Author : SURAYYAHMS Category : Romantic Hausa Novels
masallaci sallahn magrib haryanxu bai shigo gidan ba.
bangaren simran kuwa sai kusan 7pm jirgin daya daukota daga Abujan ya sauketa a garin lagos, 7:40 on the dots ta iso mufasa mansion da wani irin karfin gwiwa dan tsabar zumudi ma batama iya aje file din ajakarta ba a hannu ta rikeshi kamar trophy har ta iso gidan dashi
kai tsaye ta haura sama ta samu hajy zubaida a daki jikinnta na rawa rawa wanda ita kanta hajy zubbyn saida tay mamakin ganin simran a wann yanayin uban xumudin
data jima bata ganta aciki ba.
simran ko zama batay ba tana aje handbag dinta ta mikawa hajy zubby file din bakinta har na rawa tahau zuba mata bayani frm A-to Z akan bunda ya faru batare da ta boye mata komi ba.
hajy zuby dataji kanta na wainuwa sabida uban kudin kamfanin ubansu da simran tay wasa dasu sai batace komi ba harsaida ta kammala karanta file din tass tasss snn tadau wayarta ta kira one of her trusted private investigators ta gaya masa sunan file din nur din and within 7 good minutes yay hacking source na information ya tono mata komi tuntun na news din pregnancy news na nur da aka goggeshi a internet yay verifyn mata komi tareda kara mata wasu kanun labarai....
saida taji hakan daga trusted source kafin nan ta fashe da dariya ta rangada wani irin shewa jikinta harna bari bari ta dau file din tace ma simran basuci ta zama suje yanxun nan su fasa kwai dan dama irin wann ranar take jira
yau ko mayafi bata saka ba tafice tay hanyar dakin su anty suad ayayinda simran din kebinta abaya yau farin ciki a fuskokinsu kamar zasu tashi sama dashi dan murna.
saidai tun daga kofar sashen su anty suad din simran taga hajy xubby ta kame ta kuma bala'in shanye zumudinta, atake ta sako wani kalar fuskar makirci da jimami mai tsanani
sunayin sallama ta damke file din a hannunta tay lumi kamar ba komi tazo dashi ba.
koda sukayi gaisuwa anty suad din ko wani kulawar kirki bata musu ba lady sid ne tazo harta dan jawo simran din suka xauna tanamai tambayarta inda ta shiga kwana biyu.
mafi akasari shiru simran tay dan sam bata gane kan hajy zubaida ba dan a tunaninta daga sun shigo labari kawai zasu hau zuba musu
da rawar jiki sai kuma taga hajy xubbyn tay amfani da wann daman tawani siga na daban daya mugun bata mamaki kuma ya burgeta..
bada tashin hankli ba taje har gaban anty suad da file din ta rusuna kai kamr mutuniyar kirki duk jikinta yay sanyi.
cikin salo na makirci tafara zubda hawaye tanamai cewa anty suad ita taxo ne da wata magana me nauyi akan auren javeed sabida gaskya ita bazata iya boyewa ba dan ya shafi mutunci da datajar ahalin mufasa gabaki daya..
jin antabo zancen ahali yasaka nan take anty suad ta hatsala tanamai tuhumarta akan abunda ke tafe da ita.
hjy zubby tay shiru tana sim sim yadda tasaka duk suka xaku sunason jin maganar abakinta sosai
aikuwa kamr an taba brain din simran kawai saita fashe da makirtaccen kuka tana ambatar wai a rufa ma javeed asiri tana wasu irin makirtn maganganu tana kuka
babu yadda lady sid batay dan ta gaya mata meke faruwa ba amma taki sam tana ta kukan karya kusan karamar fargaba da hatsaniya suka kunna musu a dakin inda matayen suka xafafa tambaya agaresu..
nan kawai sai hjy xubby tafara cewa ita dai da bakinta bazai iya furtawa ba dan gaskiya batason abunda zaizo ya hadata da muguntar javeed tunda dama ba mutuncinta yake gani ba kuma ubansa yana goya mai baya an maidata bakomi ba.
