Author : MIEMIEBEE Category : Romantic Hausa Novels
sauri ta mik’e tana jan Allah ya isa har ta fice.
*****
Da daddare bayan su Baba sun dawo daga sallan Isha ya kirawo Zeezee d’akinsa, “K’anwata bana kema zanyi maki yanka kinji?”
“Dagaske Baba?” Ta fad’a sounding thrilled.
“Sosai ma K’anwata” rungumosa tayi tana meh jin dad’i ana cikin haka Mama ta fad’o d’akin “ya haka meke faruwa?”
“Baba yace zemin yanka wannan Sallan.”
“Yanka? Alhj yanka zakayi mata?”
“Eh in shaa Allah tunda Allah ya hore min.”
“Sauran kuma fah? Ai kamata yayi ka musu duka ka had’asu kan dabba d’aya.”
“Nifa kinga irin halinki da banso kenan, taya za’a had’asu duka? Allah kaimu next year suma se ayi musu amman bana kam K’anwata kad’ai za’ayi wa yanka.”
“Hmmm Allah ya shirya ka toh partiality a filin Allah haka, kullum ina ma wa’azi amman bakka ji.”
“Kanki akeji jeki huta K’anwata gobe kuna da school.”
“Toh Baba seda safe.” The next day Zeezee ta cika wa kowa kunne a gidan da waqan za’ayi mata yanka za’ayi mata yanka. Yayyun nata tun abin na damunsu ma har sun saba yanzu, hak’uri sukayi suka cire damuwan daga ransu in ba haka ba har ciwon zuciya yana iya kamasu.***
~* ~* RANAR SALLAH ~* ~*
Bayan sun dawo daga Idi Baba ya biya ya siyo raguna manya-manya guda uku, ba tare da b’ata lokaci ba yayi layyansa rago d’aya nasa, d’aya na Mama d’aya na Zeezee. Nan da nan suka shiga aikin nama banda Zeezee dake mak’ale a d’aki tana kallo a laptop nata.
“Shikenan Mama ita Zeezee ba aikin da zatayi tana zaune a d’aki sekace wata sarauniya.” Yasmeen tayi maganar.
“Toh ya muka iya Yasmeen? Dama ace Babanku bai gida ne toh amman yanzu da ance Zeezee ta d’aga koda tsinke ne se ya hau kan mutum da bala’i ki barta kawai.”
“Ai wallahi idan ku kun hak’ura ni bazan barta ba Zeezee! Zeezee! fito nan dan k’aniyanki” cewar Mariam. Jin shiru ta nufa d’akin tan da kanta, miqe kan gado ta sameta, “fito muje muyi aiki.”
“Wai aikin meh?”
“Aikin uwaki ‘yar banza kawai fito! Kin maida mutane boyi-boyin ki fito nace!”
“Ni ban iya ba wallahi kika tak’ura min zan had’aki da Baba.” Seda Mariam tayi dagaske ta samu ta fito da Zeezee daga d’akin. Kujera ta nema ta bata ta zauna suka hau gyaran kayan ciki banda toshe hanci ba abinda Zeezee ke chan kashi ya tab’a mata jiki zumbur ta mik’e “ni wallahi na fasa yin aikin k’azantar nan ku bani wani aikin daban.”
“Akwai wanke-wanke sekije ki kama.” Yasmeen tayi informing nata.
“Ni bazan yi wanke-wanke ba sede wani aikin.”
“Maza wuce kije ki kama wanke-wanken kona gaggaura miki mari maras kunya kawai,karki ga dan ina barin ki wallahi kika b’ata min zan illata ki wuce nace!” Mama ta bud’e mata “ba zaki wucen bane?”
“Ba naji ba wai kam” baki ta murgud’a sannan ta k’arasa wajen da aka tara wanke-wanken ta hau yi for the first time, se kwab’awa take tanayi kuda suna mata yawo ajiki abinda tafi tsana kenan! “Ha’aah nikam kudena tab’ani mana” tayi maganan da kudajen wai. Dariya Yasmeen ta hau mata “daidanki kenan su cinyeki ma mu huta” ganin kudan basu bar bi mata jiki ba ta je ciki ta d’au insecticide ta feffeshe wajen wanke-wanken se anan tasamu tagama jagwal-gwala wanke-wanken tayi ciki bata sake fitowa ba seda taji an soma gashi “ni ina rago na? Duk wanda ya cimin nama ban yafe ba wallahi.”
