Author : MIEMIEBEE Category : Romantic Hausa Novels
isa a tab’a yarinyan nan ba ka hau ma mutum surutu? Kalli kan Samha nan ba kitso neba akai? Amman kai kace wai bara’a tab’a ba se a aske gashin ai kowa ya huta.”
“Bara a aske ba bara kuma ayi mata kitson ba haka za’a bar gashin ku kuma Maman Sudeis da saura ina ganin ku da hankali amman kuna ganin Hafsah na rashin hankali baraku mata magana ba?”
“Kayi hak’uri Baban Zeezee hakan bare sake faruwa ba” cewar Ummu HH.
“Allah kyauta” ya fad’i tare da nufan ciki, binsa Mama tayi da harara tana meh mamakin hali irin na Baba, kap cikin yaranta ba wanda Baba ya tab’ayi mai abu haka banda Zeezee. A time na Yasmeen ma kam sata yake a mota ya kaisu gidan kitso yace ayi ma Yasmeen amman na Zeezee yace bara’a tab’a kanta ba? Toh Allah kyauta!
Hira kad’an suka tab’a da friends nata tayi masu rakiya sannan ta dawo ciki.
Ita a zaton ta ma Baba d’akinsa yake ashe a nata yake ya zauna kan gado yana wasa wa Zeezee, tana shiga ta gansa kafin ta juya ya kira sunanta chak ta tsaya tare da kewayo wa. “Gani” ta fad’i rai a b’ace sam ba annuri a fuskarta, daya gano hakan seya saki murmushi ya gyara zamansa kan gadon.
“Haba! Hajiya Hafsah ta ya da haka kuma?” Banza dashi tayi. “Maman Zeezee dake fa nake.”
“Alhj kaga zan d’aura girki in wani abun kake buk’ata ka fad’amin inada abinyi.” tayi maganan in an I don’t care manner.
“Zo ki zauna anan” yayi mata nuni da space dake gefensa nan ma tayi banza dashi “yi hak’uri mana Maman Zeezee nayi kuskure toh amman kiyi hak’uri.” Sexy long eyes nata wanda Zeezee tayi gadonsu ta d’ago tana kallonsa a yayinda ya kashe mata ido d’aya “yi hak’uri my wonderful Wife.” Batasan a lokacinda ta saki murmushi ba taje ta zauna gefensan kamar yadda ya buk’ata. Dad’i sosai yaji “yauwa ko kefa tawan?”
“Uhm” tayi murmuring.
“Nace kafin ki shiga kitchen kid’an bawa Zeezee mama inason mud’an fita strolling da ita.”
“Wai Alhj ni shikenan kullum cikin bawa Zeezee mama, banida aikin da yafi wannan! Ni gaskiya wallahi na gaji a had’a mata da madara, barin iya ba”
“Kin gaji? Ke bakisan farillah neba shayar da yaro?”
“Eh nasani amman ai ba’ace koda yaushe ba, abanza ta zubar min da nono ta mai min dasu slippers, ni gaskiya banaso ina maintaining jiki na.”
“Ahh lallai fa Hafsah sannu! Sekace bana biyanki albashi k’arshen wata kamar yadda muslinci ya tanadar as kyautatawa? Ko badan haka bama baraki shayar da ‘yarki ba?” Zata sake magana ya dakatar da ita “yimin shiru ki bata muyi mu fita kema kiyi abinda ke gabanki.” Harararsa tayi ta gefen ido sannan ta amshe Zeezee ta shiga bata mama seda ya tabbata Zeezee tayi nak ya yarda Mama ta zare abinta sannan suka fice da Zeezee.
Haka nan rayuwa ta cigaba da kasancewa, family’n Alhj Isma’il Yosouf komi Zeezee, ba’a tashi kama wa Zeezee kai se in an tabbata Baba ya fita dan kuwa in yana gida bayi bari. Ahaka yarinya take girma da kuma tashi cikin gata da tsantsan so gun mahaifinta tun tana yarinya ya saba mata da samun duk wani abinda takeso.
