Chapter 2 Reading NUR FIRDAUS BOOK 2 HAUSA NOVELS COMPLETE BY SURAYYAHMS.txt Arewa Novels

NUR FIRDAUS BOOK 2 HAUSA NOVELS COMPLETE BY SURAYYAHMS.txt

Author :  SURAYYAHMS Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   2 / 112

3K to 6K   out of 335.4K words

duk dai wai karsu barta ta zauna cikin kunci.

Dake bawai sabawa tayi ba tuni hartaji ta gaji da qamshin dan
ita kanta hjy bilkin sede in bata wulga ba kointa na tashin wani irin daddaar qamshi.

bayan nan sukay wanka suka ci Abincin rana daga nan masu hutu suka huta nan kowa yafara harkan gabansa, yau Kwata kwata Nur bata wani samu daman yin tunanin kowa ba bare ma ta tuna gida.

amma tana sane da cewa wann satin gabaki daya hidimar bikin layla akeyi da adnan acan Abuja koma ya ake ciki oho

da dare taga wai har cinema club sukeyi acikin dayan falon su, da ita da razia suka kalli film din cruella da wani maleficient nd yet they discuss soo much women power among themselves.

daga haka razia tafara mata recomending wasu fun and original educative movies inda zata na ganin mata masu aji a aikace kai films sun kai goma wanda ta bata wai tana kalla, Wanda tasan it wll defintlly help her mind develop a powerful thought game da rayuwarta na ya mace but nur wasnt really stable for that yet.


Abuja..


Daga Abuja kuwa shagalin biki akeyi wanda kusan ince kowa saida yajishi agarin Abuja, sedai sau dayawa Adnan
yana basu ciwon kai wanda yasha jawo gulmace gulmace yadda wasu tuni suka gane cewa Adnan baiyason auren aransa ko kadan.

dan wasu event din baije ba, sai an shirya sa sai yaje yasha cocaine ya kulle kansa a daki ya dinga bacci har agama hidima sede abige da bada uzurin cewa baida lafya ko ciwon kai.

hakanan akayi su hidiman kamu da liyafa da familynsa suke shiryawa ma musmn dan tarban ango da amarya Adnan duk beije ba.

habaice habaice da raina arziki da rainin wayo da aka dinga jefawa mrs haseena bana kadan ba...

yau nur take cika kwana uku a kaduna kuma yaundine ranar dinner su laylan washe gari bayan budan kai zaa kai amarya gidan mijinta da dare.

Duk walakancin da ake musu a sakaye Layla bata gani tsabar ta saka ranta akan kwadayin abun, wasu mutanen ma a idon mrs haseena suke kushe kankantar shekarun layla amma inaaa ko ajikinsu, wasu har cewa suke kwadayin abun duniya yasaka haseena siyar da mutuncin kwailar yarta wa hajy mairam kanem shehuri.

Maganganun banza da gori dai babu wanda hasina bata sha ba akan auren nan, wani abun ma saida aka tursasa adnan yazo shi wajen dinner, taga yadda familynsa suke yin komi dominsa ita kuma layla saita zama kamar yar kallo dan ko manni zasuyi basu wani fiye bita kanta ba

Tunda aka fara hidimar ko sau daya ango baiyi wani abu romantic ko da kuwa murmushi ba shiyasa ma ba ayi wani fun moment a awajen dinner ba har aka karkare. Babu lefi layla tabaza kyau kam dan kyau amma its all black out in her heart, adnan kept embrasing her awajen dinner dan duk abunda akace ango da amarya suyi tare haka yake kin motsawa, gashi babu kawa, dangi ko jini ko daya nata bare wani abin ya ragu musu.

washe gari ana shirin budan kai hirar dinner duk yacika dangi anata cewa wai auren dole akama adnan tun layla tana iya daurewa harta dawo tana boye kanta a bayin gida tay ta kuka sosai...