“Gashi chan achan ba wanda ya tab’a miki namanki keda kanki zaki soya” Mariam ta fad’a tana hararta.
“Ke wannan Adda Mariam kin kusan tafiya ma amman bazaki d’an canza hali aji dad’inki kafin ki tafi gidan miji ba, kuma kar kowa ya tab’a min ragona.”
“Saidai in baza ayi sadaqa ba, in ba haka ba cinyan gaba da na baya duk sena yi sadaqa dasu” cewar Mama.
“Wallahi kikayi sena gaya wa Baba ai dabba na ne, kiyi da naki mana.”
“Please Mama karki sake ce mata komi in aka zo yin sadaqan seta hana muga, banza kawai” cewar Omar yana cigaba da latsa wayarsa. Harara da murgud’a baki ta mai sannan ta koma d’akinta.
2 weeks after Sallah akayi bikin Mariam, biki yayi kyau masha Allah sede ace Allah shi bada zaman lafiya. Chan Kano aka kaita.
★★★★★
_10 months later..._
Alokacin Zeezee na Jss2 tana neman shiga na 3 saboda sun ma gama exams na 3rd term nasu sakamako yayi kyau sosai. Zeezee fa ba sauk’i an zama ‘yan mata yanzu se palli da rawan kai, hali zanen dutse har yau bata fasa rashin kunyarta ba, infact sede abinda ya k’aru ma. A month back Mariam da mijinta suka dawo Bauchi da zama kasancewar an mai transfer a gun aiki, sosai Mariam tayi nauyi haihuwa nan da watan gobe in Allah ya yarda, tunda Zeezee ta gano haka ta d’aga k’afa daga gidan Mariam saboda sata aikin da take.
Yau Monday Mariam ta kira Mama kan atura mata Zeezee tad’an tayata aiki zatayi bak’i, Zeezee najin haka tayi faking rashin lafiya ita sam bazata jeba seda Mama tayi dagaske sannan ta shirya akwatinta kaya biyu kacal tasa ciki dan batason ta jima, Ibraheem ne yayi dropping nata chan Fadaman mada inda gidan Mariam yake. Bayan isan Zeezee ta wuce guest room ta dire jakanta sannan ta fito ta tarar da Mariam zaune a parlour tana shan farin k’asa.
“Ina wuni? Ya k’arfin jikin?” ta gaishe ta sama sama.
“Alhamdulillah rice and stew zamuyi min Zeezee.”
“Rice and meneh? Kinfa san inba farin shinkafa ba, ba abinda na iya in zaki saki jiki ki tashi kije kiyi stew naki toh in kuma ba haka ba se bak’in naki suci garau-garau (shinkafa da mai da had’i) wai ace Uncle Mahmoud (mijin Mariam) kullum baida aiki se kawo mutane gidansa chin abinci wallahi mijina be isa yamin wannan d’anyen aikin ba.”
“Toh uwar fitsara seki bari idan Uncle Mahmoud d’in yazo ki fad’a masa.”
“Ni meya kaini? Ke matarsa bakiyi complaining ba seni, ni dama kun cigaba da zaman ku a Kano wallahi.”
“Jeki kwashe tomatoes da sauran kayan miyan dake fridge d’in ki gyara ina zuwa in d’iba miki albasa.”
“Wai Adda Mariam ni zanyi komi ke kawai zaki zauna nan kina ture-ture?”
“Inda da lafiya na ajinki ma zan ce kizo ki tayani ne?”
“Nikam gaskia bazan yanka albasa ba kema kinsan inada ciwon ido.”
“Se akace masu ciwon ido basu yankan albasa?” Haka suka ta drama har aka had’a kan stew d’in Zeezee ta dafa shinkafa.
*** ★ ***
Kwana biyu Zeezee tayi ma Mariam taji duk rayuwan bayi mata dad’i, ita ke mata wanke-wanke wai harda shara ma. “Ni wallahi yau zan tafi ban iyawa sekace ni nace kiyi cikin.”