There was a time a gidan biki Mama taje da Zeezee, Zeezee taga kayan wasa gun wani yaro ta ringa kuka tana shure k’afafu itama tanaso, Baba najin haka ya ari sample na kayan wasan yaje ya siyo mata exactly irinsa har guda biyu, itade Mama tayi magana har ta gaji, ya zamanto ta zuba mai ido kawai yanzu. Shi da kansa wataran zeyi nadaman abinda yake ma Zeezee.
*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com
PAGE 04
★★★
A kwana a tashi babu wuya game rai, Zeezee nada shekara d’aya (1 year) tal a duniya yanzu! Yarinya son kowa k’in wanda ya rasa, sede Mama bata fita da ita unguwa ko gidan biki ba idon kowa na akanta, ga kaya masha Allah tun tana Baby se to-match ake sa mata kasancewar Mama ‘yar gayu ce ajin farko amma wani abu Zeezee se tashi take da uban k’uiya, banda ‘yan gidansu bata san kowa ba again, a cikin ‘yan gidan nasu ma wani sa’in zab’a take, atimes in tana hannun Baba ko hannun Mama batason zuwa.
Tunda Baba yake be tab’a celebrating birthday’n yaransa ba se akan na Zeezee. Grand birthday party had’ad’d’e ya tsara wa Zeezee lokacinda ta cika 1 year. D’imemen cake ya sai mata akayi celebrating, families ne da ‘yan unguwan da basu fi a k’irga ba se friends nasu Mariam suka ziyarci party’n. Su Mariam se palli ake anje an gayyato friends gabad’ai ana ta rawan kai. Se a ranan suke marmarin Zeezee kan ba gobe saboda ganin yadda tayi kyau. Har dan haka suka so yin fad’a ita da Omar. Sosai Zeezee tayi kyau ranan, an gyara mata gashinta cikin colourful ribbons, bugu da k’ari kuma ga yadda glassy green princess ball gown nata ya mata kyau da silver crown nata. Pictures suka sha sosai, suka ci suka sha suka kuma chashe!
_Wannan ke nan!_
Tun da Zeezee ta cika shekara d’aya da watanni biyar a duniya Mama ta soma zancen yayeta amman inaaa Baba ya hana wai sam se Zeezee ta k’ara watanni uku ko hud’u kamar yadda muslinci ya tanadar sannan ze yarda a yayeta.
“Haba Alhj dan Allah! Yarinyan nan de tayi wayo ko a yanzu aka yayeta ba’ayi depriving nata komi ba, aiko a muslincen ma cewa akayi 18-20 months ba’a ce lallai se yaro ya cika 20 months d’inba tukuna kuma yarinyan nan is 17 months now me marabar 17 da 18?” Baba da yayi shiru yana sauraronta tun da ta fara wannan zuba yace;
“Ki fad’i koma meh Hafsah, kin ga dama kita bayani daga nan har gobe but believe me wallahi se yarinyan nan ta cika watanni ashirin (20) d’innan ki yayeta.” Yayi maganan tare da miqewa da Zeezee a hannunsa.
“Ai sede in kai zaka cigaba da shayar da ita, yarinya gata doguwa ina ma ace wacce bata girma ne! Ni wallahi har kunyan cireta nake cikin jama’a zan shayar da ita, mutane se gani suke kamar ma tayi girma a shayar da ita saboda tsawonta.”
“Awww! Yanzu Hafsah sabida bakin jama’a kikeson tauye wa Zeezee hak’k’inta? Da kyau ban yarda ki sake fita gidan suna ko biki ba har se in kin yaye Zeezee kuma ki shirya nan da anjima zan kawo ta ki bata mama seta k’oshi sannan kiyi wani harkan gabanki.” Be jira me Mama zata sake cewa ba yayi tafiyarsa.
Anyi haka da kwana uku tafiya ya tasowa Baba zasa Lagos saro laces da zannuwa da sauran abubuwa, ranar Asabar tafiyar ta kama. Duk iyalan nasa suna a garriage suna jiran ya shiga mota su mai ‘Allah kare’ amman ina seya kama hanyan zuwa mota ya dawo ya karb’e Zeezee, itama data gane tafiya zeyi se kuka take tana ‘Baba’ duk jikin sa yabi ya mutu seji yake kan ya fasa tafiya if only an yaye ta da yayi tafiyan da ita. Da k’yar ya iya ya shiga mota yayi wining glass k’asa yana kallon yadda Zeezee keta kuka hannun Mama.