anty suad datagaji da kwainanensu abazata cikin bacin rai ta fauce file din with no excuse ta mike tsaye tafara karantawa da karfi kowa najinta...
sirrikan nur ne take fayyacewa a fili dan yadda jikinta ke rawa yasaka duk suka mike tsaye lady sid ta dinga kwaroro salati tana jin kanta kamar a mafarki
..ahakan ma saida hajy zubaida ta dinga sakaya simran aciki tana mai nuna musu cewa ai simran dince taji labari sai tay bincike kuma sai taketa son taboye musu maganan dan a rufa ma javeed asiri sabida tsananin son datake ma javeed batason ace ita ta rabashi da nur firdaus dinsan tunda dai ita ya zabar ma ransa yace yana so.
tana matsa hawaye sai tace ita kuma duk dama ahalin mufasas basu dauketa uwa ga javeed ba amma gaskiya bazata iyayin shiru akan wnn maganar ba sabida wata rana in gaskya labarin nur ya fito ta kunnen makiya duk mutuncin ahalinsu ne zai zube gabaki daya.
anty suad da dama already tsanar nur din ya ginu aranta batama tsayayin wani bincike ba tasauko kasa ta fice a dakin tay hanyar falon alhaj attah babu ko takalmi akafarta fuuu kamar iska
duk matayen suka hau binta baya dan tsabar makirci simran har wani kuka take tana kama rigar anty suad din tana cewa wai a rufa ma auren javeed asiri ..
babban falon alhaj attah sukayi daidai ya shigo ciki kenan yana waya da javeed din yana daf da katsewa kenan kururuwar kukan simran ya fara katseshi wanda ko sallama baiy ma javeed dinba ya katse wayar ya juyo yana ta kallonsu yadda suka shigo masa gatsau kuma ahaukace babu sallama bare gaisuwa
ga tashin hankli da hayaniya da kuma uwa uba anty suad data gama kumbura tay famm fuskarta yay jaaaa sosai duk jikinta karkarawa yake da matsanancin baci rai..
tana zuwa a mugun zafafe ta jefa masa da file din nur din akan glass table din dake gabansa lkcin kansa na daure ko tabawa baiyi ba ya dubesu da dumbin mamaki yace kee suad lafya kuwa? daidai nan anty suad din ta sakar masa kuka mai tattare da zafin xuciya da diri
within spec of some minute ta zazzage masa labarin komi tareda tulin dumbin tsanar da takeyi ma auren javeed da nur firdaus tanamak kirar nur din da karuwa wacce tay cikin shege ta kwabar kuma babbar macuciya snn tace masa bazata taba yin shiru ba saidai ya kira javeed din suxo nan shida matarsan dan suji gaskiya abakinta dan bazata iya kallon wnn abun kunyar cikin ahalinsu ba.
kirjinsa yaji ya rike da wann labarin dan he find it very absurd ace wai nur ce da wnn mugun tarihin kai saidai in wani makirci su xubaida suka laka mata..
duk diri da zafin zuciya da kukan da anty suad takeyi anan baice mata komi ba dan yasan hanya mafi sauki na warware komi shine aji other side of the story abakin javeed a tunaninsa koma miyene game da nur dolene javeed zai sani tunda yasan dolensa zai zurfafa bincike akanta kafin ma ya tunkareta da maganan aure.
daga can javeed ya gama Re-trying lambar babansan bai dauka ba ganin lkcin da sukayi zasu hadu da nur dinsa awajwn dinner na wucewa yasaka kawai ya kama hanyarsa ya shiga gidan domin ya shirya kansa yaje private dinner din data hada musu ya sameta acan
..