“Meh kika ce?” Mariam tayi snarling at her.
“Ni nayi magana neh?” Ta murgud’a mata baki. “Wallahi yau zan tafi, don ni ba jaka bace.”
“Kanki akeji nide ki gama min shara da wanke-wanken kiyi duk abinda kika so yi.” Haka bayan tagama aikin da cuwa-cuwa kamar yadda ta saba ta shirya tsaf ta d’au wanka cikin purple lace, trolley’nta ta ja zuwa parlour inda Mariamke miqe a k’asa “zaki tafin ne?”
“Eh” tayi maganan tana plugging earpiece nata.
“Toh ki gaida su Mama” daga nan ta rufe idonta danyin bacci. Few minutes later ta bud’e idanun nata taga Zeezee tsaye inda take bata ko motsa ba. “Ya haka? Kin fasa tafiyan ne?”
“Shamawai! Da zanzo inta miki bauta da mijinki ne bazaki sallamen ba! Lallai kuwa!”
“Aww jira kike in sallameki?” Mariam tayi maganan a bit suprised tana dariya da k’yar.
“Eh mana bake kad’ai ba har da Uncle Mahmoud ma.”
Cike da mamaki Mariam ta tafe hannu sannan tace, “Ahh lallai Zeezee, kin rik’a toh nikam Allah yaga banida kud’in da zan baki seki tafi, Allah kaimu wani lokacin.”
“Wallahi k’arya ne ni ki sallameni.” Zeezee tayi maganan stubbornly.
“In d’ari biyun mota ne bazan rasa ba.”
“Chab! Wallahi Adda Mariam ba wasa nake ba ki sallamen.”
“Kisani na dole, ke wato baki aiki tsakani da Allah bama wannan ba jinki ban sane da sharan cuwa-cuwan da kike min neh? Duk dottin k’ark’ashin gado da kujera kike tura su koba haka ba?”
“Wancan kuma damuwanki ai in kikayi bak’i ba leqa k’ark’ashin gadon ko kujeran suke ba, nide ki sallameni in tafi.”
“Lallai kuwa you are not ready to leave inhar ni kike jira na sallameki, zama nan ya kamaki” Mariam na kaiwa nan ta juya mata baya da k’yar. Tsaye Zeezee tayi wajen if only tasan ina Mariam ke b’oye kud’inta, tana cikin wannan tunani ta jiyo k’aran motan Uncle Mahmoud robe dake cikin handbag nata tayi sauri ta ciro ta shafa k’ark’ashin idonta take ta soma hawaye dai-dai nan Uncle Mahmoud ke shigowa anan Zeezee ta soma magana cikin kuka, “wallahi baki isa ba sekin biyani 5k na, ai ba haka mukayi da ke ba wallahi kibani kud’i na” ta rushe da kuka. Mariam batasan alokacin da ta mik’e zaune ba tana kallon wonders kafin tayi magana Uncle Mahmoud yayi sallama, “wa’alaikumus-salam” ita da Zeezee suka amsa in unison “sannu da zuwa Uncle” tace tana share hawayenta kaman dagaske.
“Yauwa sannu Zeezee ta, Hajiya Mariamu sannu da jiki.” Da ya lura da Zeezee seya kamar kuka take, “ya da kuka kuma? Wani abu ne?” A rayuwa Uncle Mahmoud nason Zeezee badan komi ba sede dan k’iriniyarta musamman inya tuna days back da inyaje zance gun Mariam itama tafito tace se anyi zancen da ita.
*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com
PAGE 15
*December, 2016*
“Babu komai Uncle ni na tafi” taja jakarta kaman dagaske.
“Kaman ya ba komai? Gashi ina gani kina kuka kice babu, Hajiya Mariamu na me kikayi wa K’anwar tamu take kuka?”
“Wallahi Dear ban mata komi ba ni kaina bansan meke damunta ba.”
“Ai dama haka zakice kin kama kin cinye min 5k kikace nazo tafiya zaki bani, baki ban ba dole kice ai baki san meke damu na ba ni zan tafi.”
“Ni?!” Mariam ta dafe k’irji “yaushe na tab’a cin bashi gunki Zeezee?”