“Toh ki lalasheta mana Hafsah!”
“Alhj wani irin lalashi ne ban ma yarinyan nan ba? Ai inba wai tafiya kayi ba barata bar kukan ba.”
“Zeezee na yi hak’uri kinji barin dad’e ba zan dawo.” Cikin kuka take ta fad’in “Baba... Baba... Baba.”
“Toh wallahi Hafsah sauran bayan tafiya na ki yaye Zeezee ki jira kiga abinda zan miki.” Shiru tayi batace koami ba, “dake fa nake magana!”
“Yanzu Alhj nace wani abu ne? Allah dawo da kai lafiya.”
“Ameen, kuma kar ki barta da yunwa, Ibraheem, Mariam nabar Zeezee a kulawanku in wani abu ya sameta ban yafe ba.”
“Toh Baba Allah ya kare hanya ya dawo da kai lafiya” yaran suka fad’i a tare. D’ari biyar-biyar ya bisu dashi sannan ya tada mota nan fa Zeezee ta fara sabon kuka ahaka Mama tayi ciki da ita. Yau Baba ya tafi washegari Mama ta yaye Zeezee, yarinya data saba kowani minti shan nono kam seji take duniyar ma gabad’ai ba dad’i tata kukan ‘mama... mama’ ina sede Mama ta d’au abinci ta bata haka zata k’i chi da yamma Mama ta aika Ibraheem kasuwa ya siyo cerealac aka fara bawa Zeezee sam tak’i sha ita wai se mama seda yunwa yaci k’aniyanta ta amince tasha cerealac d’in. Na yini biyu Zeezee ta saba dashi sede still atimes zata ta kukan mama ko tata sa hannunta cikin kayan Mama amman hakan bai sa Mama ta cire ta bata.
Baba kuwa tun tafiyarsa kullum se yayi video call yasa a had’a sa da Zeezee ya tai mata wasa tana dariya. Sati d’aya cus Baba yayi kamar yadda Mama tayi addu’a dan kuwa inhar ace before a week ya dawo tsab zece beji abinsa haka ba se an mayar wa Zeezee nono amman yanzu da ya kai sati Zeezeen kanta ta manta da nonon. Pounded yam and eghusi soup me rai da lafiya Mama ta shirya wa Baba sannan duk sukayi wanka suka shirya tsaf bayan kintsa gidan da sukayi sannan suka fara zaman jiran shigowan Baba.
Da misalin k’arfe 5:14PM Baba ya shigo Bauchi seda ya tsaya a Bauchi club ya siyo masu gashi sannan ya k’arasa gida duk sun yi murnan dawowan sa tare da mai sannu da zuwa sannan suka soma shiga da kayakin ciki, shide Baba Zeezee ya amshe yana ta mata wasa sosai itama taji dad’in dawowan Babanta.
*~ *~ Zaune suke duka a parlour se cin tsire suke suna sipping cool Maltinan su hankalin kowa na ayi a gama ci abud’e kaya. Baba dake tauna naman yana bawa Zeezee yaga alaman kamar yunwa takeji dan yadda take taci har in be sa mata a baki da wuri ba ta soma kuka. “Hafsah anya kuwa yarinyan nan ba yunwa takeji ba?”
“Yaushe ne ta sha cerealac natan?” Tayi maganan ba tare da tasan how and when ba.
“Dawo baya meh kikace?” Baba yayi maganan cike da k’in gaskata abinda kunnensa suka jiye mai. Nan fa Mama ta shiga kame-kame tayi tsit ta kasa cewa komai. “Dake fa nake Hafsah, meh kikace?”
“Alhj...” Ta kasa k’arisa maganan.
