out!” kuka ta soma ba makawa amman ko a jikinsa, kamar kyaftawan ido ya fisgota da hannu ya direta bakin k’ofar tare da rufewa harda kwad’o. Kuka Zeezee ta ringa yi wajen haka dan kanta tayi shiru sabida Baba yafita bai gida Mama kuwa nacan d’akinta tana kwance. Mariam dake tsakar gida ko a kwalan rigarta ta lalasheta daman acike take da ita for what she did to her makeup items earlier.

Chan da ta gama kukan ta k’arisa wajen garriage inda takejin hayaniyan su Omar. Zaune ta tarar dasu yana ma Yasmeen homework nata na ‘paper mache.’ Waje ta nema ta zauna kusa dasu itama sannan tace, “Ya Omal meh kukeyi?” Kamar wanda bare amsa taba yace, “homework.”
“Ya Omal paper ne kuka dafa?”
“Eh da Allah shegen tambayoyi sekace ‘yar jarida kinga baraki iya yin shiru ba find your exit” daga nan Zeezee bata sake cewa komai ba sede duk abinda suke tana observing nasu.
K’arfe uku suka gama shiri suka wuce islamiyya nan Zeezee ta samu kanta, da full confidence nata taje tana k’ok’arin bud’e k’ofa only to find it locked kamar Mama tasan b’arna data saba zatayi any moment yayyun nata suka barta ita kad’ai a gida, dalilin rufe k’ofan d’akin datayi kenan don restraining nata.

“Mama ki bud’emin k’ofa.” Banza da ita Mama dake shirin bacci tayi.
“Mama ki bud’e.” tayi maganan tana jijjik’a k’ofan.
“Saboda kije kiyi b’arna ba taho mu kwanta in bara ki kwanta ba ga kayakin wasan ki can se kiyi wasa.”
“O’o ni ki bud’e min.”
“Barin bud’en ba mab’arnaciya kawai.” Kuka Zeezee ta soma rusawa wajen tun Mama tana ignoring nata har ya soma daminta haka seda ta bud’e mata k’ofar bayan jan kunnen data mata na karta tab’a kayan yayyun ta. Like a good girl tace ita wasan ta zatayi. Mama na maida k’ofanta Zeezee ta zarce d’akinsu Mariam luckily yau sun mance basu rufe k’ofan su ba nan ta samu ta shiga. Bata nufi ko ina ba cikin d’akin se inda suke jera school bags nasu, na Yasmeen taja ta bud’e ta ciro notebook d’aya sannan ta fice izuwa kitchen inda ta nemo tukunya ta loda ruwa ciki sannan ta bud’e littafin Yasmeen wanda ya kasance Mathematics ta soma yagewa tana kacancanawa tana sawa cikin kwanon in aka tambayeta wai haka taga su Omar sunyi d’azu. Hakan ta cigaba da yi seda taci rabin littafin sannan ta ajiye ta d’au tukunyar ta aza akan charcoal stove, ashana ta shiga nema wanda bata samu ba saboda chan saman cupboard Mama ke ajiyewa. Dan kanta ta hak’ura bayan ‘yan mintuna ta sauk’e tukunyan sannan ta d’ibo cups da plates da saucers duk bibbiyu ta zauna tsakar gidan itama a dole zatayi paper mache.

Moulding jikin cups d’in ta shiga yi tana manna papers d’in jiki amman ina se sumb’ilewa suke, haka ba fashi ta tayi sannan data gama taje ta jerasu layi d’aya da inda Omar ya ajiye wa Yasmeen nata.

_5:30PM_
Anan yaran suka dawo daga islamiyya se Allah Allah Yasmeen ke ta ajiye jakarta ta duba home work nata ko yayi dan gobe Monday zasuyi submitting. Dad’i sosai taji ganin Zeezee bata tab’a mata abinta ba sede ganin wasu cups datayi a gefe bayan data gama duba nata seta d’au na Zeezee tana dariya “wai! Ji shirme itama wai a dole tayi pap-” maganan da Yasmeen bata k’arisa ba kenan ganin handwriting nata jikin paper’n data lura da kyau kuwa taga Mathematics note nata ne. Salati ta saki sannan tasa gudu zuwa d’akinsu ta shiga neman Maths note nata sede its nowhere to be found. Dam idanta ya cike da hawaye ta kama hanyan d’akin Mama dan kai k’ara, tana fitowa taga rabin Maths note nata a k’asa gabad’ai ya canza kamanni tunanin irin dukan da Mr. Chika (Maths teacher’nsu) ze mata kawai take. D’akin Mama ta nufa tana kuka, Zeezee da tasan this was comig tuni taje ta lab’e jikin Mama.

