Chapter 51 Reading NUR FIRDAUS BOOK 2 HAUSA NOVELS COMPLETE BY SURAYYAHMS.txt Arewa Novels

NUR FIRDAUS BOOK 2 HAUSA NOVELS COMPLETE BY SURAYYAHMS.txt

Author :  SURAYYAHMS Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   51 / 112

150K to 153K   out of 335.4K words

na girki a kitchen din nan kenan i promise you this..

nur tay karamin dariya
cikin jan tsaki tace we will see...

tsaki simran tay a fusace ta karbi drink din hannun liiyatun ta yar akasa ta kwabar a fusace.

nur ta karaso da wani irin rashin kunya kusa da simran tace chill chief...ko haushi kikaji dan ke ban baki ba.

kafin simran ta amsa taji an watsa mata sauran juice din ajiki,

ihu tay ta daga kai ta kalli nur da fusata taga ashe wanda yake hannuntan ta watsa mata

zatay mata tsawa nur ta fashe da dariya ohh u want more? tasake daukar wanda ya rage a roban salon maida ta mahaukaciya ta kara watsa mata ajiki

ganin simran tafara ihu kamar tabbabbiya yasaka naima ta janye hannun nur sukabar kitchen din suka koma sashenta tun bayan nan basu sake sanin ya simran ta kare a kitchen din ba
[21/05, 21:36] BLUE💙: EPISODE 58
AREWABOOKS AY SURAYYAHMS

bazaka san ran nur ya mugun baci da kalar gadara da rainin da simran ta mata akitchen din ba saida suka koma site inta dan duk da na'ima tay kkarin bata haquri amma ko kadan nur bataji alaman zata sauko ba.

babban burinta baifi ta san javeed yaci abincinta ba ynxu sabida yau so take ta girgiza ma simran zuciyarta sabida wani rainin ya ragu tasan kuma cewa itama tana da kalar haukar datakeji dashi.


after like two hours da faruwar haka nur bata samu labarin ko javeed yaci abincinta ko baici ba duk taji ta damu sosai koda taje site dinsa saida taci karo da janet a kofa haka zata mata ai javeed bai isa ba bayan kuma yana ciki yanakan ayyana abubuwan dake gabansa a computersa saidai baiso ne kawai yay gaggawar bata fuska yanxu dan sosai nur ta bashi
mamaki dayaga kalar effort din datakeyi harda masa girki hmm

wanda tun yana jan aji wa girkin har ya hakura ya janyo ha cinye tass snn yace ma janet ta tsaya a kofa tace kawai be dawo ba cos he is going to be busy koda ace yanason suyi magana bazai iya ba dan yasan baida wnn lkcin yanxu

hakanan nur ta zauna da damuwar javeed bai dawo ba bare yaci abincinta...


ata fannin simran kuwa tunda ta koma sashenta da borin hauka yau ko zama batay ba tanata kulla maganganun da zata kai karar nur da shi dan gani take nur bata kai wance zata kirata karuwar gida agaban maids dinsun ba.

tun tuni kawai diri take dan hajya zubby kawai take jira tadawo daga offshore meetings a Egypt dataje wanda is just four hours flight to return a private jet so tasan da yamma haka duk tsiya hajya zubyn tadawo gida, dan yau ta riga ta rantse sai taje da case har gabansu hajya suad da lady sid takai karar nur firdaus dan araba musu raini duk a tunaninta ai yanzu itace da ragamar komi kuma kowa ya shaida.


saida yamma anrd 5:00 pm snn javeed yay wanka ya sace jiki ya fita a gidan me gabaki daya ko janet bata san inda yaje ba.

nur data gama cire rai tana zuwa tasamu har janet ta fitar da kwanokan takai kitchen wajen faiza an wanke amma dake oganta ya hanata cewa komi sai tace ma nur itama haka kawai tagani empty bata san ko shine ya dawo yaci ko yabawa mr aqeel ne ba

duk dama abun bai qamsheta ba amma dai is a bit of reliave for her tunda dai anci sai kawai ta haqura beside koma miyene yayimata ai ita tace masa bata son ganinsa dama so she os not suprise dayaki zuwan tasan lefinta ne data koresa ajikinta.