“Wait... Wait Zeezee na, Adda Mariam ce ta ranta kud’i gunki bata biya kiba?”
“Eh Uncle” ta fad’a tana gyad’a kai.
“Wallahi Dear karka jita sharri take neman min.”
“Tsaya mana Habibti muji daga bakin K’anwar tamu.”
“Wallahi karka jita sharri take neman min.”
“Wallahi ba k’arya bane Uncle Mahmoud if only Yasmeen was here data gaskata hakan, a idonta Adda Mariam ta ranta kud’in.”
“Chab! Lallai Zeezee bakijin tsoron Allah.”
“Ai nasan baki k’arya Zeezee, nawa ne kud’in nakin?” Dad’i taji sosai tasa hannu ta share hawayen ta “5K ne.”
“Dear Allah karka bata.”
“Ba ruwanki Hajiya Mariamu tsakani na da K’anwata” wallet nasa ya ciro ya irga 10k “gashi wannan duka naki ne” bayan ta amsa ta irga tsalle ta hau yi “duka nawa Uncle?”
“Eh mana, stew na ranan yayi dad’i wannan tukuici ne.”
“Fa ba ita tayi stew d’in ba.” cewar Mariam.
“Wallahi nice ai Uncle ma yasani” pillow Mariam ta wurga mata “mak’aryaciya kawai” gwallo Zeezee ta mata ganin Uncle Mahmoud bai ganinta “toh Uncle ni zan tafi nagode Allah ya k’ara bud’i.”
“Ameen K’anwata bazaki jira in having lunch nayi dropping naki ba?”
“A’a Uncle karka damu zan tafi da kaina”
“Toh ki gaishe da Mama and everyone” bayan ba-bye taja jakarta ta tafi.
Isanta gida keda wuya ta wuce d’aki direct ta ajiye jakanta sannan ta fito tayi d’akin Mama “ya har kin dawo neh?” Mama dake zaune bakin gado tayi maganar.
“Eh tace tana gaisheki haka Uncle ma kuma yabani 10k.”
“Toh masha Allah zan kira sa na masa godiya ina kud’in yake?”
“Me zakiyi dashi? Bade karb’ewa zakiyi ba!”
“Yo dama ‘yar yarinya dake sena barki da 10k?”
“Ni wallahi shiyasa banson fad’amiki ammin kyauta ni wallahi kibarmin kud’ina.”
“Haka kika ce?”
“Eh” ta amsa tana gyad’a kai “kinyi dai-dai, Allah kawo ranan da zakice na baki kud’i kiga in ban gaggaura miki mari ba.”
“Allah bare kawo ranan bama ni zan fita gidan su Miss Rama sena dawo” bata jira jin meh Mama zata ce ba ta fice.
*****
Cikin sati biyu Zeezee ta gama kashe 10k d’in cikin k’ananun siyayyan da basuda amfani, ayau Monday suka koma school su Zeezee ‘yan matan Jss3. K’arfe 7:10AM ta gama shirinta Ibraheem yayi dropping nata kasancewar Baba yayi tafiya, yana dropping nata ya wuce office shima. Kasancewar yau ne first day at school basuyi wani abin arziki ba se hira suka ta sha ita da Lubiee and others 2:30PM Ibraheem yazo d’aukan Zeezee ko kad’an bata lura da motansa ba as she was busy gisting with her friends, ransa ne ya mugun b’aci ya fito daga motar a fusace ya nufi inda suke tsayen da hijabinta ya jata. Ashar ta hau d’urawa ba tare da tasan waya mata hakan ba, tana juyawa tayi 4 eyes da angry Ibraheem. “Ya yaushe kazo?”
“Wa kike zaga?” Ya danna mata rank’washi a presence na friends nata “Allah ya isa ni nasan kazo ne kuma seka kama ka jani da hijabi ka sakeni”
“Kinada bakin magana ko?” Kunnenta ya kama ta hijabin ya murd’a da k’arfi batasan lokacinda ta soma kuka ba amman hakan besa tayi shiru ba se Allah ya isa take ja mai a haka har yajata mota ya bud’e ya turata ciki se ihu take tana kuka a motan ganin ya faka gefe guda tayi kum da bakinta gudun karya karyi reshe ya mata kalan na kwanaki.