ahakan kuma wai tana tunawa da nur firdaus dan gani take kamar duk inda matsala ya sameta nur zatazo kuma ai bata taba barinta acikin matsala ba sai a wann karon

a daddafe dai akayi hidiman karshen har aka karkare budan kai
wanda shima Adnan beizo wajen ba sai can da yamma yarufa duk aka gaji da jira kuma yana zuwa ma bejima ba akayi manni da sauransu suka kama gabansu shida abokansa.

hankalin mrs Haseena bakaramin tashi yay ba dataji yadda sunan layla ya karade dangi da gulma kawai a fito fili ace musu auren cushe ne kawai ba a fada ba amma Adnan makes everything difficult and obvious

wanda basu san baison auren bama saida yayi yadda suka fahimce lamarin tun daga yanayin yadda yake banzatar da komi na auren kamar ba aurensa ba


Koda akazo kai layla dakin mijinta haka Mrs hasina ta dinga lallabata tace mata ta toshe kunnuwanta komi zaizo ya wuce
Kwanan nan inta haihu da shi bakin yan gulma duk zai rufu

da haka ta lallabata laylan suka rabu suna hawaye aka kai layla wani irin hadadden sabon gida da aka gina ma adnan a maitama wanda still iyayensa ne suka saka komi aciki dan hjy mairam ta gayawa mrs hasina cewa bata da arxikin da zata yi ma yarta irin garar da sukeso so agidan dansu dam haka zasuyi abunsu aidama auren na alfarma ne bana soyayya ba.

ahaka dai aka rabu Babu dadi cikin zucyar Mrs haseena dan ranar da aka kai layla dakin miji ko runtswa bata iyay ba tsaban tunanin irin ukubar dangin miji da yarta zata shiga gata bata da wani wayo kai shekaruntan har nawa ne abunda duk yazo kuma yanata damunta


daga gidan amarya layla kuwa tunda aka kaita dakinta kowa ya watse akabarta ita daya tun tana zaune a tsakiyar gado tana jiran ango yazo ya bude mata kai suci kazar amarci har ta gaji da xama dataga karfe biyun dare ya wuce baizo ba ta hakura tayaye makanta mayafin tay wanka tanemi tea tasha ta kwanta ita

kasa baccin tayi sai inta tuna nur firdaus sai kuma taji kamar bata kyauta mata ba.

hakanan rayuwarta ya fara agidan da tunanin any time soon zataga shigowar Adnan amma sai shiru, koda tazaga gidan sai taga ashe ma sashensa agidan anyisa ne daban dakayan alatun da sukaci uban wanda yake sashenta sai kuma damuwa yabi ya cikata cos all she can rmbr awajen auren nasu is how adnan keep reminding her cewa he is going to be her walking night mare...NA KUDINE
PLEASE DONT SHARE IT


08060712446


[23/04, 23:03] Anne-Aurora🦋: NF2surayyahms:

Bayan kwana biyu da hidimar biki layla itakadai tacigaba da zamanta agidan tana mai dada lumar da zucyarta acikin tsananin tsoro da damuwa gashi bbu me nemanta koda a waya face mummynta kullum kuma acikin kaimata kuka take akan tunda aka kawota gidan adnan harynxu bai shigo gidan ba mrs haseena kullum tana kan aikin rarrashinta akan ai dama zaman aure haquri akeyi.

A sati na farko da kammala biki burin Mrs haseena ya cika sakamakon damka mata takardun gida da hajya mairam tay

she is now the sole owner of her own mansion na gwarimpa iyakan ne kawai ya faranta mata ranta amma banda batun auren yarta layla gashi bata isa ta kai korafi gaban hjy akan adnan ba dan mutane ne da basuson agaya musu aibun yayansu kokadan ynnxun nan saisu hau fushi da gorance gorance

domin kujewa gori da baqar magana yasaka kawai mrs haseena tay shiru saidai kawai ta rarrashe yartan..