bai wani saka komi aransa ba yahau shiri saidai wandonsa kawai yasaka yanakan shirin saka rigar saiga kirar babansa ya kara shigowa bai dauka ba saida ya kammala saka rigar yay tsaf jin kirar yay yawa saiya dauka sai yaji muryan babansan wani iri ga kuma koke koken anty suad dayake shakowa
tun anan yafara tambayar ko lafya amma baban nasa sai baice mai komi ba yace masa marmaza kawai yabar duk abunda yakeyi yanxu ya dauko nur firdaus sutaho gidan yanzu nan. javeed ya daga wayar a kunnensa da mamaki ganin wai har ya katse masa waya
agaggauce bai tsaya yin wani tunani ba ya dau agogonsa da jacket dinsa ya fito ya samu nur tay mugun kyau a red dress dinta tana zaune like an angel tanakan jiransa
kallo daya yay ma wajen yadda ta gyara shi yay masifar kyau duk sai yaji baiji dadin da zaiyi ruining mata wnn moment din nata ba
da murnanta ta mike data gansa yazo, sai kuma tagansa da dogon coat dinsa ahannu muryansa a tausashe ya taho yay kissing din goshinta yace mata tay kyau snn yace mata tay haquri zasuje gida ynxu amma ya mata alkwari komin dare zasu dawo suyi privte dinner dinsu zai kuma saurari abunda zata ce mai...
bata musunta masa ba tace mai okay ,ya karasa saka long coat dinsa akan casuals din dayasaka data mai kyau bana kadan ba, ya riko hannunta suka dawo dakin ta canza kaya sharply ta saka plain abaya blacl colour zuciyarsu duk ba asake ba suka shiga mota suka kama hanyar gidan agaggauce.
sai satar kallonsa nur take duk ta rasa meyene yake shirin faruwa ganin kamr shikansa hanklinsa baya jikinsa sosai
9pm on d dot suka iso cikin mufasa mansion lokcin har kura ya dan lafa sun zazzauna banda alhaj attah dake rike da file din yana tsaye yana dada latsa wayarsa yana verifying komi da secret scanner dake jikin xobben azurfa dake hannunsa.
what really borders him shine da baiga alaman fake news aciki ba..
kowa dai yay shiru banda anty suad dake karkada kafa tana wasu irin munanan maganganu akan nur firdaus tana cewa dama can tasan auren nan bazaije koina ba kawai anyi shi ne dan sabida ana daure ma javeed gindi ana fifita shi sama da uban kowa dan gani take kamar aidolene ma ace javeed yasan da wann maganar kawai boyewa yay dan ya raina musu hankali sabida baya darajasu kuma bai dauke al'adar ahalinsa da mutuncin gidansun abakin komi ba shiyasa har zaije ya auro wacce tagama watsewar ta akan titi tay cikin shege ya kawo musu gida a matsayin matarsa na aure.
ita babu ruwanta da details kawai abu biyun nan ta rike na cewa nur ta taba cikin shege ta kuma zubar shiyasa tabar gaban uwarta ta dawo zama a kaduna. iya nan kawai ta rike ta dinga zafafawa kai kace shine kawai labarin data gani bata ga cewa case na barayi da kuma rape bane.
nur bata tashi jin tsananin faduwar gaba ba har saida ta suka sauka a mota taga javeed ya wuce gaba cikin sauri like he is tensed gabanta na faduwa sosai tabiyosa abaya.
tafiya take gabanta na faduwa har suka yi sallama cikin falon wanda kafin tadaga ido taga duk su anty suad sun mike tsaye suna mata wani irin kyamataccen kallo
anty suad din tana wani huci kamar zatayo kan nur din ta kamata da duka lady sid tay marmaza ta rirriketa tanata cewa haba mummy calm down mummy dont attack her wallh wallh ba girmanki bane alhamdullh tunda zmsunzo aiyanxu gaskiyar zai fito
maganan yay ma nur wani iri jikinta sai ya fara rawa rawa kadan
rusunawa javeed yay ya gaida babansa daya amsashi dakyar
nan nur dinma ta gaishesa da sanyin murya sai kawai ya kalleta wani iri bai amsata ba..
acikin dauke kai tunma anty suad bata fara nara reaction din ba ya dago ma javeed maganar background na nur firdaus..