“Ya haka Yasmeen waya tab’aki?” Cikin sautin kuka tace, “Mama kalli fah, kalli abinda Zeezee tamin da Maths notebook d’ina” se kuma ta fashe da kuka. Amsan littafin Mama tayi ta k’are mai kallo sannan ta mai da kallonta kan Zeezee datayi tsit, daga bisani tace;
“Mama bani bane.”
“In ba keba ai nice, mesa bakiya ji ne iyye? Meh amfanin hakan? Wallahi ga ta Yasmeen kimata duk abinda zaki mata nan gaba ko cewa akai ta tab’a jakarki barata tab’a ba” da hannu Yasmeen ta finciko Zeezee ta nad’a mata na jaki, Mama na kallonsu batace komai ba se anan Yasmeen taji tad’an huce. Kuka Zeezee take wane dan shi aka kawota duniya. Chan ta wuce wajen garriage ta cigaba da kukan har tazo tayi shiru, tana jin k’aran motan Baba ta soma sabon kukan aiko parking na arziki Baba beyi ba yafito yana tambayarta ita da waye. Nishinta har wani sama sama yake tace, “Mam.. Mama ne tasa Yasmeen tamin duka.”

“Duka?! A dalilin meh? Muje ina Maman naku?” tun daga gun ya shiga k’wala wa Mama kira.
“Alhj lafiya haka?” Tayi maganan tana k’ok’arin fitowa daga kitchen.
“Me kika sa Yasmeen ta mata? Yasmeen! Yasmeen! Kema fito nan.” Nan da nan ta fito rik’e da Maths note nata.
“Ehen ina jinki kibani k’wararren dalilin da zaisa kice Yasmeen ta daka min k’anwa.”
“Yasmeen mik’a mishi littafin naki” cewar Mama, nan Yasmeen ta miqa wa Baba bayan daya k’are wa littafin kallo yace, “wa yayi maki haka da littafin?”
“Zeezee ce.”
“Taya kika san itan ce? A idonki tayi ne?”
“Alhj wani irin magana kake haka? Mu biyu da ita aka bari a gidan nan ko ni kakeson kace nayi wannan b’arna?”
“Ba abinda nake nufi ba kenan abinda nake nufi shine ku dena zato tunda ba kamata kukayi in the process ba, ko ke kikayi Zeezee?” Kai ta girgiza alaman a’a. “Toh baga erin saba kun kama kun d’au alhak’in yarinya a banza.”

“Baba wallahi Zeezee ce, ita tamin kuma Maths teacher’n mu duka na zeyi wallahi.”
“Naji gobe zamu je makarantar naku na masa bayani amman koda wasa karki kuskura ki sake d’aga hannu ki tab’a Zeezee ever!”
“Meh kake nufi da hakan Alhj? Baka yarda Zeezee ce tayi wannan tabargaza ba kenan ko meh?”
“Taya zan yarda bayan ban kamata red-handed ba?”
“Lallai kam!” Mama ta had’e hannunta biyu ta dafe a ciki “baka yarda bama bale ace ka ja mata kunne koh?”
“A dalilin me zan ja mata kunne, ba abinda zan mata.”
“Toh wallahi Alhj ka cigaba kai da kanka wataran zakayi nadaman abinda kakeyi, yarinya ace bata jin maganan kowa se naka Allah kyauta!”

~* ~*
Da daddare bayan Sallan Isha’i Baba da Mama suna d’akinsu yaran suma haka a d’akinsu. Zeezee ne zaune a parlour ta baje kayakin wasanta se wasa take chan da taji ta gaji ta miqe ta nufa d’akinsu Mariam inda duk yayyun nata suke mik’e suna kallo a laptop na Ibraheem ba tare da tace dasu komai ba ta jawo k’ofan tayi d’akin Mama taje ta samu Baba.
“Baba zan kayyi fyozen (Frozen.)”
“Toh je kice wa Ibraheem ya sa miki.”
“Toh” tace sannan taje ta samu Ibraheem. “Ya Ibyaheem Baba yace kasha min fyozen.”
“Bara asa ba ke baki tashi kallo se kinga mutane sunayi toh bara’a sa ba, se mun gama za’a sa maki.” Ibraheem yayi maganar ba tare da ya kalli

5 / 98