zuciyarta akarye ta koma estate dinta, daga nan taje tay wanka tasako wani irin plain blue gown inta mai kyau tay rolling da farin veil yau ko naima bata gayyata ba takai yammaci wajen father in law da evening snack masu dadi data saka chef faiza tay

tanayin sallama a sashen bakaramin dadi dataji shikadai ne ya amsa mata ba dan dama bataso tazo ta samu su anty suad.

cike da ladabi ta karaso ciki ganinsa zaune akan dadduma yana karatun qur'ani sai ta rusuna kasa ta jirashi har saida ya idda da girmamawa da kuma biyayya a muryanta ta gaishe sa snn ta bashi snack din takuma nuna masa ai komi yawuce tsakanin ta da javeed din.

yaji dadin hakan afarko amma dake shi din babbane bai wani gama aminta ba har saida ya fara mata tambaya akan snacks din, nur tay kamar bata san metakeyi ba tafara bashi labarin shirme dana girkin da takeyi acan agidan iyayenta.

yana cin snacks din yana murmushi yana kuma jin dadin hirar kamar da wasa tajawo mind dinsa akan abunda tazo da shi aikuwa yana tuhumarta batun kitchen tafara cemai ai mai aikinta tariga tace mata watace agidan nan take basu oder akan kayan food stores da management shiyasa ma ita take jin sanyin jikin yin abunda take so a kitchen

nan dai ta shigar da maganan awani yanayi datasan zai gane abubuwan dake faruwa game da ikon da simran takeyi da kayan abinci batare da ambaci sunanta afili ba.

shikuwa atake sai yaji ransa ya mugun baci sosai ganin wai surkuwan sa akewa gadara da kayan abincin agidan atake ya bari akan duk wann lefin matar sa zubaida ne amma kuma yacigaba da mumurshinsa yanajin hirar nur din datakeynshi normal amma da hikima take soka masa maganan simran aciki batare da ta ambace sunan kowa ba har tagama hirar gabaki daya.


kirar sallahn magrib ne ya katsesu tana shirin masa sallama zata koma sashenta kenan sai ga hajy zubbyn tasha wani irin lullumi da tsadadden lafaya yanayinta adan gajiye ganin nur zaune da mijinta suna magana yasaka ta dauke wuta tawani hade rai..

nur kuwa ko ajikinta ta tsuguna ta gaisheta, da wani irin harara da kallon banza hajya zubyn ta amsata ciki ciki batare da sanin cewa idon Alhji attahn duk yana kanta ba

nur tay kamr bata san ma an mata kallon banzan ba tay murmushi ta musu sallama ta wuce sashenta.


alwala kawai tay ta hau sallaya tay magrib ta zauna anan ko wani sallahn isha bata karkare ba sai ganan naima tazo tace mata ma neman ta anan falonta yanxun nan

sake gyara fuskarta tay kirjinta na bugawa amma ta riga ta rantse zata nuna ma simran iyakarta


da hijabin dake jikinta ta fito tana hango hajy zubby atsaye ta sauya taku tafarayinshi cikin yauqi har ya karaso ta samesu ita da liyatu kowa ya hada gabar da yamma ga liyatun ta kwaso dukka spare keys din food stores da komi na gidan harda sauran tarkacen abubuwan daya danganci dokoki a hannun simran sunzo da shi..

bacin rai dake kan fuskar hajy zubyyn ya kasa boyuwa dan koda taga nur din ji tay kamar ta rufeta da dukkka tuna irin azaban masifar da alhj attah ya gama mata yay mata fata fata yace kuma ta amshi duk wani keys a hannun simran in takai ma wacce ya dace ta rike su dan baiga dalili da za afara raina ma surkuwan gidansa wayo ba...