“Yayeta kikayi koh?” Shiru... “Nace yayeta kikayi ko?!” Yayi maganar cikin sautin tsawan da yasa Zeezee cusa kanta jikinsa. “Wai mesa bara’a tab’a gaya miki magana kiji bane iyyeh? Mena gaya miki kafin nayi tafiyar? Kinsan ko gun Allah kinada laifi koh?”
“Alhj kayi hak’uri” be sake cewa komai ba ya miqe ya bar musu wajen nan su Mariam duka suka dawo da kallonsu kan Mama. Ibraheem yace, “Mama wallahi da baki yaye wannan Zeezee ba a banza yanzu ran Baba ya b’aci d’an tsaraban da ya kawo manan ma seya fasa badawa.”
“D’an banza abinda ke daminka kenan koh? Mschw!” Nan itama Mama ta miqe tabi sahun Baba, d’akinta ta fara dubawa bata gansa ba hakan yasa ta nufa d’akinsa direct, k’ofar tasamu a rufe tayi knocking shiru Baban dake zaune bakin gado yana bawa Zeezee bobo yayi be amsa knock natan ba.
“Baban Zeezee na shigo?” Bata jira amsar sa ba ta bud’e k’ofar ta shige, ko d’ago kai ya kalleta beyi ba se feeding Zeezee yake. A hankali tazo ta zauna gefensa a bakin gadon tana kallon yadda Zeezee keta shan bobon sekuma ta bata tausayi taji dama bata yaye tan ban. “Baban Zeezee kayi hak’uri nayi laifi.” Kamar wanda bareyi magana ba yace;
“Ita ya kamata ki baiwa hak’uri bani ba” yayi maganar ba tare da ya d’aga kai ya kalle ta ba. Daga nan Mama bata sake fad’in komi ba seda Zeezee ta shanyen bobon sannan ta miqa hannu ta d’agota daga cinyan Baba ta aza ta kan nata. Hannu tasa ta ciro mamanta ta gwada kaiwa Zeezee duk Baba na kallonta bece ko uffan ba sede abin mamaki ko kallon nonon Zeezee bata son yi hasali kuka ma ta soma kai Baba ya kad’a yace, “tsami kika ringa shafawa bakin nonon seda kika kori hankalin ta daga kai ko ba haka ba?” Shiru Mama tayi duk kunya yabi ya kamata, “ko ba haka ba?” Ya sake tambayar ta. A hankali ta gyad’a kai.
“Kin kyauta sosai bani ‘yata” ya miqa hannu ya amshe Zeezee.
“Alhj nafa baka hak’uri we are humans we all make mistakes wallahi da zata kama maman yanzu na yarda zan cigaba da shayar da ita se lokacin da ka yarda a yayeta, kayi hak’uri kaji?”
“Yaushe kika yayetan?” Chan k’asa k’asa tace, “washe garin tafiyar ka.”
“Hmm! kin kyauta Hafsah.” Hak’uri Mama tata bashi da k’yar ta samu ta shawo kansa ya hak’ura. Bayan Sallan Maghrib duk ya tara yaran a parlour ya ciro wa kowa tsarabansa Ibraheem da Omar English wears qualitative jeans da T-shirts set biyar-biyar, Mariam laces uku masu tsadan gaske da atamfofi super biyu, se Yasmeen laces biyu da ‘yar kanti masu kyau guda uku. Mama kuma laces biyar da atamfofi super biyu, se Yasmeen laces biyu da ‘yar kanti masu kyau guda uku. Mama kuma laces biyar da atamfofi super biyu sena uwa uba Zeezee wanda suke nan fiye a k’irga.
★★★
Life couldn’t be better for Zeezee! Wato duk wani abinda take so shi ake mata a gidan sede in Baba bai gida, yarinya tana girma tana dad’a kyau da kuma dad’a kama da mahaifiyarta. Cikin rumfa da rayen Allah Zeezee ta kai har shekaru biyu da watanni goma a duniya (2 years 10 months) baki ya nuna ras se aukin surutu da kuma rashin ji da b’arna. Sede duk laifin da tayi komin girman sa Baba bai bari ko tsawa ayi mata bale wai amata duka koda wasa ba wanda ya tab’a d’aga hannu ya daki Zeezee harta Mama da kanta.