yadda adnan ya jefa layla a matsanancin damuwar rashin ganinsa a gidan tun ranar da aka kawota yasaka Mrs haseena tunanin inama ace da nur firdaus tana nan da zata umarceta ta kirasa ta dan lallaba musu shi yadawo gida wajen matarsa dan tasani sarai adnan zaiji maganan nur firdaus fiye da na kowa.


tanason tay hakan amma kuma ego ya hanata saukar dakai ta nemi lambarta gani take kamar intay hakan girmanta ya fadi kasa warwas kawai gara ta nemi mafita ta wani waje.


a fannin Adnan din kuwa wani hotel suka kama shida abokansa suke zama aciki tun da ya san cewa nur ta bar rayuwarsu batama zaune cikin Abujan yanxu ya dada tabarbarewa. daren aurensa they do alot of drugs sabida he kept imagining ina ma ace nur zaije ya tarar a gidansa amatsayin matarsa na sunna.

wann tunanin kusan haukata brain dinsa ta dingayi wanda ya jawo masa dada zurfafa cikin shan kayan maye sosai...

gashi dad dinsa ko ya kirashi baya son daukawa bare mum dinsa da haryau yake dora mata laifin komi, tun suna daga jjiyar wuyarsu akan ya dawo gida har suka gaji suka kyalesa..

tunda aka kai masa layla akalla saida yay kusan sati be leko inda take ba, akwana na takwas din ne cikin tsakiyar dare ya dawo gidan yakwanta a can shashensa snn yafara tunanin akan rayuwarsa da alkwarun daya dauka ma nur firdaus cewa zai koma kan karatu da kuma aikinsa duk sanda ya tuna cewa ba nur bace agidansa matsayin matarsa sai yayita kuka shikadai


washe gari da safe koda suka hadu da laylah ta fito daga nata sashen kenan tahangosa zai fita.

jiki na bari tay sauri tataho wajensa tafara masa magana lkcin ransa a mugun harde dan beiko kalleta ba bare ya amsata ya saka kai ya fita

jikin window tay ta kama labula tana kallonsa hawaye na zuba aidonta tana kallo har ya shige cikin motarsa ya kara bar mata gidan ofishin mum dinsa ya wuce kai tsaye Domin fara shirin komawa bakin aiki da karatunsa wai koda wani abun zai masa sauki.


**********

Bayan kwana biyu.

Kamar kiftawar ido da bismillah Rayuwa ya fara sauyawa Nur firdaus acan gidan kawunta dan kuwa kulawa na musman ake bata ta kowani bangare, doc taher shima yana balain taimakwa wajen engaging dinta da deep converstion session irinasu na professionals ahankli ahankli yanayi yana jin ra'ayoyinta tana kuma fitar da abubuwa da yawa wanda suke toshe mata tunani da jin dadi.

ga wasu allurai da ake mata ajijiya suna da mugun zafi kam amma cikin kankanin lokaci tasomajin kamar kwaco kwaklta akeyi daga halin data shiga na tsananin damuwa abaya, sosai tasoma fahimtar kanta takuma soma jin sauki sauki sosai a zuciyarta sabida samin nitsaten bacci da kwanciyar hankli tare da kulawar Razia,

gabaki daya satin sai tajita daban with no one to scold or hurt her, snn babu kadaici ko lokacin yin tunani dan matan uncle dinta ma kadai basa barinta da kalar suruntunsu thy are alwys in her company,safe rana dare suna sakata dariya da magana dan dole kuma dama docton cewa yay abashi sati guda da ita zai iya bakin kkrinsa wajen rage mata tunani da yawan damuwa sauran kuma su dasu dora daga nan...

Dan haka hajy sa'a da hajya bilki suka hau shirya abubuwan da zasuna dorata akai anasu fannin na gargajiya irinde home training da suka ba razia kamr koyan girki
,qamshi, da sauran dabiu masu kyau na yan mata dan sunsan ba lallaine ace mrs Haseena ta zauna ta bata tarbiya ko koya musu yadda kalubalen dake cikin rayuwar ya mace yake ba.