“Nayi shiru wallahi nayi dan Allah kayi hak’uri.”
“Marasa kunya kawai bari mu isa gida” yaja mota. Bayan isansu gida ta shiga bayi a guje ta danna lock tana ji yana kiranta tak’i bud’ewa seda ta tabbata ya fita masallaci ta fito ta nufa d’akinsu, wayarsa ta d’au ta shiga whatsapp ta tayi sending had’ad’d’en break up message cike da zagi da cin fuska wa Fateemah girlfriend na Ibraheem ta wuce d’akinta tasa lock tana me praising kanta.
Koda Fateemah taga message d’in dariya sosai taci dan kuwa she’ve trust in her Ibraheem tasan sarai aikin Zeezee ne. Batasan me ta mata ba Zeezee ta tsaneta, Ibraheem na dawowa ya shiga whatsapp yaga d’anyen aikin da Zeezee ta mai ita dan sokanci ma bata goge chat d’in ba. Murmushin mugunta ya saki ta one side of his face sannan ya kira Fateemah tana d’agawa ta k’yalk’yale da dariya “aikin Zeezee koh?”
“Barni da ita Babe.”
“No Baby please karka tab’a ta kabarta.”
“Kamar ya na barta! Baki karanta message d’in bane?”
“I did but please let her be for me dan Allah.” Seda ya nisanta yace, “naji I won’t beat her amman she’ll have to serve some punishment.”
“Eh better amman karka tab’a ta please” hira kad’an suka tab’a sukayi sallama d’akin Zeezee ya nufa direct daman gashi Baba bai gida bale ya d’aure mata gindi kamar yadda ya saba.
“Zeezee!” Bata san lokacin da ta saki fitsari a panties nata ba jin kakkausar muryarsa, shiru tayi bata amsa ba.
“Zainab!” Ya kira sunanta more tensed this time around “wallahi before the count of three ki bud’e k’ofan nan ko na b’ab’b’alki wallahi.” Safa da marwa take a d’akin ta rasa nayi chan tace, “Ya ina toilet nefa.”
“I don’t care ki bud’e k’ofan nan nace kar kiyi pushing d’ina kisa na miki duka.”
“Bazaka dake niba idan na bud’e maka?”
“Nace ki bud’e!”
“Ya dan Allah kayi hak’uri” a hankali ta nufi k’ofan ta bud’e take tayi kneeling “dan Allah kayi hak’uri” ko saurarenta beyi ba ya fincikota da hannu se side nasu yayi wurgi da ita a d’akin. Gabad’aya Zeezee ta gama tsurewa se faman hak’uri take basa “rufa min baki!” Ya daka mata tsawa “ce miki akayi dukan ki zanyi? Kuma koda dukankin ma zanyi, you think wannan hak’urin kin could stop me?” Dan sanyi taji a ranta, wajen laundry basket ya nufa ya fara fiddo da laundry’nsa duk anan kallonsa take bata ce komi ba bayan daya gama ya wurga mata sabulu da omo “oya pack them kije ki wanke min su tatas, isolate the white coloured ones from the rest and believe me in har be wanku me kyau ba zaki sake and don’t think wai da washing machine zaki wanke, uh-uh” yayi shaking kanshi “da bare hands naki now off you go.”
“Chabd’i! Nice zan maka wanki kuma wai da hannu? Allah yaga ko panties d’ina ban tab’a wankewa ba seda machine, ko nama da washing machine kokuwa kayan naka su zauna da dotti.” Belt nasa ya zare “meh kikace?” Nan ta maraice fuska, “Ya dan Allah kayi min rai kayi hak’uri wallahi ban iya ba zan maka da washing machine.”
“Nace banaso tattara ki bani waje! Now!” Tana b’ari ta tattara kayakin tayi waje da su waje ta nema ta zauna tana sharb’an kukanta tsakani da Allah tana sumbatu tana kiran sunan Baba, ko uffan Mama bata ce mata ba da ta ganta, bayan data gama shan kukan ta tsoma kayakin cikin bucket tana tunanin ya zata fara wankin. Ganin Ibraheem tayi ya fito da belt a hannunsa take