*~ *~
Yau ranar ta kasance Sunday as usual tin k’arfe 7:00AM Zeezee ta tashi ta d’ago babban teddy bear nata sannan ta sauk’o daga kan gadonta fuskan Mama da Baba ta leqa taga du bacci suke sannan a hankali ta fice daga d’akin ta sake ja musu k’ofar. D’akin su Mariam ta nufa ta bud’e ta tarar da su suma suna ta bacci kan gadon nasu ta d’ale ta fara tsalle-tsalle a kai, badan komi ba dan kawai ta tadasu. Cikin bacci Mariam ta soma magana tun bata bud’e ido ba tasan waye da d’anyen aiki haka.
“Zeezee dan Allah kiyi wa Allah kiyi hak’uri ki koma d’akin ku Baba na kiranki.”
“K’ayyan kine Baba na basshi.”
“Toh muma ki bar mu mana muyi baccin.”
“O’o ce kun tashi dan sha tea.”
“Fisabilillahi Zeezee sau nawa kike shan tea a rana? Kibari se anjima.”
“O’o ni yanzu nake sho” ta cigaba da tsalle kan gadon. A fusace Mariam ta miqe ta galla mata wani mugun harara aiko Zeezee dan munafirci tasa kuka sekace dukanta akayi. Yasmeen da k’aran kukan Zeezee ya tada ta tace, “Adda Mariam kin shiga uku me kika mata?”
“Kibar munafuka ko tab’ata banyi ba.”
“Zeezee dawo” cewar Yasmeen. Kafad’a Zeezeen dake bakin k’ofa tana k’okarin bud’ewa ta buga da nufin o’o. “Wayyayi chena fad’a ki da Baba.”
“A’a Zeezee ta yi hak’uri kar kije zo abinki kinji?” Cewar Yasmeen trying to sooth her.
“Ki barta tajen in ta fasa ai in taga ana tsoron takai k’aran mutum ne take jin dad’i yake kuma sake bata garab’asan cigaba da yin hakan, kije ba wanda ya rik’e miki k’afa.” Mariam na kaiwa nan ta juya masu baya tare da rufe fuskarta da bargo ta cigaba da kwanciya. Zeezee na barin d’akin tasa sabon kuka ahaka har ta isa d’akinsu Mama ta hau jijjiqa Baba. Jin kukanta take ya tashi ya zauna, “ya haka Zeezee keda waye?” Ya azata kan cinyansa. Cike da shakwab’a kan yadda ta saba tace, “Adda Mayyam.”
“Ai kaman na sani muje mu sameta.”
**
Banging k’ofar d’akin su Mariam yayi firgit suka miqe zaune dukansu. “Me kika mata?” yayi tambayar wa Mariam yana me hararta.
“Nifa ba abinda na mata tazo muna bacci tana mana tsalle-tsalle kan gado shine nace ta bari take wannan kukan.”
“Laaa! Baba wayyayi kayyan tane, mari na tayi a zuciya na.”
“A zuciyanki Zeezee? Ni?!” Mariam ta nuna kanta. “Yaushe ma naga zuciyan naki bale in mara?”
“Eh a zuciya na.” Zeezee ta kuma jaddada mata.
“Sannu ko k’anwata” Baba ya shafa kan Zeezee “yi hak’uri” sannan ya dawo da kallonsa kan Mariam “Allah Mariam ki kiyaye ni in sake jin kin tab’a yarinyan nan kiga! Ke shikenan kullum kina cikin bin gindin yarinya kina sata kuka sekace ba babba ba, this should be the last time I’ll warn you again.”
“Allah sark-”
“Rufa min baki!” yayi saurin katse ta.
“Shikenan Zeezee?” Kai ta gyad’a a shagwab’ance sannan tace, “zan sha tea.”
“Tea? Ko a dafa miki Indomie kina jin yunwa ne?” Ya matse cikinta yana mata cakul-kuli, nan ta hau dariya.
“Eh” ta basa amsa.
“Oya Mariam miqe ki je ki dafa mata Indomie da k’wanta