Burin su baifi suga nur firdaus din ta dawo tamkar yar cikinsu agidan ba. They all belive she have a better future ahead of her, ko sau daya basu sake tuna mata da abunda ya faru da ita abaya ba, dan sosai kawunta yake so ya cika mata burinta nayin zurfin karatu dan haryau kokadan bai karaya da rayuwar Nur firdaus ba.

su hajya sun fara shirin hiring wanda zasu koyar mata kala kalan girki kenan sai kuma tafiyan business ya kamasu dan atare suke harkan shipping din kayan kitchen da kayan sawa agidan sun maidashi kamar family business.

Bayan tafiyarsu Daga ita sai razia da wasu mata masu aikin kulawa dasu agidan aka bari gidan sai ya zama shiru babu abun yi duk sai tarasa abunda yake mata dadi jim tunanin abubuwa sun fara dawo mata afresh


yau ya kasance Ranar jumua da yamma nur tana zaune quietly akan wani creame suede couch tana dan wasa da tsiraran yatsun hannunta with so much heavy hrt nd naivety ayanayin da zaka san ita kanta ayanxu bata wani daukar kanta da muhimmanci. kusan kullum inta kalle kanta a madubi sai tadinga ji kamar ba ita ba, dan deep within her mind gani take rayuwarta ya kare duk wani mijin da zai sota anan gaba dolene zaiji labarin cewa itace yarinyar nan da mijin mamanta yayi raping, snn tayi ciki kuma mamanta ta zubar mata dashi and she is not even in schl anymore, toh menene kuma yanxu yay saura na darajar ya mace atattareda ita? inta zauna tuna rayuwarta na baya saidai kawai kaga hawayenta na sauka, dan she is just tryng to force her mind amd body to be okay amma har cikin kokon ranta she is still feeling pains and ashame of being seen ako ina ma. kawaide gani take kmr bata da wani daraja ko kima da zaa kalleta dashi yanxu.

tana cikin wann tunanin idanuwanta suka kara cikowa da ruwan hawaye cikin sauke nannauyar ajiyan zuciya tadan lumshe ido wanda ko 3scnds batay ba taji muryan razia akanta abazata, kafin ta juyo very calmy razia tace "Nur, u're tensed ko?daf tana shirin bude lumsashun idanunta kenan sai taga wai har razian tadawo ta gabanta ta dan tsuguna gently suna masu kallon idanun juna, karamin mamaki ne a fuskarta dan harga Allah bata san yaushe razian ta dawo daga outin inta ba,

da har zatay magana raxia ta dan katseta da karamin murmushi tace its "okay to feel sad again and again ure still healing little sis. amma kinsan wani abu kuwa?

jiki a sanyaye nur ta girgza kai ahankli
...tace a'a, nan razia tahau share mata hawaye tace suck it up..yau nazo mana da baqi kintuna nace miki no dull moments? toh gabaki dayansu aminai na ne, so, they are all professionals duka zamu hadu muna catching fun har se su mama sun dawo. nd rmber what i told u basai kin kira wani acikinmu da anty ba, kawai kiy chill ki sake jikinki, and we are not here to judge you okay... kawai kisaka hanklinki akan abubuwan da zasuna koya miki, we all cool with u kinji?..

..murmushin dole kawai nur tay tace okay, ...razia tana murmushi tace are u ready to meet them..?

tunbata amsa ba crew din razia suka fara shigowa falon daya bayan daya, da wani irin fuskar fara'a molly tashigo dan itace agaba gaba hannunta abude tazo direct tay hugging nur tace Hi baby girl, are u ready to taste freedom?