kai tsaye javeed ya gaya masa iyakan abunda ya sani akan halayyarta wanda tun bai idda ba anty suad tahau masa ihu tana cewa karyane.. karya ne...macucuiya ce..
watsatsiya wacce ta gama zubda kanta wa maza tay cikin shege ta xubar snn ta gudu agaban uwarta tana faking nitsatsiya..
duk dai javeed baiyi wani reacting ba duk da kukan dayaji nur ta fashe dashi sosai musmn da babansan ya fara tambayarta akan dalilinta na barin Abuja yana tuno mata batun case din cikin sam taki tace mishi ehh ko a'a kanta kawai ta sauke kasa tanata kuka maicike da radadi da kuma matsanancin tsoro..
ko dar dar javeed baiji aransa da shirun nur ba har saida babansa ya fara masa bayanin komi calmly tareda tabbatar masa cewa tabbas nur ta aikata abunda ake zarginta dashi, sabida he even scanned it,..kuma ya lura da cewa angoge information dintan ne a media news but all of it is on the dark web kuma duk sune
aciki file din nan..
anty suad kuma har iyanxu sai tambayar nur din take azafafe
ta gama hatsala wai saidai ta furta musu agaban kowa tace musu eh tay cikin shege ta zubar da bakinta..
nur kuma tay shiru ta rufe fuskrta da veil din abayarta tanata kuka sosai batace komi ba
javeed duk sai yaji ya rasa abunda zaice yay shiru dan wnn karon ne na farko dayaji brain dinsa ya kasa daukar magana a bugu daya ahnkli ya juya yana kallon nur dayaga yanayinta sai yaji komi nashi ya tsaya cak numfashin sa yazo masa har magworo yana neman shakesa dan atake idanunsa yay wani irin kadawa yay jaaa
ga ihu da anty suad take musu tana zage zage saidai nur ta bar gidan cikin daren nan saboda aganinta ai shirun da nur tay ma babban amsa ce
cikin lunshe ido da budewa javeed yay tsam yanajin how utterly shaky and dispointed babansa yake fidda wasu maganganun duk dama ahnkli yakeyin sa amma yasani in har yace zaiyi yunkurin defending din character din nur anan wajen yanxu haka bamai fahimtar sa gara yay shiru...
karasowa gaban babansa yay ahnkli yace masa yana so yabashi dama yay magana da nur din privately tunda dai matarsa ce koma miyene she wll be able to tell him amma ba agaban kowa ba...
yarje masa da baban yay ma bakaramin bori anty suad ta tayar ba saidai bai kulata ba
javeed ya juya batare da ya kalle nur ba ya fice a falon bata san ya akayi ta fara binshi cikin sauri tanata kuka ba dan kodaga yanayin tafyarsa tasan ba adaidai yake ba.
yana isa sashensa tun baikai ga kofa ya daka wata uban tsawa wa su mr aqeel cikin bacin rai inda arazane suka bar wajen ya zamo daga ita sai shi.
suna isa kofar dakin sa tun bai bude ba ya juyo ya kalleta jikinsa har na rawa rawa...
muryansa kasa kasa da tsananin tashin hankli da bacin rai ya kalleta yace "is it true?
tun kafin ta amsa yaji ya kasa daurewa cikin daka mata wani irin borataccen tsawar daya kusa sumar da ita tay baya kamar zata fadi ya fizgota yace answr the damn question is it true?wani abu me kama da haka yafaru dake nd i dint know?...
numfashinta kamar zai bar jikinta take kuka sabida ta tsorata
jikinta na rawa tabi ta runtse idon sabida kallon dayake mata sai batace mai komi ba ta gyada masa kai cikin kuka sosai, wani cak taji ya dauke baya motsi dan sai da yay kamar 3 minutes kafin nan taji ya saketa tun kafin tadago ta masa wani bayani yabude dakinsa da mugun sauri ya shiga ya barta anan atsaye bata hankara ba saijin karar buguwar kofar wanda saida ta kara razana ta kankame jikinta sosai tana kuka
ta tsaya cak awajen tanata buga kofar tana kiran sunan sa
amma bai kulata ba
dan yana shiga ya kwanta akan gadonsa ruf da ciki shikansa bai san lkcin da zazzfr hawaye ya fara sauka masa ba, how did he not even knw this??? koda shike shine nan ya hana kansa yin bincike akan yanayin rayuwarta na baya sosai dan aganinsa zai iya fahintar nur tunda ya aureta batare da sai ya zafafa wasu bincike past akan files dinta.