cewa ma dayayi wai ba hurumin simran bane rike keys da saka doka agidan snn kar simran din tasake taba wani abu daya shafi welfare na maaikata bada izinin nur ba duk shiyafi hatsalata dan all these year da simran keyi baiga kkrinta ba har yana da bakin cewa ai bawani ya dorata ba tanayi ne radin kanta yanxu kuma tunda akwai matar javeed shi baison jin wani magana kuma ya masifeta tasss yace mata komai lefinta ne bata san respinsiblites dinta na uwa bane agidan da wn maganan ma basai angaya mata ba.


gabaki daya batasan waya kai cunen simran gabansa ba amma kuma sosai jikinta yake bata kamr nur din ne tunda dai tare ta samesu kuma tana barin wajen ne ya rufeta da masifar


nur tadan tsaya kanta na kallon gefe kadan muryanta ciki ciki tace hajiiya gani nan.

wani tsaki mai sauti hajy zubby taja...tace ke liyatu bata duka keys din..

da ladabi liyatu ta kawo cikin jan ajk nur taki karba tama naima ido akan ta amsa snn tace hajiya wai keys din meyene kuma wann?.

Da wani irin kallon banza hjya zuby tace " nima bansani ba, Kina matsayin surkuwan gida ai yanzu kika fara rike keys..but lets see if u can hold them well tunda mu ance bamu iya ba

ahnkli nur tace uhum..

ta kalli naima tace kaisu ciki ki ajje su tukun sai nayi nazari


wani fuuuu hajya zubaidan ta juya tabar sashen tsabar ranta ya baci har bata ganin gabanta.
[22/05, 17:56] BLUE💙: EPISODE 59
Arewabooks@surayyahms.
idanun hajiya zuby a rufe dan tsabar bacin rai har ta karaso shashenta da wani irin huci ta rufe kofartan kirif.

Ahaka daren ranar ya zame mata me daci dan gabaki daya baiyi mata dadi aranta ba daga ita har simran din datun da hajya zubyn ta shigo ta kwace komi na gidan ahannunta takai ma nur ta kwanta agado ta rike zuciyarta tana nishi nishi tana zage zage wai zazabbin high fever ya rufeta

gashi duk wann gurmin anyi shi ne adan kankanin lokci wanda kwata kwata harsu lady sidd ma basu ji labari ba bare su hana yuwar wani abu dake kawai oder ya bawa hjya zubaida yace mata with immidiete effect dan aganinsa samun waje ne ya jawo zubaida da yar uwanta suke masa mulkin kama karya a gidansa musmn akan surkuwan sa dan sun ganta karamar yarinya.


fannin nur kuwa ko ajikinta wai irin kaji dar dar kayi abuna makircin din nan bata kuma ko ji alamar ta girgiza da maganan hajya zuby ba.

yauma tajira ganin shigowar javeed da baizo ba kawai sai tay haquri ta rufe idonta ta kwanta, yau kam tay kkrin share abun danma tay disracting mind inta yasaka ta fasa baccin suka xauna a falonta ita da private servant dinta na'ima nan suka fara warware duk wani salon hauka da mugayen dokokin rashin hankli dana cuta da simran take zubawa akan sha'anin tafiyar da duk wani walfare na gidan

naima ne ka bata duk wani information suna dubawa wanda yakai su har wajajen one o'clok na dare kafin nan nur ta sallameta itama tay addua ta je daki ta kwanta bata jima ba bacci me nauyi ya dauketa.


bayan wann daren, dare daya da kuma wuni biyu ne kacal ya rage ma javeed agidan, dn haka goben ya yanke ranar hutunsa ne dan dokane basa training 2 days before a mission attack dan haka yaudinne kawai ya samu ya karkare duk wata shirinsa da duk wani training dinsa na karshe sabida goben ya samu isasshen bacci da kuma hutu..


bashida da gama shiri ba sai wajajen 2 oclk na dare, wanka kawai yay yasaka wata dark blue plain pyjams riga da wando dacan har zai kwanta saidai jin yakasa samun wata nitsuwa a
ransa saiya taho cikin dakin nur din yashigo queitly batare da yay wani motsin dayasan zai tashe ta ba.