tun kan nur ta gama karema molly kallo sai ga Rico ta shigo da wani irin lazy smirk tanamai kare ma nur din kallon kurilla while evrything scream luxury ajikinta tana zuwa hannunta ta mika ma nur tace "you and i will have a real talk..woman to woman..no lies. i am going to be your best friend..nur tay kamr zatay murmushi, tana daga kai taga wani hot statue ya shigo tamkar wani fashion director, frankie ne ya bayyana yasaka wani irin hadadden kaya theme of 1960s house of liberty fashion collection,nur ta kasa dena iya dauke ido akansa dan ta rasa gane ko shi mace ne kona miji ne, suna kuwa hade ido da nur sounding confused ya rike chest dinsa yace woahhh, But razzy, you dint tell me she is this originally beautiful..Hi Nur,

ahnkli nur tace masa Hi...adan nitse yazo ya zauna kusa da ita yanamai kare ma fuskarta kallo yana murmushi dan aransa haryaga ta inda kalar kwalliyar da zai na dacewa da ita zai fito" "she got excellent natural lashes,we wll just need a proper foundation match, and heels...God..yes
heels....razy i am so obsess, this girl is a beauty itself. yana cikin maganan muna ta katseshi da karar key din hadadden motarta datake wasa dashi a hannunta very gently takalle nur tace
"girl, i wll fly you around. in sha Allah u will rember what the winds feel like when ure not hiding.

NUR duk sai taji ta rude tarasa me xatace musu nan Razia tazo tarike hannunta calmy tace "hey sis karkiji tsoron komi kawai kibude zuciyarki no body will give u a tropy for suffering let go of it, wanda suka cutar dake fa suna can suna cigaba da rayuwarsu bayan kece kikafi cancanta da ki cigaba., uve survive alot, and now its time to live like youve survived it.

riqe numfashinta tay ahankli tana dada kallonsu, they werent just ppl, they were full energy. identity, ga purpose, data kalle kanta sai taga kamar she is just a trauma in a dress too loose for her own body.

tsorata taji tay muryanta na dan rawa rawa ta mike tsaye tadan tsaya agabansu tace "guys, its really nice meeting yhall,
ammma...i dont think...sai tadan lumshe ido ahnkli tace gosh i am not like you.
nifa babu abunda nasani. da sauri rico ta zo tarike hannunta suna kallon idanun juna tace you dont have to be like us or anyone nur..you just have to rember who you are, kuma munan zamu taimaka miki.

hawaye taji ya kara cika idonta tace "but i don even know who i am ryt now?hawayen ta yafara sauka dan tunanin dake toshe mata kai kenan kullum
duk dai gani take kamar ta canza rayuwarta ya riga ya lalace hala bazata taba dawowa kmr nur firdaus din data sani adacan baya ba.

Wani irin Rungumota taji molly tay ta baya gently tace"shhhushh "kituna fa kece yarinyar nan da kikay surviving thru so much trials and hell, wanda dukanmu anan ba lallai mu iya daukar irinsa ba, duk cikin mu babu wanda ya isa ya koya miki wani abu, kin ma fimu daraja da kima nur cos ure already a strong lady
pls u need to live..you have a full life ahead of you. let us be ur friend for a while.

nan hawaye suka kara sauka idanun nur batace komi ba dede nan frankie ya katsesu da tafi. "ah'a bazan bar kyakkawa kamar ki tana zubar da hawaye ba..guys lets stop talking and do sumting fun. ni kun san bana son harkan kuka da baqin ciki ina tattalin kyauna ahaaa
kunsan kuwa yawan kuka da baqin ciki yana saka mutum muni? dan dariya suka masa, nan danan kuwa suka warwashe, dan wani game sukayi playing tsakaninsu dats very intresting aka sassaka candles a tsakiyar falon kowa zai shigo circle din ya kira sunansa aciki sai yace"i forgive myself.
i am not what happen to me. sai kowa ya dan bada labarin kansa da battles din yay facing a rayuwa, hakanan har suka gama nur tajijji labarin su, wasu abun tausayi sede gani take kaf basu kai nata ciwo ba
amma koda suka nuna mata they all have scars sai taji ta kara sakewa da su sosai, they had fun tasha mamakin yadda suka iya abubuwa na Addini, har dana ciye ciye masu dadi duk da wayewa da uban haduwarsun nan.

itade bata taba ganin mutane irinsu ba they are just sooo fun and really living

2 / 112