baisan yana mata wani irin muguwar so ba sai yanxu dayaji kusan kominsa na neman tsayawa cak sabida ita dan wani irin matsanancin zafin kishi yaji ya rufesa.
babu kalar rokon da batay masa akan ya saurareta ba amma sai shiru..
karshe kasa motsi tay tanemi waje ta zauna bakin kofar akasa tanata kuka har saida hawayen ta ya gaji dankansa ya dena zuba ga dan uban zazzabi dataji ya rufeta atake.
washe gari da asubah kawai tsintar kanta tay akan gadonta an saka mata drip she dont knw why and who tadai ga na'ima da janet suna tsaye akanta
[11/06, 16:28] BLUE💙: Arewabooks@surayyahms
tana gama bude ido ko tsayawa sanin awani duniya take batay ba takama igiyan drip din ta tsinke ta sauka akan gadon batama jin me suke cewa takoma kofar dakinsa ta dinga bugawa tana kirar sunansa tana kuka yana jinta daga kan sallayar daya zauna akai amma bai ko motsa ba sabida rabonsa dayay hawaye akan wata ya mace tun mutuwar mahaifyarsa..
yana masifar sonta snn yanada tsananin kishi amma babban damuwarsa ba labarin tay cikin bane shide yadda komi daya farun zai iya jawo mutuwar aurensu ne yake damunsa dan koda maza dubune suka rabe nur bayajin hakan zai iya goge masa son dayake mata aransa
tunaninta ya kwana yi ya kuma kikira duka lambar wayar sultan amma dukkansu suna akashe, yau din ko runtsawa baiyi ba bare ya samu sukuni aransa,.
it took him a great deal of emotional outbust kafin nan ya samu dan karamin nitsuwa duk ya kasa fitowa waje da umbin fargaban haduwar sa da mahaifinsa acikin masjid dan yasan by now duk jiran maganan bakinsa kawai sukeyi akan nur kafin nan ayanke musu hukuncin raba aurensu, tunda dai kakkarfan doka ce a ahalin su kan cewa basu taba auren macen da wani da namijin daban ya fara saninta tun awaje gashi shikuma ji yake kamar bazai taba iya rabuwa da nur firdaus ba.
yanaji nur tanata kuka tana ambatar sunansa daga kofar dakin san abun na konashi mishi rai amma baijin zai iya sake kallon idanunta sabida tsananin kishi da mahaukacin son dayake mata aransa
anan bakin kofarsan nur ta sulale kasa ta zauna atakure tana kuka na tsawon lkci har saida numfashinta ya dena fita, few more minutes taji bata san inda kanta yake ba kawai tingling pains na yadda ake soka mata alluran bacci taji daga nan sai bata sake sanin inda take ba.
cikin tsananin damuwa na'ima data tay taurin kai taje ta daukota daga kofar dakin tazauna tay summm agefenta tanata nazarin meka faruwa tsakanin nur da javeed dan har yanzu basu san meke faruwa ba tukuna.
koda yajita shiru babu sautin kukantan awaje nan sai ya mike tsaye ya bude kofar da sauri ya dudduba sai yaga babu kowa awajen face janet data tsaya acan gefe tay tagumi duk ta ta kasa gaba ta kasa baya sabida tsoron kalar tsawar daya musu jiyan ya koresu a sashensan me gabaki daya.
suna hade ido ta rusuna kasa a tsorace tafara gaishesa
fuskarsa a shake be ko kulata ba yace mata taje ta kira