yana daga tsaye ya kalleta yaga tay nisa abaccin sosai ahankli ya karaso ya zauna agefenta bai tabata ba yazuba mata mayun idanunsa masu cike da muguwar kaunarta yanata kallonta da tunanin inya tafi baida tabbacin zai dawo mata da ransa koko a muce..

kallon innocent figure inta yakey da dukkan imaninshi atake kuma sai yaji wani irin rauni na neman rufeshi da tunanin in yaje yamutu acan ribar soyyrsa kenan guda daya da ya auri macen dayake so aransa, saidai yasan zai iya saka rayuwar nur a wata matsala duba da gata karama batama san dadin auren ba bare kuma tarin soyayyar dake ransa akanta wanda har yau bai samu daman nuna mata yawansa ba.

tausayinta sosai ya rufeshi har kamar hawaye zai taru a idanunsa yana zaune awajen yafi awa daya yana tunani yasan lokci yagama kurewa nayin wata maganar fahimtar juna atskainsu dan baison yay zatay reacting ba kuma shi rayuwarsa yake dubawa sabida ya samu ya dawo araye saboda ita.

da wani irin tsumammen rauni a idanunsa ya manna mata kiss mai sanyi a saman lips dinta

ganin tafara motsi tana dan sniffing perfume dinsa yasaka yamike sikinini yabar dakin yakoma nashi kawai ya kwanta bai jima ba yafarka sallahn asubahi yana fita nan ma baijima ya dawo dakinsa ya kwanta abunsa yafara bacci tareda bada oder cewa baison ko kadan atadashi...


sassafe nur tay sallanta jikinta na ta bata cewa javeed yazo dakin jiya da dare dan haryanxu tana jin qamshinsa ajikinta da akan hannunta daya riken amma kuma sai tabarshi kawai a imaginations ne dan yadda ta masa rashin kunyar nan ta koresa a jiknta batajin hala zai taba takowa yazo
...

tun 6:30am na safiya naima tazo suka fita waje tare, nur ta saka dogon hijabinta har kasa daya killaceta kirif cikin takun ta na nitsuwa har suka je general workers estate nur tay paying ma ogogin maaikatn gidan unxpected visit.

already ta riga tasan yadda ake magana cike da confidence, nuna girma tareda sanyin dattako agaban mutane sabida abunda ma molly tafara koya mata kenan.

dan haka koda sukaje aka tara ogogin taga kowa na rawan jiki ana gaisheta duk dama ta san yawancin su sunkai su haifeta amma bata sake tay musu over sabi face ba.

yanayinta anitse kuma da isashen kamiya ta musu bayanin yadda ta tsara nata dokokin

snn ta basu daman ushering din opinions dinsu da wasu ra'ayoyinsu wanda abune da abataba musu agidan ba sabida simran ne take hawa kan komi dacan kuma hajya zubaida ne.


cikin 1hour sai gashi har sunyi resolving komi da komi anan ma takejin yadda simran ke mugun kakkara kudi akan abubuwan gida tana makewa..

ashe simran ba kulawa da business din babantan takeyi ba kawai wayann yan kudeden cutar data keyi agidan mufasa shitake rike kamfanin dashi har ake ganin kamar tanada wasu boyayyun investmts ne duk ba asan kudin sata bane datake mammakewa daga cikin kudin abinci da welfares na duka ma'aikatan gida

duk wani kayan masarufi ko karin kudin aiki ko ihsani sam ko kujerar macca da ake rabawa wokers simran ragewa takey acikin na wasuma takan tsakura kadan ta basu wasu kuma takan hanasu taba komi.

zagewa manyan cikin su sukayi suka hau gayawa nur komi dake faruwa agidan basu boye mata aya ba, dan tun bayan rasuwar mahaifyr javeed komi ya lalace musu amma kuma sabida hajya zubbyce agidan ya zamo basu isa sukai karar simran ba nan da nan sai kaga ta karyatasu ko tay musu mummn sharri.


nan komi akayishi cikin girmamawa da aminci snn ta ja kunnen kowa akan suyi aikansu da amana da gaskiya wasu haqqin su da aka tauye duk atake ta saukar, masu bukatar canji duk ta canza musu, har liyatu saida ta dawo da ita snn tay assingn ma simran din wata yar yarinya dede da aikin gida.


yau kamar sallahrsu hakanan sukejin dadi kowa na sambarka da nur firdaus atleast babu tsiwa ba tsawa babu gadara da mulkin kama karya kuma anji raayinsu akan abubuwan dake damunsu kuma an dau hanyar samar musu mafita..

wasu da akayi case din jiya dasu a kitchen yadda simran ta dinga cika baki agabansu yasa sukasha mugun mamakin yadda har nur takwace komi ovenight a hannun simran duk gadarar datayin nan.

masu yayata gulma akan hakan kuwa yasaka kowa yafara jin mugun shakkar nur din aransa ganin yadda alokci daya ta kifar da mulkin simran data jima tana nuna musu itadin wata kainuwa ce agidan

wasu dama sunsan basu isa su dama sutaba nur akowani siga ba saboda sunsan javeed baiya wasa da kowa.


sassafen kuwa ko wani bangaren wokers aka canza tsari aka fara abubuwa cikin salo me tsafta da sauki kafin 8am nur tay signing wasu pay cheques din su da simran take hanasu.

kai hatta chat table na abincin duk tasaka an sauyashi musmn na main kitchen da simran ta saka ake musu hauka kowani safiya..

janet da naima da faiza yau bakaramin jinjina ma nur sukayi ba saidai babu mai iya furta mata duk ana tsoron shiga gonan javeed amma daga fuskarsu zakasan suna mugun jin dadin yanayinta sosai


normal routine dinta na kullum sukayi, nur ta shirya tsaf yauma atmfa ta saka peplum stylish blouse me strght skirt grey colour tay lullumi da karamin veil abinta koda taje sashensa yaukam ko su janet din ma bata gani a kofa ba and once is locked frm the inside bamai iya budewa.

bata saka komi aranta ba tay zaton ko ya sake fita training ne as usual kawai sai ta danne zuctarta ta sauko kasa ita daya abunta taje main falon.

nan ma ta samu har angama kawo breakfast an shirya musu komi kuma akan lokaci anty suad sai yabawa da sabon tsarin girkin yau din takey amma tunda hajy zuby tace mata ai nur ce ta amshi ragamar komi sai ta tsime tana neman hadiye magananta


haka akaci abincin babu javeed babu simran dake kwance a dakinta tana kuka tun jiya da dare haryau tunani takei na me zatay ma nur ta rama wann uban cin mutuncin da rainin data mata agidan dan tasan yanxun kowani servants da maids zasuna mata kallon bata da iko snn nata ya kare.

wani tukukin numfashi taja akarsashe zuciyar ta na mata wani irin zafi tace "inaaaa...
wallh bazai taba yuwa ba saina ramaaaa ta mike zaune tana wani irin kukan yadda saka san abun yay mugun ci mata rai har wani sheshheka takeja ta ciki....

saida ta gama tunanin me xatay snn ta mike ta shiga ta wanke fuska tana fitowa tasha tea me kauri hade da magani tukunna ta fita wajen motsa jiki.


kazar kazar tareda walwalan dake wanzuwa a fuskan wokers din yasaka lady sidd tayita neman cikakken karin bayani akan lamarin daya faru jiyan har aka yanke hukuncin bawa nur firdaus keys, haka hajya zubaida ta dinga dunkule maganan tanamai gaya matashi a wata sigar me cike da hada gurmi.

tana nuna kmar komi bisa makirci kawai akayi cewarta ai ba a ma simran adalci ba dan tun bata kai haka ba ita take zuwa ta kula da komi na gidan dan kawai yanxu an kawo wata sai aci mata fuska bayan kuma ga trauma datake fama dashi na rasa javeed.

yau hajiya zubaida har hawaye tay agaban su anty suad tanamai fayyace musu irin secrifices din da simran tay agidan tun da jimawa. ..lady sidd sosai abun ya dan tabata saidai anty suad kuma aranta gani

51 / 112